< Ezekiyel 38 >

1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
La parole de Yahvé me fut adressée en ces termes:
2 “Ɗan mutum, ka fuskanci Gog, na ƙasar Magog, babban sarkin Meshek da Tubal; ka yi annabci a kansa
Fils d'homme, tourne ta face vers Gog, du pays de Magog, prince de Rosh, de Meshech et de Tubal, et prophétise contre lui.
3 ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gāba da kai, ya Gog, babban sarkin Meshek da Tubal.
Tu diras: « Le Seigneur Yahvé dit: Voici, j'en veux à toi, Gog, prince de Rosh, de Meshech et de Tubal.
4 Zan juyar da kai, in sa ƙugiyoyi a muƙamuƙanka in fitar da kai tare da dukan sojojinka, dawakanka, mahayan dawakanka saye da makamai, da kuma jama’a mai girma masu riƙe da garkuwoyi manya da ƙanana, dukansu da takuba a zāre.
Je te tournerai, je mettrai des crochets dans tes mâchoires, et je te ferai sortir avec toute ton armée, chevaux et cavaliers, tous revêtus d'une armure complète, une grande troupe, avec bouclier et cuirasse, tous maniant l'épée;
5 Farisa, Kush da Fut za su kasance tare da su, duka riƙe da garkuwoyi da hulunan kwano,
la Perse, Cush, et Put avec eux, tous avec bouclier et casque;
6 haka ma Gomer da dukan sojojinsa, da Bet Togarma daga can arewa tare da dukan sojojinsa, al’ummai masu yawa tare da kai.
Gomer et toutes ses hordes, la maison de Togarma, à l'extrémité du nord, et toutes ses hordes, beaucoup de peuples avec toi.
7 “‘Ka shirya; ka kintsa, kai da dukan jama’arka da suka taru kewaye da kai, ka kuma zama mai ba su umarni.
"''Prépare-toi, oui, prépare-toi, toi et toutes tes troupes qui sont rassemblées auprès de toi, et sois un gardien pour elles.
8 Bayan kwanaki masu yawa za a kira ka. A shekaru masu zuwa za ka kai hari a ƙasar da ta farfaɗo daga yaƙi, wadda aka tattara mutanenta daga al’ummai masu yawa zuwa duwatsun Isra’ila, dā kango ne sosai. An fitar da su daga al’ummai, yanzu kuwa dukansu suna zama lafiya.
Après bien des jours, vous serez visités. Dans la suite des temps, tu entreras dans le pays qu'on ramène de l'épée, qu'on recueille d'un grand nombre de peuples, sur les montagnes d'Israël, qui ont été un désert continuel; mais on le retire des peuples et ils habiteront en sécurité, tous.
9 Kai da dukan sojojinka da kuma al’ummai masu yawa da suke tare da kai za ku haura, kuna cin gaba kamar hadari; za ku zama kamar girgijen da yake rufewa ƙasa.
Tu monteras. Tu viendras comme une tempête. Tu seras comme une nuée pour couvrir le pays, toi et toutes tes hordes, et de nombreux peuples avec toi. »
10 “‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa a ranar, tunani zai shiga cikin zuciyarka za ka kuma ƙirƙiro muguwar dabara.
"'Le Seigneur Yahvé dit: « En ce jour-là, des choses te viendront à l'esprit et tu concevras un plan diabolique.
11 Za ka ce, “Zan kai hari wa ƙasar da ƙauyukanta ba su da katanga; zan fāɗa wa mutanen da suke zamansu kurum cikin salama, dukansu suna zama babu katanga babu ƙofofi ko ƙyamare.
Tu diras: « Je monterai dans le pays des villages sans murs. J'irai vers ceux qui sont au repos, qui habitent en sécurité, tous sans murs, sans barres ni portes,
12 Zan washe in kwashe ganima in kuma juye hannuna gāba da kufai da aka sāke zaunar da mutanen da aka tattara daga al’ummai, masu yawan shanu da kayayyaki, masu zama a tsakiyar ƙasa.”
pour prendre le pillage et le butin; pour tourner ta main contre les ruines habitées, et contre le peuple rassemblé des nations, qui a du bétail et des biens, qui habite au milieu de la terre.''
13 Sheba da Dedan da’yan kasuwar Tarshish da dukan ƙauyukanta za su ce maka, “Ka zo ka kwashe ganima ne? Ka tattara jama’arka don ka yi waso, ka kuma kwashe azurfa da zinariya, ka kwashe shanu da kayayyaki ka kuma ƙwace ganima mai yawa?”’
Saba, Dedan et les marchands de Tarsis, avec tous ses jeunes lions, te demanderont: « Es-tu venu pour prendre le butin? As-tu rassemblé ta troupe pour prendre le butin, pour emporter de l'argent et de l'or, pour emporter du bétail et des biens, pour faire un grand pillage? »
14 “Saboda haka ɗan mutum, ka yi annabci ka ce wa Gog, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa a ranar, sa’ad da mutanena Isra’ila suna zaman lafiya, ba za ka sani ba?
« C'est pourquoi, fils d'homme, prophétise et dis à Gog: « Le Seigneur Yahvé dit: « En ce jour où mon peuple Israël habitera en sécurité, ne le sauras-tu pas?
15 Za ka zo daga wurinka a can arewa, kai da al’ummai masu yawa tare da kai, dukansu suna hawan dawakai, jama’a mai yawa, babbar runduna.
Tu viendras de ton lieu de résidence, des extrémités du nord, toi et beaucoup de peuples avec toi, tous montés sur des chevaux, une grande troupe et une armée puissante.
16 Za ka ci gaba a kan mutanena Isra’ila kamar yadda girgijen yakan rufe ƙasa. A kwanaki masu zuwa, ya Gog, zan kawo ka, ka yi yaƙi da ƙasata, domin al’ummai su san ni sa’ad da na nuna kaina mai tsarki ta wurinka a gabansu.
Tu monteras contre mon peuple d'Israël comme une nuée qui couvre le pays. C'est dans la suite des temps que je te ferai venir contre mon pays, afin que les nations me connaissent, quand je serai sanctifié en toi, Gog, sous leurs yeux. »
17 “‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ba kai ba ne na yi magana da kai a kwanakin dā ta wurin bayina annabawan Isra’ila? A lokacin sun yi annabci shekaru masu yawa cewa zan kawo ka, ka yaƙe su.
"'Le Seigneur Yahvé dit: « Es-tu celui dont j'ai parlé autrefois par mes serviteurs les prophètes d'Israël, qui ont prophétisé en ces jours-là pendant des années que je te ferais venir contre eux?
18 Ga abin da zai faru a ranar. Sa’ad da Gog ya fāɗa wa ƙasar Isra’ila, fushina mai zafi zai ƙuna, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
En ce jour-là, quand Gog viendra contre le pays d'Israël, dit le Seigneur Yahvé, ma colère montera dans mes narines.
19 Cikin kishina da hasalata mai zafi zan furta cewa a wannan lokaci za a yi babbar girgizar ƙasa a ƙasar Isra’ila.
Car j'ai parlé dans ma jalousie et dans le feu de ma colère. En ce jour-là, il y aura une grande secousse dans le pays d'Israël,
20 Kifin teku, tsuntsayen sarari, namun jeji, kowace halitta mai rarrafe da kuma dukan mutane a duniya za su yi rawar jiki a gabana. Za a tumɓuke duwatsu, a ragargaza tsaunuka, kuma kowane bango zai fāɗi ƙasa.
en sorte que les poissons de la mer, les oiseaux du ciel, les animaux des champs, tous les reptiles qui rampent sur la terre et tous les hommes qui sont à la surface de la terre trembleront en ma présence. Alors les montagnes seront renversées, les lieux escarpés s'écrouleront, et toutes les murailles tomberont à terre.
21 Zan kira takobi a kan Gog a dukan duwatsuna, in ji Ubangiji Mai Iko Duka. Kowane takobin mutum zai yi gāba da ɗan’uwansa.
J'appellerai l'épée contre lui sur toutes mes montagnes, dit le Seigneur Yahvé. « L'épée de chacun sera contre son frère.
22 Zan yi hukunci a kansa da annoba da kuma zub da jini; zan yi ruwa mai yawa da ƙanƙara da kibiritu mai cin wuta a kansa da a kan sojojinsa da kuma a kan al’ummai masu yawa da suke tare da shi.
J'entrerai en jugement avec lui par la peste et par le sang. Je ferai pleuvoir sur lui, sur ses hordes et sur les nombreux peuples qui sont avec lui, des pluies torrentielles avec de grosses grêles, du feu et du soufre.
23 Ta haka zan nuna girmana da kuma tsarkina, zan sanar da kaina a gaban al’ummai masu yawa. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji.’
Je me glorifierai et me sanctifierai, et je me ferai connaître aux yeux de nombreuses nations. Alors ils sauront que je suis Yahvé. »''

< Ezekiyel 38 >