< Ezekiyel 38 >

1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
And the word of the Lord came to me, saying:
2 “Ɗan mutum, ka fuskanci Gog, na ƙasar Magog, babban sarkin Meshek da Tubal; ka yi annabci a kansa
Son of man, set thy face against Gog, the land of Magog, the chief prince of Mosoch and Thubal: and prophesy of him,
3 ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gāba da kai, ya Gog, babban sarkin Meshek da Tubal.
And say to him: Thus saith the Lord God: Behold, I come against thee, O Gog, the chief prince of Mosoch and Thubal.
4 Zan juyar da kai, in sa ƙugiyoyi a muƙamuƙanka in fitar da kai tare da dukan sojojinka, dawakanka, mahayan dawakanka saye da makamai, da kuma jama’a mai girma masu riƙe da garkuwoyi manya da ƙanana, dukansu da takuba a zāre.
And I will turn thee about, and I will put a bit in thy jaws: and I will bring thee forth, and ail thy army, horses and horsemen all clothed with coats of mail, a great multitude, armed with spears and shields and swords.
5 Farisa, Kush da Fut za su kasance tare da su, duka riƙe da garkuwoyi da hulunan kwano,
The Persians, Ethiopians, and Libyans with them, all with shields and helmets.
6 haka ma Gomer da dukan sojojinsa, da Bet Togarma daga can arewa tare da dukan sojojinsa, al’ummai masu yawa tare da kai.
Gomer, and all his bands, the house of Thogorma, the northern parts and all his strength, and many peoples with thee.
7 “‘Ka shirya; ka kintsa, kai da dukan jama’arka da suka taru kewaye da kai, ka kuma zama mai ba su umarni.
Prepare and make thyself ready, and all thy multitude that is assembled about thee, and be thou commander over them.
8 Bayan kwanaki masu yawa za a kira ka. A shekaru masu zuwa za ka kai hari a ƙasar da ta farfaɗo daga yaƙi, wadda aka tattara mutanenta daga al’ummai masu yawa zuwa duwatsun Isra’ila, dā kango ne sosai. An fitar da su daga al’ummai, yanzu kuwa dukansu suna zama lafiya.
After many days thou shalt be visited: at the end of years thou shalt come to the land that is returned from the sword, and is gathered out of many nations, to the mountains of Israel which have been continually waste: but it hath been brought forth out of the nations, and they shall all of them dwell securely in it.
9 Kai da dukan sojojinka da kuma al’ummai masu yawa da suke tare da kai za ku haura, kuna cin gaba kamar hadari; za ku zama kamar girgijen da yake rufewa ƙasa.
And thou shalt go up and come like a storm, and like a cloud to cover the land, thou and all thy bands and many people with thee.
10 “‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa a ranar, tunani zai shiga cikin zuciyarka za ka kuma ƙirƙiro muguwar dabara.
Thus saith the Lord God: In that day projects shall enter into thy heart, and thou shalt conceive a mischievous design.
11 Za ka ce, “Zan kai hari wa ƙasar da ƙauyukanta ba su da katanga; zan fāɗa wa mutanen da suke zamansu kurum cikin salama, dukansu suna zama babu katanga babu ƙofofi ko ƙyamare.
And thou shalt say: I will go up to the land which is without a wall, I will come to them that are at rest, and dwell securely: all these dwell without a wall, they have no bars nor gates:
12 Zan washe in kwashe ganima in kuma juye hannuna gāba da kufai da aka sāke zaunar da mutanen da aka tattara daga al’ummai, masu yawan shanu da kayayyaki, masu zama a tsakiyar ƙasa.”
To take spoils, and lay hold on the prey, to lay thy hand upon them that had been wasted, and afterwards restored, and upon the people that is gathered together out of the nations, which hath begun to possess and to dwell in the midst of the earth.
13 Sheba da Dedan da’yan kasuwar Tarshish da dukan ƙauyukanta za su ce maka, “Ka zo ka kwashe ganima ne? Ka tattara jama’arka don ka yi waso, ka kuma kwashe azurfa da zinariya, ka kwashe shanu da kayayyaki ka kuma ƙwace ganima mai yawa?”’
Saba, and Dedan, and the merchants of Tharsis, and all the lions thereof shall say to thee: Art thou come to take spoils? behold, thou hast gathered thy multitude to take a prey, to take silver, and gold, and to carry away goods and substance, and to take rich spoils.
14 “Saboda haka ɗan mutum, ka yi annabci ka ce wa Gog, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa a ranar, sa’ad da mutanena Isra’ila suna zaman lafiya, ba za ka sani ba?
Therefore, thou son of man, prophesy and say to Cog: Thus saith the Lord God: Shalt thou not know, in that day, when my people of Israel shall dwell securely?
15 Za ka zo daga wurinka a can arewa, kai da al’ummai masu yawa tare da kai, dukansu suna hawan dawakai, jama’a mai yawa, babbar runduna.
And then shalt come out of thy place from the northern parts, thou and many people with thee, all of them riding upon horses, a great company and a mighty army.
16 Za ka ci gaba a kan mutanena Isra’ila kamar yadda girgijen yakan rufe ƙasa. A kwanaki masu zuwa, ya Gog, zan kawo ka, ka yi yaƙi da ƙasata, domin al’ummai su san ni sa’ad da na nuna kaina mai tsarki ta wurinka a gabansu.
And thou shalt come upon my people of Israel like a cloud, to cover the earth. Thou shalt be in the latter days, and I will bring thee upon my land: that the nations may know me, when I shall be sanctified in thee, O Gog, before their eyes.
17 “‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ba kai ba ne na yi magana da kai a kwanakin dā ta wurin bayina annabawan Isra’ila? A lokacin sun yi annabci shekaru masu yawa cewa zan kawo ka, ka yaƙe su.
Thus saith the Lord God: Thou then art he, of whom I have spoken in the days of old, by my servants the prophets of Israel, who prophesied in the days of those times that I would bring thee upon them.
18 Ga abin da zai faru a ranar. Sa’ad da Gog ya fāɗa wa ƙasar Isra’ila, fushina mai zafi zai ƙuna, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
And it shall come to pass in that day, in the day of the coming of Gog upon the land of Israel, saith the Lord God, that my indignation shall come up in my wrath.
19 Cikin kishina da hasalata mai zafi zan furta cewa a wannan lokaci za a yi babbar girgizar ƙasa a ƙasar Isra’ila.
And I have spoken in my zeal, and in the fire of my anger, that in that day there shall be a great commotion upon the land of Israel:
20 Kifin teku, tsuntsayen sarari, namun jeji, kowace halitta mai rarrafe da kuma dukan mutane a duniya za su yi rawar jiki a gabana. Za a tumɓuke duwatsu, a ragargaza tsaunuka, kuma kowane bango zai fāɗi ƙasa.
So that the fishes of the sea, and the birds of the air, and the beasts of the field, and every creeping thing that creepeth upon the ground, and all men that are upon the face of the earth, shall be moved at my presence: and the mountains shall be thrown down, and the hedges shall fall, and every wall shall fall to the ground.
21 Zan kira takobi a kan Gog a dukan duwatsuna, in ji Ubangiji Mai Iko Duka. Kowane takobin mutum zai yi gāba da ɗan’uwansa.
And I will call in the sword against him in all my mountains, saith the Lord God: every man’s sword shall be pointed against his brother.
22 Zan yi hukunci a kansa da annoba da kuma zub da jini; zan yi ruwa mai yawa da ƙanƙara da kibiritu mai cin wuta a kansa da a kan sojojinsa da kuma a kan al’ummai masu yawa da suke tare da shi.
And I will judge him with pestilence, and with blood, and with violent rain, and vast hailstones: I will rain fire and brimstone upon him, and upon his army, and upon the many nations that are with him.
23 Ta haka zan nuna girmana da kuma tsarkina, zan sanar da kaina a gaban al’ummai masu yawa. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji.’
And I will be magnified, and I will be sanctified: and I will be known in the eyes of many nations: and they shall know that I am the Lord.

< Ezekiyel 38 >