< Ezekiyel 39 >

1 “Ɗan mutum, ka yi annabci a kan Gog ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gāba da kai, ya Gog, babban sarkin Meshek da Tubal.
And thou, son of man, prophesy against Gog, and say, Thus says the lord Jehovah: Behold, I am against thee, O Gog, ruler of Rosh, Meshech, and Tubal.
2 Zan juya ka in kuma ja ka. Zan kawo ka daga can arewa in aike ka don ka fāɗa wa duwatsun Isra’ila.
And I will turn thee about, and will lead thee on, and will cause thee to come up from the outermost parts of the north, and I will bring thee upon the mountains of Israel.
3 Sa’an nan zan karya bakan da take a hannun hagunka, in sa kibiyoyin da suke a hannun damanka su fāɗi.
And I will smite thy bow out of thy left hand, and will cause thine arrows to fall out of thy right hand.
4 A kan duwatsun Isra’ila za ka fāɗi, kai da sojojinka da kuma al’ummai da suke tare da kai. Zan bayar da kai ka zama abinci ga tsuntsaye da namun jeji masu cin nama.
Thou shall fall upon the mountains of Israel, thou, and all thy hordes, and the peoples who are with thee. I will give thee to the ravenous birds of every sort, and to the beasts of the field to be devoured.
5 Za ka mutu a fili, gama haka ni na faɗa, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
Thou shall fall upon the open field, for I have spoken it, says the lord Jehovah.
6 Zan aika da wuta a kan Magog da kuma a kan waɗanda suke zama lafiya a bakin teku, za su kuwa san cewa ni ne Ubangiji.
And I will send a fire on Magog, and on those who dwell securely in the isles. And they shall know that I am Jehovah.
7 “‘Zan sanar da sunana mai tsarki a cikin mutanena Isra’ila. Ba zan ƙara bari a ɓata sunana mai tsarki ba, kuma al’ummai za su san cewa Ni Ubangiji Mai Tsarki ne a cikin Isra’ila.
And I will make my holy name known in the midst of my people Israel, nor will I allow my holy name to be profaned any more. And the nations shall know that I am Jehovah, the Holy One in Israel.
8 Yana zuwa! Tabbatacce zai faru, in ji Ubangiji Mai Iko Duka. Ranar da na yi magana ke nan.
Behold, it comes, and it shall be done, says the lord Jehovah. This is the day of which I have spoken.
9 “‘Sa’an nan waɗanda suke zama a garuruwan Isra’ila za su fita su tattara makamai su hura wuta da su su kuma ƙone su, manya da ƙanana garkuwoyi, bakkuna da kibiyoyi, kulake da māsu. Shekara bakwai za su yi amfani da su don hura wuta.
And those who dwell in the cities of Israel shall go forth, and shall make fires of the weapons and burn them, both the shields and the bucklers, the bows and the arrows, and the hand staves, and the spears. And they shall make fires of them seven years,
10 Ba za su yi wahalar zuwa jeji don neman itacen hura wuta ba, domin za su yi amfani da makamai don hura wuta. Za su kuma washe waɗanda suka washe su ganima, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
so that they shall take no wood out of the field, nor cut down any out of the forests, for they shall make fires of the weapons. And they shall plunder those who plundered them, and rob those who robbed them, says the lord Jehovah.
11 “‘A ranar zan yi wa Gog makabarta a cikin Isra’ila, a kwarin waɗanda suke tafiya wajen gabashin Teku. Za tă tare hanyar matafiya, domin za a binne Gog da dukan mutanensa a can. Ta haka za a kira wurin Kwarin Haman Gog.
And it shall come to pass in that day, that I will give to Gog a place for burial in Israel: the valley of those who pass through on the east of the sea. And it shall stop those who pass through, and they shall bury Gog and all his multitude there. And they shall call it The valley of Hamon-gog.
12 “‘Watanni bakwai gidan Isra’ila zai yi ta binne su don a tsarkake ƙasar.
And the house of Israel shall be burying them seven months, that they may cleanse the land.
13 Dukan mutanen ƙasar za su binne su, kuma ranar da za a ɗaukaka ni za tă zama ranar tuni a gare su, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
Yea, all the people of the land shall bury them, and it shall be to them a renown in the day that I shall be glorified, says the lord Jehovah.
14 “‘Za a ɗauki mutane kullum don tsabtacce ƙasar. Waɗansu za su ratsa ƙasar, ƙari da waɗannan, waɗansu za su binne gawawwakin da suka ragu a ƙasar. A ƙarshen watanni bakwai ɗin za su fara bincikensu.
And they shall set apart men of continual employment, who shall pass through the land. And, with those who pass through, those that bury those who remain upon the face of the land, to cleanse it, after the end of seven months they shall search.
15 Yayinda suke ratsa ƙasar, in waninsu ya ga ƙashin mutum, zai kafa shi kamar alama a gefe sai masu haƙa kabari sun binne shi a Kwarin Haman Gog.
And those who pass through the land shall pass through, and when any man sees a man's bone, then he shall set up a sign by it till the buriers have buried it in the valley of Hamon-gog.
16 Akwai wani garin da ake kira Hamona zai kasance a can. Ta haka za su tsabtacce ƙasar.’
And Hamonah shall also be the name of a city. Thus they shall cleanse the land.
17 “Ɗan mutum, ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, ka gayyato kowane irin tsuntsu da dukan namun jeji, ‘Ku taru ku kuma zo wuri ɗaya daga ko’ina don hadayar da nake shirya muku, babbar hadaya a kan duwatsun Isra’ila. A can za ku ci nama ku kuma sha jini.
And thou, son of man, thus says the lord Jehovah: Speak to the birds of every sort, and to every beast of the field, Assemble yourselves, and come. Gather yourselves on every side to my sacrifice that I sacrifice for you, even a great sacrifice upon the mountains of Israel, that ye may eat flesh and drink blood.
18 Za ku ci naman manyan mutane ku kuma sha jinin sarakunan duniya sai ka ce an yanka raguna da’yan tumaki, awaki da bijimai, dukansu turkakkun dabbobi daga Bashan.
Ye shall eat the flesh of the mighty, and drink the blood of the rulers of the earth, of rams, of lambs, and of goats, of bullocks, all of them fatlings of Bashan.
19 A hadayar da nake shirya muku, za ku ci kitse sai kun ƙoshi ku kuma sha jini sai kun bugu.
And ye shall eat fat till ye be full, and drink blood till ye be drunken, of my sacrifice which I have sacrificed for you.
20 A teburina za ku ci iya ƙoshiyarku da naman jama’a da kuma mahaya, manyan mutane da sojoji na kowane iri,’ in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
And ye shall be filled at my table with horses and chariots, with mighty men, and with all men of war, says the lord Jehovah.
21 “Zan nuna ɗaukakata a cikin al’ummai, kuma dukan al’ummai za su ga hukuncin da zan yi da kuma hannu mai nauyin da zan ɗora a kansu.
And I will set my glory among the nations. And all the nations shall see my judgment that I have executed, and my hand that I have laid upon them.
22 Daga wannan rana zuwa gaba gidan Isra’ila zai san cewa ni ne Ubangiji Allahnsu.
So the house of Israel shall know that I am Jehovah their God, from that day and forward.
23 Al’ummai kuma za su san cewa mutanen Isra’ila sun tafi zaman bauta saboda zunubinsu, domin sun yi rashin aminci gare ni. Saboda haka na kawar da fuskata daga gare su na miƙa su ga abokan gābansu, suka kuwa mutu ta takobi.
And the nations shall know that the house of Israel went into captivity for their iniquity, because they trespassed against me, and I hid my face from them. So I gave them into the hand of their adversaries, and they fell all of them by the sword.
24 Na yi da su gwargwadon rashin tsabtarsu da laifofinsu, na kuma kawar da fuskata daga gare su.
I did to them according to their uncleanness and according to their transgressions. And I hid my face from them.
25 “Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan komo da Yaƙub daga zaman bauta zan kuma yi wa dukan Isra’ila jinƙai, zan kuma yi kishi saboda sunana mai tsarki.
Therefore thus says the lord Jehovah: Now I will bring back the captivity of Jacob, and have mercy upon the whole house of Israel. And I will be jealous for my holy name.
26 Za su manta da kunyar da suka sha da dukan rashin amincin da suka nuna mini sa’ad da suke zama lafiya a ƙasarsu inda ba wanda zai tsorata su.
And they shall bear their shame, and all their trespasses by which they have trespassed against me, when they shall dwell securely in their land. And none shall make them afraid
27 Sa’ad da na komo da su daga al’ummai na kuma tattara su daga ƙasashen abokan gābansu, zan nuna kaina mai tsarki ta wurinsu a gaban al’ummai masu yawa.
when I have brought them back from the peoples, and gathered them out of their enemies' lands, and am sanctified in them in the sight of many nations.
28 Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji Allahnsu, gama ko da yake na tura su zaman bauta a cikin al’ummai, zan tattara su zuwa ƙasarsu, ba tare da barin wani a baya ba.
And they shall know that I am Jehovah their God, in that I caused them to go into captivity among the nations, and have gathered them to their own land. And I will leave none of them any more there,
29 Ba zan ƙara kawar da fuskata daga gare su, gama zan zuba Ruhuna a kan gidan Isra’ila, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”
nor will I hide my face any more from them. For I have poured out my Spirit upon the house of Israel, says the lord Jehovah.

< Ezekiyel 39 >