< Ezekiyel 39 >

1 “Ɗan mutum, ka yi annabci a kan Gog ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gāba da kai, ya Gog, babban sarkin Meshek da Tubal.
Du, Menneskesøn, Profeter mod Gog og sig: Så siger den Herre HERREN. Se, Jeg kommer over dig, Gog, Fyrste over Rosj, Mesjek og Tubal!
2 Zan juya ka in kuma ja ka. Zan kawo ka daga can arewa in aike ka don ka fāɗa wa duwatsun Isra’ila.
Jeg vender dig, leder dig og fører dig op fra det yderste Nord og bringer dig til Israels Bjerge.
3 Sa’an nan zan karya bakan da take a hannun hagunka, in sa kibiyoyin da suke a hannun damanka su fāɗi.
Så slår jeg Buen ud af din venstre Hånd og lader Pilene falde ud af din højre.
4 A kan duwatsun Isra’ila za ka fāɗi, kai da sojojinka da kuma al’ummai da suke tare da kai. Zan bayar da kai ka zama abinci ga tsuntsaye da namun jeji masu cin nama.
På Israels Bjerge skal du falde, du og alle dine Hobe og Folkeslagene, der følger dig; jeg giver dig til Føde for alle Hånde Rovfugle og Markens vilde Dyr.
5 Za ka mutu a fili, gama haka ni na faɗa, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
I åben Mark skal du falde, så sandt jeg har talet, lyder det fra den Herre HERREN.
6 Zan aika da wuta a kan Magog da kuma a kan waɗanda suke zama lafiya a bakin teku, za su kuwa san cewa ni ne Ubangiji.
Og jeg sætter Ild på Magog og på de fjerne Strandes trygge Indbyggere; og de skal kende, at jeg er HERREN.
7 “‘Zan sanar da sunana mai tsarki a cikin mutanena Isra’ila. Ba zan ƙara bari a ɓata sunana mai tsarki ba, kuma al’ummai za su san cewa Ni Ubangiji Mai Tsarki ne a cikin Isra’ila.
Mit hellige Navn kundgør jeg midt i mit Folk Israel, og jeg vil ikke mere vanhellige mit hellige Navn; og Folkene skal kende, at jeg er HERREN, den Hellige i Israel.
8 Yana zuwa! Tabbatacce zai faru, in ji Ubangiji Mai Iko Duka. Ranar da na yi magana ke nan.
Se, det kommer, det skal ske, lyder det fra den Herre HERREN; det er Dagen, jeg har talet om.
9 “‘Sa’an nan waɗanda suke zama a garuruwan Isra’ila za su fita su tattara makamai su hura wuta da su su kuma ƙone su, manya da ƙanana garkuwoyi, bakkuna da kibiyoyi, kulake da māsu. Shekara bakwai za su yi amfani da su don hura wuta.
Så skal Indbyggerne i Israels Byer gå ud og gøre Ild på og tænde op med Rustninger, små og store Skjolde, Buer, Pile, Håndstave og Spyd; og de skal bruge det til at gøre Ild med i syv År.
10 Ba za su yi wahalar zuwa jeji don neman itacen hura wuta ba, domin za su yi amfani da makamai don hura wuta. Za su kuma washe waɗanda suka washe su ganima, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
De skal ikke hente Træ i Marken eller hugge Brænde i Skovene, men gøre Ild på med Rustningerne. De skal plyndre dem, de plyndredes af, og hærge dem, de hærgedes af, lyder det fra den Herre HERREN.
11 “‘A ranar zan yi wa Gog makabarta a cikin Isra’ila, a kwarin waɗanda suke tafiya wajen gabashin Teku. Za tă tare hanyar matafiya, domin za a binne Gog da dukan mutanensa a can. Ta haka za a kira wurin Kwarin Haman Gog.
Og på hin Dag giver jeg Gog et Gravsted i Israel, Vandringsmændenes dal østen for Havet, og den skal spærre Vejen for Vandringsmænd; der skal de jorde Gog og hele hans larmende Hob og kalde Stedet: Gogs larmende Hobs dal.
12 “‘Watanni bakwai gidan Isra’ila zai yi ta binne su don a tsarkake ƙasar.
Israels Hus skal have hele syv Måneder til at jorde dem og således rense Landet.
13 Dukan mutanen ƙasar za su binne su, kuma ranar da za a ɗaukaka ni za tă zama ranar tuni a gare su, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
Alt folket i Landet skal jorde dem, og det skal tjene til deres Ros, på den Dag jeg herliggør mig, lyder det fra den Herre HERREN.
14 “‘Za a ɗauki mutane kullum don tsabtacce ƙasar. Waɗansu za su ratsa ƙasar, ƙari da waɗannan, waɗansu za su binne gawawwakin da suka ragu a ƙasar. A ƙarshen watanni bakwai ɗin za su fara bincikensu.
Man skal udvælge fast Mandskab til at drage Landet rundt og søge efter dem, der er blevet tilbage ud over Landet, for at rense det; når syv Måneder er gået, skal de skride til at søge;
15 Yayinda suke ratsa ƙasar, in waninsu ya ga ƙashin mutum, zai kafa shi kamar alama a gefe sai masu haƙa kabari sun binne shi a Kwarin Haman Gog.
og når de vandrer Landet rundt og en får Øje på Menneskeknogler, skal han sætte et Mærke derved, for at Graverne kan jorde dem i Gogs larmende Hobs Dal;
16 Akwai wani garin da ake kira Hamona zai kasance a can. Ta haka za su tsabtacce ƙasar.’
også skal en By have Navnet Hamona". Således skal de rense Landet.
17 “Ɗan mutum, ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, ka gayyato kowane irin tsuntsu da dukan namun jeji, ‘Ku taru ku kuma zo wuri ɗaya daga ko’ina don hadayar da nake shirya muku, babbar hadaya a kan duwatsun Isra’ila. A can za ku ci nama ku kuma sha jini.
Og du, Menneskesøn! Så siger den Herre HERREN: Sig til alle Fugle og alle Markens vilde Dyr: Saml eder og kom hid, kom sammen alle Vegne fra til mit Slagtoffer, som jeg slagter for eder, et vældigt Slagtoffer på Israels Bjerge; I skal æde Kød og drikke Blod!
18 Za ku ci naman manyan mutane ku kuma sha jinin sarakunan duniya sai ka ce an yanka raguna da’yan tumaki, awaki da bijimai, dukansu turkakkun dabbobi daga Bashan.
Kød af Helte skal I æde, Blod af Jordens Fyrster skal I drikke, Vædre, Får, Bukke og Tyre, alle fedet i Basan.
19 A hadayar da nake shirya muku, za ku ci kitse sai kun ƙoshi ku kuma sha jini sai kun bugu.
I skal æde eder mætte i Fedt og drikke eder drukne i Blod af mit Slagtoffer, som jeg slagter for eder.
20 A teburina za ku ci iya ƙoshiyarku da naman jama’a da kuma mahaya, manyan mutane da sojoji na kowane iri,’ in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
I skal mætte eder ved mit Bord med Køreheste og Rytterheste, Helte og alle Hånde Krigsfolk, lyder det fra den Herre HERREN.
21 “Zan nuna ɗaukakata a cikin al’ummai, kuma dukan al’ummai za su ga hukuncin da zan yi da kuma hannu mai nauyin da zan ɗora a kansu.
Jeg åbenbarer min Herlighed blandt Folkene, og alle Folkene skal skue den Dom, jeg fuldbyrder, og min Hånd, som jeg lægger på dem.
22 Daga wannan rana zuwa gaba gidan Isra’ila zai san cewa ni ne Ubangiji Allahnsu.
Israels Hus skal kende, at jeg, HERREN, er deres Gud fra hin Dag og fremdeles;
23 Al’ummai kuma za su san cewa mutanen Isra’ila sun tafi zaman bauta saboda zunubinsu, domin sun yi rashin aminci gare ni. Saboda haka na kawar da fuskata daga gare su na miƙa su ga abokan gābansu, suka kuwa mutu ta takobi.
og Folkene skal kende, at Israels Hus vandrede i Landflygtighed for deres Misgerningers Skyld, fordi de var troløse imod mig, så jeg skjulte mit Åsyn for dem og gav dem i deres Fjenders Hånd, hvorfor de alle faldt for Sværdet.
24 Na yi da su gwargwadon rashin tsabtarsu da laifofinsu, na kuma kawar da fuskata daga gare su.
Efter deres Urenhed og deres Overtrædelser handlede jeg med dem og skjulte mit Åsyn for dem.
25 “Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan komo da Yaƙub daga zaman bauta zan kuma yi wa dukan Isra’ila jinƙai, zan kuma yi kishi saboda sunana mai tsarki.
Derfor, så siger den Herre HERREN; Nu vil jeg vende Jakobs Skæbne, forbarme mig over alt Israels Hus og være nidkær for mit hellige Navn;
26 Za su manta da kunyar da suka sha da dukan rashin amincin da suka nuna mini sa’ad da suke zama lafiya a ƙasarsu inda ba wanda zai tsorata su.
og de skal glemme deres Skændsel og al den Troløshed, de viste mig, når de bor trygt i deres Land, uden at nogen skræmmer,
27 Sa’ad da na komo da su daga al’ummai na kuma tattara su daga ƙasashen abokan gābansu, zan nuna kaina mai tsarki ta wurinsu a gaban al’ummai masu yawa.
når jeg fører dem tilbage fra Folkeslagene, samler dem fra deres Fjenders Lande og helliger mig på dem for mange Folks Øjne.
28 Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji Allahnsu, gama ko da yake na tura su zaman bauta a cikin al’ummai, zan tattara su zuwa ƙasarsu, ba tare da barin wani a baya ba.
Og de skal kende, at jeg er HERREN deres Gud, når jeg efter at have ført dem i Landflygtighed blandt Folkene samler dem i deres Land uden at lade nogen af dem blive tilbage derude
29 Ba zan ƙara kawar da fuskata daga gare su, gama zan zuba Ruhuna a kan gidan Isra’ila, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”
og ikke mere skjuler mit Åsyn for dem, da jeg har udgydt min Ånd over Israels Hus, lyder det fra den Herre HERREN.

< Ezekiyel 39 >