< Ezekiyel 37 >

1 Hannun Ubangiji yana a kaina, ya kuma fitar da ni ta wurin Ruhun Ubangiji ya sa ni a tsakiyar kwarin; yana cike da ƙasusuwa.
Herrens hånd kom over mig, og Herren førte mig i ånden ut og satte mig ned midt i dalen, og den var full av ben.
2 Ya sa na kai na komo a ciki, na kuma ga ƙasusuwa masu girma da yawa a ƙasar kwarin, ƙasusuwan da suka bushe ƙwarai.
Og han førte mig rundt omkring dem, og jeg så at de lå der i store mengder utover dalen, og de var aldeles tørre.
3 Sai ya tambaye ni cewa, “Ɗan mutum, waɗannan ƙasusuwa za su iya rayu?” Ni kuwa na ce, “Ya Ubangiji Mai Iko Duka, kai kaɗai ka sani.”
Og han sa til mig: Menneskesønn! Skal disse ben bli levende? Jeg svarte: Herre, Israels Gud, du vet det!
4 Sai ya ce mini, “Ka yi wa waɗannan ƙasusuwa annabci ka ce musu, ‘Busassun ƙasusuwa, ku ji maganar Ubangiji!
Da sa han til mig: Spå om disse ben og si til dem: I tørre ben, hør Herrens ord!
5 Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce wa waɗannan ƙasusuwa. Zan sa numfashi ya shiga muku, za ku kuwa rayu.
Så sier Herren, Israels Gud, til disse ben: Se, jeg lar det komme livsånde i eder, og I skal bli levende.
6 Zan harhaɗa muku jijiyoyi in sa muku tsoka in kuma rufe ku da fata; zan sa numfashi a cikinku, za ku kuwa rayu. Sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji.’”
Jeg vil legge sener på eder og la det komme kjøtt på eder og dekke eder med hud og gi livsånde i eder, og I skal bli levende; og I skal kjenne at jeg er Herren.
7 Saboda haka sai na yi annabci yadda aka umarce ni. Da nake annabcin, sai aka ji motsi, ƙarar girgiza, sai ƙasusuwan suka harhaɗu, ƙashi ya haɗu da ƙashi.
Og jeg spådde således som det var befalt mig, og mens jeg spådde, hørtes det en sterk lyd; det blev et bulder, og benene nærmet sig til hverandre.
8 Na duba, sai ga jijiyoyi da nama suka bayyana a kansu fata kuma ta rufe su, amma ba numfashi a cikinsu.
Og jeg så, og se, det kom sener og kjøtt på dem, og ovenpå det drog det sig hud over dem; men livsånde var det ikke i dem.
9 Sa’an nan ya ce mini, “Ka yi annabci wa numfashi; ka yi annabci, ɗan mutum, ka ce masa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ka fito daga kusurwoyi huɗu, ya numfashi, ka kuma numfasa cikin waɗannan matattu, don su rayu.’”
Da sa han til mig: Spå og tal til livsånden! Spå, menneskesønn, og si til livsånden: Så sier Herren, Israels Gud: Kom du livsånde fra de fire vinder og blås på disse drepte menn, så de kan bli levende!
10 Saboda haka na yi annabci yadda aka umarce ni, sai numfashi ya shiga musu; suka rayu suka kuma miƙe tsaye a ƙafafunsu babbar runduna ce ƙwarai.
Og jeg spådde således som han hadde befalt mig, og livsånden kom i dem, og de blev levende og stod op på sine føtter, en meget, meget stor hær.
11 Sa’an nan ya ce mini, “Ɗan mutum, waɗannan ƙasusuwa su ne dukan gidan Isra’ila. Suna cewa, ‘Ƙasusuwanmu sun bushe, sa zuciyarmu duk ya tafi; an share mu ƙaf.’
Og han sa til mig: Menneskesønn! Disse ben er hele Israels hus. Se, de sier: Våre ben er fortørket, og vårt håp er gått til grunne; vi er fortapt.
12 Saboda haka yi annabci ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ya mutanena, zan buɗe kaburburanku in fitar da ku daga cikinsu; zan mai da ku ƙasar Isra’ila.
Spå derfor og si til dem: Så sier Herren, Israels Gud: Se, jeg åpner eders graver og lar eder, mitt folk, stige op av eders graver, og jeg fører eder til Israels land.
13 Sa’an nan ku, mutanena, za ku san cewa ni ne Ubangiji, sa’ad da na buɗe kaburburanku na fitar da ku daga cikinsu.
Og I skal kjenne at jeg er Herren, når jeg åpner eders graver og lar eder, mitt folk, stige op av eders graver.
14 Zan sa Ruhuna a cikinku za ku kuwa rayu, zan kuma zaunar da ku a ƙasarku. Sa’an nan za ku san cewa Ni Ubangiji na faɗa, zan kuma aikata, in ji Ubangiji.’”
Og jeg vil gi min Ånd i eder, og I skal bli levende, og jeg vil bosette eder i eders land, og I skal kjenne at jeg, Herren, har sagt det, og at jeg også vil gjøre det, sier Herren.
15 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Og Herrens ord kom til mig, og det lød så:
16 “Ɗan mutum, ka ɗauki sanda ka rubuta a kansa, ‘Na Yahuda da Isra’ilawan da suke tare da shi.’ Sa’an nan ka ɗauki wani sanda, ka rubuta a kansa, ‘Sandan Efraim, na Yusuf da dukan gidan Isra’ilan da suke tare da shi.’
Og du menneskesønn! Ta dig en stav og skriv på den: For Juda og for Israels barn, hans medbrødre! Og ta dig en annen stav og skriv på den: For Josef - en stav for Efra'im og hele Israels hus, hans medbrødre!
17 Ka haɗa su su zama sanda guda saboda su kasance ɗaya a hannunka.
Og sett dem sammen, den ene til den andre, til én stav, så de blir til ett i din hånd!
18 “In mutanen ƙasarka suka tambaye ka cewa, ‘Ba za ka faɗa mana abin da kake nufi da wannan ba?’
Og når ditt folks barn sier til dig: Vil du ikke la oss få vite hvad du mener med dette? -
19 Ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, Zan ɗauki sandan Yusuf, wanda yake a hannun Efraim, da na kabilan Isra’ilawan da suke tare da shi, in haɗa shi da sandan Yahuda, in mai da su sanda guda, za su kuwa zama ɗaya a hannuna.’
da skal du si til dem: Så sier Herren, Israels Gud: Se, jeg tar Josefs stav, som er i Efra'ims hånd, og Israels stammer, hans medbrødre, og jeg legger dem til Judas stav og gjør dem til én stav, så de blir til ett i min hånd.
20 Ka riƙe sandunan da ka yi rubutun a gabansu
Og de staver som du skriver på, skal du holde i din hånd for deres øine.
21 ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan fitar da Isra’ilawa daga al’ummai inda suka tafi. Zan tattara su daga dukan kewaye in komo da su ƙasarsu.
Si så til dem: Så sier Herren, Israels Gud: Se, jeg henter Israels barn fra de folk som de drog bort til, og jeg vil samle dem fra alle kanter og føre dem til deres eget land.
22 Zan mai da su al’umma ɗaya a cikin ƙasar, a kan duwatsun Isra’ila. Za a kasance da sarki guda a kan dukansu ba za su ƙara zama al’ummai biyu ko su rabu su zama masarautai biyu ba.
Og jeg vil gjøre dem til ett folk i landet, på Israels fjell, og én konge skal være konge for dem alle, og de skal ikke mere være to folk og ikke mere dele sig i to riker.
23 Ba za su ƙara ƙazantar da kansu da gumaka da mugayen siffofi ko kuma da wani daga laifofinsu ba, gama zan cece su daga dukan zunubinsu na ridda, zan kuma tsarkake su. Za su zama mutanena, ni kuma zan zama Allahnsu.
Og de skal ikke mere gjøre sig urene med sine motbydelige avguder og med sine vederstyggeligheter eller med nogen av sine misgjerninger, og jeg vil utfri dem fra alle deres bosteder, hvor de har syndet, og rense dem, og de skal være mitt folk, og jeg vil være deres Gud.
24 “‘Bawana Dawuda zai zama sarki a kansu, dukansu kuwa za su kasance da makiyayi guda. Za su bi dokokina su kuma kiyaye ƙa’idodina.
Og min tjener David skal være konge over dem, og én hyrde skal det være for dem alle, og mine lover skal de følge, og mine bud skal de holde og gjøre efter dem.
25 Za su zauna a ƙasar da na ba wa bawana Yaƙub, ƙasar da kakanninsu suka zauna. Su da’ya’yansu da’ya’ya’ya’yansu za su zauna a can har abada, kuma Dawuda bawana zai zama sarkinsu har abada.
Og de skal bo i det land jeg gav min tjener Jakob, det som eders fedre bodde i; de skal bo i det, de og deres barn og deres barnebarn, til evig tid, og David, min tjener, skal være deres fyrste evindelig.
26 Zan yi alkawarin salama da su; zai zama madawwamin alkawari. Zan kafa su in ƙara yawansu, zan kuma sa wuri mai tsarkina a cikinsu har abada.
Og jeg vil gjøre en fredspakt med dem - en evig pakt med dem skal det være; og jeg vil bosette dem i mitt land og la dem bli tallrike, og jeg vil sette min helligdom midt iblandt dem for evig tid.
27 Mazaunina zai kasance da su; zan kuwa zama Allahnsu, za su kuma zama mutanena.
Og min bolig skal være over dem, og jeg vil være deres Gud, og de skal være mitt folk.
28 Sa’an nan al’ummai za su san cewa Ni Ubangiji na mai da Isra’ila mai tsarki, sa’ad da wuri mai tsarkina yana a cikinsu har abada.’”
Og folkene skal kjenne at jeg er Herren, som helliger Israel, når min helligdom blir midt iblandt dem til evig tid.

< Ezekiyel 37 >