< Ezekiyel 38 >

1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
And the word of the Lord came to me, saying:
2 “Ɗan mutum, ka fuskanci Gog, na ƙasar Magog, babban sarkin Meshek da Tubal; ka yi annabci a kansa
“Son of man, set your face against Gog, the land of Magog, the prince of the head of Meshech and Tubal, and prophesy about him.
3 ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gāba da kai, ya Gog, babban sarkin Meshek da Tubal.
And you shall say to him: Thus says the Lord God: Behold, I am against you, O Gog, prince of the head of Meshech and Tubal.
4 Zan juyar da kai, in sa ƙugiyoyi a muƙamuƙanka in fitar da kai tare da dukan sojojinka, dawakanka, mahayan dawakanka saye da makamai, da kuma jama’a mai girma masu riƙe da garkuwoyi manya da ƙanana, dukansu da takuba a zāre.
And I will turn you around, and I will place a bit in your jaws. And I will lead you away, with all your army, the horses and the horsemen all clothed in armor, a great multitude, equipped with spears and light shields and swords,
5 Farisa, Kush da Fut za su kasance tare da su, duka riƙe da garkuwoyi da hulunan kwano,
the Persians, the Ethiopians, and the Libyans with them, all with heavy shields and helmets,
6 haka ma Gomer da dukan sojojinsa, da Bet Togarma daga can arewa tare da dukan sojojinsa, al’ummai masu yawa tare da kai.
Gomer, and all his companies, the house of Togarmah, the northern parts, and all his strength, and the many peoples with you.
7 “‘Ka shirya; ka kintsa, kai da dukan jama’arka da suka taru kewaye da kai, ka kuma zama mai ba su umarni.
Prepare and equip yourself, with all your multitude which has been assembled to you. And you shall be like a commandment to them.
8 Bayan kwanaki masu yawa za a kira ka. A shekaru masu zuwa za ka kai hari a ƙasar da ta farfaɗo daga yaƙi, wadda aka tattara mutanenta daga al’ummai masu yawa zuwa duwatsun Isra’ila, dā kango ne sosai. An fitar da su daga al’ummai, yanzu kuwa dukansu suna zama lafiya.
After many days, you will be visited. At the end of the years, you will arrive at the land which was turned back by the sword, and which has been gathered from many peoples to the mountains of Israel that have been continually abandoned. These ones have been led away from the peoples, and all of them will be living confidently within it.
9 Kai da dukan sojojinka da kuma al’ummai masu yawa da suke tare da kai za ku haura, kuna cin gaba kamar hadari; za ku zama kamar girgijen da yake rufewa ƙasa.
But you will ascend and arrive like a tempest and like a cloud, so that you may cover the land, you and all your companies, and the many peoples with you.
10 “‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa a ranar, tunani zai shiga cikin zuciyarka za ka kuma ƙirƙiro muguwar dabara.
Thus says the Lord God: In that day, words will climb into your heart, and you will invent a most wicked plan.
11 Za ka ce, “Zan kai hari wa ƙasar da ƙauyukanta ba su da katanga; zan fāɗa wa mutanen da suke zamansu kurum cikin salama, dukansu suna zama babu katanga babu ƙofofi ko ƙyamare.
And you will say: ‘I will ascend to the land without a wall. I will go to those who are resting and dwelling securely. All these live without a wall; they have no bars or gates.’
12 Zan washe in kwashe ganima in kuma juye hannuna gāba da kufai da aka sāke zaunar da mutanen da aka tattara daga al’ummai, masu yawan shanu da kayayyaki, masu zama a tsakiyar ƙasa.”
Thus, you will plunder spoils, and you will take possession of prey, so that you may lay your hand upon those who had been abandoned, and afterwards were restored, and upon a people who were gathered away from the Gentiles, a people who have begun to possess, and to be the inhabitants of, the navel of the earth.
13 Sheba da Dedan da’yan kasuwar Tarshish da dukan ƙauyukanta za su ce maka, “Ka zo ka kwashe ganima ne? Ka tattara jama’arka don ka yi waso, ka kuma kwashe azurfa da zinariya, ka kwashe shanu da kayayyaki ka kuma ƙwace ganima mai yawa?”’
Sheba, and Dedan, and the merchants of Tarshish, and all its lions will say to you: ‘Could you have arrived in order to purchase from the spoils? Behold, you have gathered your multitude in order to plunder a prey, so that you may take silver and gold, and carry away equipment and substance, and plunder immeasurable wealth.’
14 “Saboda haka ɗan mutum, ka yi annabci ka ce wa Gog, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa a ranar, sa’ad da mutanena Isra’ila suna zaman lafiya, ba za ka sani ba?
Because of this, son of man, prophesy, and you shall say to Gog: Thus says the Lord God: How is it that you do not know of that day, when my people, Israel, will be living in confidence?
15 Za ka zo daga wurinka a can arewa, kai da al’ummai masu yawa tare da kai, dukansu suna hawan dawakai, jama’a mai yawa, babbar runduna.
And you will advance from your place, from the parts of the north, you and the many peoples with you, all of them riding on horses, a great assembly and an immense army.
16 Za ka ci gaba a kan mutanena Isra’ila kamar yadda girgijen yakan rufe ƙasa. A kwanaki masu zuwa, ya Gog, zan kawo ka, ka yi yaƙi da ƙasata, domin al’ummai su san ni sa’ad da na nuna kaina mai tsarki ta wurinka a gabansu.
And you will rise up over my people, Israel, like a cloud, so that you may cover the earth. In the latter days, you will be. And I will lead you over my own land, so that the Gentiles may know me, when I will have been sanctified in you, O Gog, before their eyes.
17 “‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ba kai ba ne na yi magana da kai a kwanakin dā ta wurin bayina annabawan Isra’ila? A lokacin sun yi annabci shekaru masu yawa cewa zan kawo ka, ka yaƙe su.
Thus says the Lord God: Therefore, you are the one, about whom I spoke in the days of antiquity, by the hand of my servants the prophets of Israel, who prophesied in the days of those times that I would lead you over them.
18 Ga abin da zai faru a ranar. Sa’ad da Gog ya fāɗa wa ƙasar Isra’ila, fushina mai zafi zai ƙuna, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
And this shall be in that day, in the day of the advent of Gog over the land of Israel, says the Lord God: my indignation will rise up in my fury.
19 Cikin kishina da hasalata mai zafi zan furta cewa a wannan lokaci za a yi babbar girgizar ƙasa a ƙasar Isra’ila.
And I have spoken, in my zeal and in the fire of my wrath, that there shall be a great commotion over the land of Israel, in that day.
20 Kifin teku, tsuntsayen sarari, namun jeji, kowace halitta mai rarrafe da kuma dukan mutane a duniya za su yi rawar jiki a gabana. Za a tumɓuke duwatsu, a ragargaza tsaunuka, kuma kowane bango zai fāɗi ƙasa.
And before my face there shall be stirred up: the fish of the sea, and the flying things of the air, and the beasts of the field, and every crawling thing that moves across the soil, and all the men who are upon the face of the earth. And the mountains will be overturned, and the hedges will fall, and every wall will fall in ruin to the ground.
21 Zan kira takobi a kan Gog a dukan duwatsuna, in ji Ubangiji Mai Iko Duka. Kowane takobin mutum zai yi gāba da ɗan’uwansa.
And I will call for the sword against him on all my mountains, says the Lord God. Each one’s sword will be directed toward his brother.
22 Zan yi hukunci a kansa da annoba da kuma zub da jini; zan yi ruwa mai yawa da ƙanƙara da kibiritu mai cin wuta a kansa da a kan sojojinsa da kuma a kan al’ummai masu yawa da suke tare da shi.
And I will judge him by pestilence, and blood, and violent rainstorms, and immense hailstones. I will rain fire and brimstone upon him, and upon his army, and upon the many peoples who are with him.
23 Ta haka zan nuna girmana da kuma tsarkina, zan sanar da kaina a gaban al’ummai masu yawa. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji.’
And I will be magnified and sanctified. And I will be known in the eyes of the many nations. And they shall know that I am the Lord.”

< Ezekiyel 38 >