< Ezekiyel 38 >
1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Veiu mais a mim a palavra do Senhor, dizendo:
2 “Ɗan mutum, ka fuskanci Gog, na ƙasar Magog, babban sarkin Meshek da Tubal; ka yi annabci a kansa
Filho do homem, dirige o teu rosto contra Gog, terra de Magog, principe e chefe de Mesech e Tubal, e prophetiza contra elle,
3 ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gāba da kai, ya Gog, babban sarkin Meshek da Tubal.
E dize: Assim diz o Senhor Jehovah: Eis que eu estou contra ti, ó Gog, principe e chefe de Mesech e de Tubal;
4 Zan juyar da kai, in sa ƙugiyoyi a muƙamuƙanka in fitar da kai tare da dukan sojojinka, dawakanka, mahayan dawakanka saye da makamai, da kuma jama’a mai girma masu riƙe da garkuwoyi manya da ƙanana, dukansu da takuba a zāre.
E te farei voltar, e porei anzoes nos teus queixos, e te levarei a ti, com todo o teu exercito, cavallos e cavalleiros, todos vestidos bizarramente, congregação grande, com escudo e rodela, manejando todos a espada:
5 Farisa, Kush da Fut za su kasance tare da su, duka riƙe da garkuwoyi da hulunan kwano,
Persas, ethiopes, e puteos com elles, todos elles com escudo e capacete;
6 haka ma Gomer da dukan sojojinsa, da Bet Togarma daga can arewa tare da dukan sojojinsa, al’ummai masu yawa tare da kai.
Gomer e todas as suas tropas, a casa de Togarma, da banda do norte, e todas as suas tropas, muitos povos comtigo.
7 “‘Ka shirya; ka kintsa, kai da dukan jama’arka da suka taru kewaye da kai, ka kuma zama mai ba su umarni.
Prepara-te, e dispõe-te, tu e todas as tuas congregações que se ajuntaram ao pé de ti, e serve-lhes tu de guarda.
8 Bayan kwanaki masu yawa za a kira ka. A shekaru masu zuwa za ka kai hari a ƙasar da ta farfaɗo daga yaƙi, wadda aka tattara mutanenta daga al’ummai masu yawa zuwa duwatsun Isra’ila, dā kango ne sosai. An fitar da su daga al’ummai, yanzu kuwa dukansu suna zama lafiya.
Depois de muitos dias serás visitado: no fim dos annos virás á terra que se retirou da espada, e que foi congregada d'entre muitos povos aos montes de Israel, que sempre serviram de assolação; mas aquella terra foi tirada d'entre os povos, e todos elles habitarão seguramente.
9 Kai da dukan sojojinka da kuma al’ummai masu yawa da suke tare da kai za ku haura, kuna cin gaba kamar hadari; za ku zama kamar girgijen da yake rufewa ƙasa.
Então subirás, virás como uma tempestade, far-te-has como uma nuvem para cobrir a terra, tu e todas as tuas tropas, e muitos povos comtigo.
10 “‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa a ranar, tunani zai shiga cikin zuciyarka za ka kuma ƙirƙiro muguwar dabara.
Assim diz o Senhor Jehovah: E será n'aquelle dia que subirão conselhos sobre o teu coração, e maquinarás um mau designio,
11 Za ka ce, “Zan kai hari wa ƙasar da ƙauyukanta ba su da katanga; zan fāɗa wa mutanen da suke zamansu kurum cikin salama, dukansu suna zama babu katanga babu ƙofofi ko ƙyamare.
E dirás: Subirei contra a terra das aldeias, virei contra os que estão em repouso, que habitam seguros; todos elles habitam sem muro, e não teem ferrolho nem portas;
12 Zan washe in kwashe ganima in kuma juye hannuna gāba da kufai da aka sāke zaunar da mutanen da aka tattara daga al’ummai, masu yawan shanu da kayayyaki, masu zama a tsakiyar ƙasa.”
Para despojar o despojo, e para roubar o roubo, para tornar a tua mão contra as terras desertas que agora se habitam, e contra o povo que se ajuntou d'entre as nações, e já tem gado e possessões, que habita no meio da terra.
13 Sheba da Dedan da’yan kasuwar Tarshish da dukan ƙauyukanta za su ce maka, “Ka zo ka kwashe ganima ne? Ka tattara jama’arka don ka yi waso, ka kuma kwashe azurfa da zinariya, ka kwashe shanu da kayayyaki ka kuma ƙwace ganima mai yawa?”’
Sheba, e Dedan, e os mercadores de Tarsis, e todos os seus leõesinhos te dirão: Porventura tu vens a despojar o despojo? ou ajuntaste o teu ajuntamento para roubar o roubo? para levar a prata e o oiro, para tomar o gado e possessões, para despojar o grande despojo?
14 “Saboda haka ɗan mutum, ka yi annabci ka ce wa Gog, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa a ranar, sa’ad da mutanena Isra’ila suna zaman lafiya, ba za ka sani ba?
Portanto, prophetiza, ó filho do homem, e dize a Gog: Assim diz o Senhor Jehovah: Porventura não o experimentarás n'aquelle dia, quando o meu povo Israel habitar com segurança?
15 Za ka zo daga wurinka a can arewa, kai da al’ummai masu yawa tare da kai, dukansu suna hawan dawakai, jama’a mai yawa, babbar runduna.
Virás pois do teu logar, das bandas do norte, tu e muitos povos comtigo, montados todos a cavallo, grande ajuntamento, e exercito numeroso,
16 Za ka ci gaba a kan mutanena Isra’ila kamar yadda girgijen yakan rufe ƙasa. A kwanaki masu zuwa, ya Gog, zan kawo ka, ka yi yaƙi da ƙasata, domin al’ummai su san ni sa’ad da na nuna kaina mai tsarki ta wurinka a gabansu.
E subirás contra o meu povo Israel, como uma nuvem, para cobrir a terra: no fim dos dias succederá; então te trarei contra a minha terra, para que as nações me conheçam a mim, quando eu me houver sanctificado em ti aos seus olhos, ó Gog
17 “‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ba kai ba ne na yi magana da kai a kwanakin dā ta wurin bayina annabawan Isra’ila? A lokacin sun yi annabci shekaru masu yawa cewa zan kawo ka, ka yaƙe su.
Assim diz o Senhor Jehovah: Porventura não és tu aquelle de quem eu disse nos dias antigos, pelo ministerio de meus servos, os prophetas de Israel, que n'aquelles dias prophetizaram largos annos, que te traria contra elles?
18 Ga abin da zai faru a ranar. Sa’ad da Gog ya fāɗa wa ƙasar Isra’ila, fushina mai zafi zai ƙuna, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
Succederá, porém, n'aquelle dia, no dia em que vier Gog contra a terra de Israel, diz o Senhor Jehovah, que a minha indignação subirá a meus narizes.
19 Cikin kishina da hasalata mai zafi zan furta cewa a wannan lokaci za a yi babbar girgizar ƙasa a ƙasar Isra’ila.
Porque fallei no meu zelo, no fogo do meu furor, que n'aquelle dia haverá grande tremor sobre a terra de Israel;
20 Kifin teku, tsuntsayen sarari, namun jeji, kowace halitta mai rarrafe da kuma dukan mutane a duniya za su yi rawar jiki a gabana. Za a tumɓuke duwatsu, a ragargaza tsaunuka, kuma kowane bango zai fāɗi ƙasa.
De tal maneira que tremerão diante da minha face os peixes do mar, e as aves do céu, e os animaes do campo, e todos os reptis que se arrastam sobre a terra, e todos os homens que estão sobre a face da terra; e os montes serão deitados abaixo, e os precipicios cairão, e todos os muros cairão á terra.
21 Zan kira takobi a kan Gog a dukan duwatsuna, in ji Ubangiji Mai Iko Duka. Kowane takobin mutum zai yi gāba da ɗan’uwansa.
Porque chamarei sobre elle a espada por todos os meus montes, diz o Senhor Jehovah: a espada de cada um se voltará contra seu irmão.
22 Zan yi hukunci a kansa da annoba da kuma zub da jini; zan yi ruwa mai yawa da ƙanƙara da kibiritu mai cin wuta a kansa da a kan sojojinsa da kuma a kan al’ummai masu yawa da suke tare da shi.
E contenderei com elle pela peste e pelo sangue; e uma chuva inundante, e grandes pedras de saraiva, fogo, e enxofre choverei sobre elle, e sobre as suas tropas, e sobre os muitos povos que estiverem com elle.
23 Ta haka zan nuna girmana da kuma tsarkina, zan sanar da kaina a gaban al’ummai masu yawa. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji.’
Assim eu me engrandecerei e me sanctificarei, e me farei conhecer aos olhos de muitas nações; e saberão que eu sou o Senhor.