< Ezekiyel 36 >
1 “Ɗan mutum, ka yi annabci wa duwatsun Isra’ila ka ce, ‘Ya duwatsun Isra’ila, ku ji maganar Ubangiji.
Un tu cilvēka bērns, sludini par Israēla kalniem un saki: Israēla kalni, klausiet Tā Kunga vārdu.
2 Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa abokin gāba yana magana game da ku cewa, “Yauwa! Tsofaffin tuddai sun zama mallakarmu yanzu.”’
Tā saka Tas Kungs Dievs: tādēļ ka ienaidnieks par jums saka: redzi, tie mūžīgie kalni mums ir tikuši par mantību,
3 Saboda haka ka yi annabci ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa domin sun lalace ku suka kuma maishe ku kufai marar amfani a kowane gefe saboda ku zama mallakar sauran al’ummai da kuma abin magana da tsegumi ga mutane,
Tādēļ sludini un saki: tā saka Tas Kungs Dievs: Tāpēc ka jūs visapkārt esat postīti un aprīti, ka jūs tiem atlikušiem pagāniem esat par mantību un esat nākuši ļaužu mēlēs un valodās,
4 saboda haka, ya duwatsun Isra’ila, ku ji maganar Ubangiji Mai Iko Duka, ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana faɗa wa duwatsu da tuddai, wa kwazazzabai da kwaruruka, wa kufai da garuruwan da suka zama kango waɗanda aka washe aka wulaƙanta suka zama ganimar sauran al’ummai da suke kewaye da ku,
Tāpēc, Israēla kalni, klausiet Tā Kunga Dieva vārdu. Tā saka Tas Kungs Dievs uz kalniem un pakalniem, gravām un ielejām, tukšām posta vietām un atstātām pilsētām, kas ir palikušas par laupījumu un apsmieklu visām atlikušām tautām visapkārt, -
5 ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa cikin kishina mai ƙuna na yi magana gāba da sauran al’ummai, da kuma gāba da Edom, gama da farin ciki da reni a zukatansu suka mai da ƙasata mallakarsu don su washe wuraren kiwonta.’
Tāpēc tā saka Tas Kungs Dievs: tiešām, Es Sava karstuma ugunī runāju pret tām atlikušām tautām un pret visu Edomu, kas Manu zemi sev ņēmuši par mantību ar visas sirds prieku, ar lielu nicināšanu, to izpostīt un aplaupīt.
6 Saboda haka ka yi annabci game da ƙasar Isra’ila ka kuma ce wa duwatsu da tuddai, wa kwazazzabai da kwaruruka, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ga shi, na yi magana da kishina da hasalata saboda sun sha zargi wurin al’ummai.
Tāpēc sludini Israēla zemei un saki uz kalniem un pakalniem, gravām un ielejām: tā saka Tas Kungs Dievs: redzi, Es Savā karstumā un Savā bardzībā esmu runājis, tāpēc ka jums apsmiekls bija jānes no pagāniem.
7 Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa na ɗaga hannuna sama na rantse cewa al’ummai da suke kewaye da ku za su sha ba’a.
Tādēļ Tas Kungs Dievs tā saka: Es, Es paceļu Savu roku, tiešām, tām tautām, kas visapkārt ap jums, pašām būs nest savu apsmieklu.
8 “‘Amma ku, ya duwatsun Isra’ila, za ku miƙa rassanku ku ba da amfani ga mutanena Isra’ila, gama ba da daɗewa ba za su komo gida.
Bet jūs, jūs Israēla kalni, atkal zaļosiet un nesīsiet savus augļus Maniem Israēla ļaudīm, jo īsā laikā tie pārnāks.
9 Na damu da ku kuma zan dube ku da tausayi; za ku nome ku kuma shuka,
Jo redzi, Es būšu pie jums, un Es skatīšos uz jums, un jūs tapsiet kopti un apsēti.
10 zan kuma riɓaɓɓanya mutane a kanku, dukan gidan Isra’ila ke nan. Za a zauna a birane a kuma sāke gina rusassun wurare.
Un Es vairošu pie jums cilvēkus, visu Israēla namu visnotaļ: un pilsētās dzīvos un postītas vietas uztaisīs.
11 Zan sa mutane da dabbobi su yi yawa a kanku, za su kuma ba da’ya’ya su kuma yi yawa. Zan zaunar da mutane a kanku kamar dā zan kuma sa ku wadaita fiye da dā. Sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji.
Un Es pie jums vairošu cilvēkus un lopus, tie vairosies un vaislosies, un Es iekš jums likšu dzīvot kā jūsu vecos laikos, un Es jums darīšu vairāk labuma nekā jūsu senajos laikos, un jūs samanīsiet, ka Es esmu Tas Kungs.
12 Zan sa mutanena Isra’ila su yi tafiya a kanku. Za su mallake ku, za ku kuma zama gādonsu; ba za ku ƙara sa su rasa’ya’yansu ba.
Un Es pie jums atvedīšu cilvēkus, Savus Israēla ļaudis, tie tevi iemantos, un tu tiem būsi par mantību un tiem vairs nelaupīsi bērnus.
13 “‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa domin mutane suna magana game da ku cewa, “Kun cinye mutane kuka kuma sa al’ummarku ta rasa’ya’yanta,”
Tā saka Tas Kungs Dievs: tādēļ ka uz jums saka: tu esi cilvēku rijēja un savu ļaužu bērnu aplaupītāja,
14 saboda haka ba za ku ƙara cinye mutane ko ku sa al’ummarku ta rasa’ya’ya ba, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
Tādēļ tu cilvēkus vairs nerīsi un saviem ļaudīm vairs nelaupīsi bērnus, saka Tas Kungs Dievs.
15 Ba zan ƙara bari ku ji maganar banza ta al’ummai ba, ba kuwa za ku ƙara shan ba’ar mutane ko in sa al’ummarku ta fāɗi ba, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”
Un Es tev vairs nelikšu dzirdēt pagānu apsmieklu, un tu nenesīsi vairs tautu negodu un saviem ļaudīm vairs nelaupīsi bērnus, saka Tas Kungs Dievs.
16 Maganar Ubangiji ta sāke zuwa mini cewa,
Atkal Tā Kunga vārds uz mani notika sacīdams:
17 “Ɗan mutum, sa’ad da mutanen Isra’ila suke zama a ƙasarsu, sun ƙazantar da ita ta wurin halinsu da kuma ayyukansu. Halinsu ya yi kamar rashin tsarkin mace a lokacin al’adarta a gabana.
Cilvēka bērns, Israēla nams, kad tie savā zemē dzīvoja, tad tie to sagānīja ar savu ceļu un ar saviem darbiem; viņu ceļš bija Manā priekšā kā sārņainas sievas nešķīstība.
18 Saboda haka na husata da su domin sun yi kisankai a ƙasar kuma domin sun ƙazantar da ita da gumakansu.
Tādēļ Es Savu bardzību pār viņiem izgāzu to asiņu dēļ, ko tie tai zemē bija izlējuši, un viņu elku dēļ ar ko to bija sagānījuši.
19 Na warwatsa su cikin al’ummai, suka kuwa warwatsu cikin dukan ƙasashe; na hukunta su gwargwadon halinsu da ayyukansu.
Un Es tos izkaisīju starp tautām, un tie tapa izputināti pa valstīm, Es tos sodīju pēc viņu ceļa un pēc viņu darbiem.
20 Kuma ko’ina da suka tafi a cikin al’ummai sun ɓata sunana mai tsarki, gama an yi magana a kansu cewa, ‘Waɗannan mutanen Ubangiji ne, duk da haka dole su bar ƙasarsa.’
Kad tie nu pie tām tautām nonāca, kurp tie bija gājuši, tad tie sagānīja manu svēto vārdu, tāpēc ka no tiem tapa sacīts: šie ir Tā Kunga ļaudis un izgājuši no viņa zemes.
21 Na damu saboda sunana mai tsarki, wanda gidan Isra’ila ya ɓata a cikin al’ummai inda suka tafi.
Bet Man ir žēl Sava svētā Vārda, ko Israēla bērni sagānījuši starp tām tautām, kur tie bija nākuši.
22 “Saboda haka ka faɗa musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ba dominku ba ne, ya gidan Isra’ila da nake yin waɗannan abubuwa, amma saboda sunana ne mai tsarki, wanda kuka ɓata a cikin al’ummai inda kuka tafi.
Tāpēc saki uz Israēla namu: tā saka Tas Kungs Dievs: Es to nedaru jūsu dēļ, Israēla nams, bet Sava svētā Vārda dēļ, ko jūs esat sagānījuši starp tām tautām, kur esat nākuši.
23 Zan nuna tsarkin girman sunana, wanda aka ɓata a cikin al’umma, sunana da kuka ɓata a cikinsu. Sa’an nan al’ummai za su san cewa ni ne Ubangiji, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, sa’ad da na nuna kaina mai tsarki ta wurinku a idanunsu.
Jo Es pagodināšu Savu lielo Vārdu, kas starp pagāniem ir sagānīts, ko jūs viņu vidū esat sagānījuši. Un pagāni samanīs, ka Es esmu Tas Kungs, saka Tas Kungs Dievs, kad Es pie jums svēts parādīšos priekš viņu acīm.
24 “‘Gama zan fitar da ku daga al’ummai; zan tattara ku daga dukan ƙasashe in komo da ku zuwa ƙasarku.
Jo Es jūs atvedīšu no tām tautām un jūs sapulcināšu no visām valstīm, un Es jūs atvedīšu atkal jūsu zemē.
25 Zan yayyafa muku ruwa mai tsabta, zan kuwa tsarkake ku daga dukan ƙazantarku daga kuma dukan gumakanku.
Un Es uz jums slacināšu šķīstu ūdeni, ka topat šķīsti; no visas jūsu nešķīstības un no visiem jūsu elkiem Es jūs šķīstīšu.
26 Zan ba ku sabuwa zuciya in kuma sa sabon ruhu a cikinku; zan fid da zuciyar dutse in kuma ba ku zuciyar nama.
Un Es jums došu jaunu sirdi un došu jums jaunu garu, un atņemšu to akmens sirdi no jūsu miesām un došu jums miesīgu sirdi.
27 Zan kuma sa Ruhuna a cikinku in kuma motsa ku ku bi ƙa’idodina ku kuma kiyaye dokokina.
Un Es jums došu Savu Garu un darīšu, ka jūs staigāsiet Manos likumos un sargāsiet un darīsiet Manas tiesas.
28 Za ku zauna a ƙasar da na ba wa kakanninku; za ku zama mutanena, ni kuwa zan zama Allahnku.
Un jūs dzīvosiet tai zemē, ko Es jūsu tēviem esmu devis, un jūs Man būsiet par ļaudīm, un Es jums būšu par Dievu.
29 Zan cece ku daga dukan rashin tsabtarku. Zan sa hatsi ya yi yalwa ba zan kawo yunwa a kanku ba.
Un Es jūs atpestīšu no visas jūsu nešķīstības un aicināšu labību un to vairošu un nevedīšu pār jums badu.
30 Zan ƙara’ya’yan itatuwa da amfanin gona, saboda kada ku ƙara shan kunya a cikin al’ummai saboda yunwa.
Un Es vairošu koku augļus un tīruma augļus, ka jūs bada dēļ starp tautām vairs netopat nicināti.
31 Sa’an nan za ku tuna mugayen hanyoyinku da mugayen ayyukanku, za ku kuwa ji ƙyamar kanku saboda zunubanku da kuma ayyukanku na banƙyama.
Tad jūs pieminēsiet savus ļaunos ceļus un savus nelabos darbus un būsiet paši sev riebīgi par saviem noziegumiem un par savām negantībām.
32 Ina so ku san cewa ba na yi wannan saboda ku, in ji Ubangiji Mai Iko Duka. Ku ji kunya ku kuma giggita saboda halinku, ya gidan Isra’ila!
Un to Es nedaru jūsu dēļ, saka Tas Kungs Dievs, to jums būs zināt. Kaunaties un nosarkstiet savu ceļu dēļ, jūs, Israēla nams!
33 “‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa a ranar da na tsarkake ku daga dukan zunubanku, zan sāke zaunar da ku a garuruwanku, a kuma sāke gina kufai.
Tā saka Tas Kungs Dievs: tai dienā, kad Es jūs šķīstīšu no visas jūsu nešķīstības, tad Es pilsētās likšu dzīvot, un postažas taps uztaisītas.
34 Ƙasar da take kango a dā za ku nome ta a maimakon zama kango a idon dukan masu ratsawa a cikinta.
Un tā tukšā zeme atkal taps apkopta, kur posts bija priekš ikviena acīm, kas gāja garām.
35 Za su ce, “Wannan ƙasar da take kango a dā ta zama kamar lambu Eden; biranen da dā suke kufai, kango da kuma aka lalata, yanzu suna da katanga ana kuma zama a ciki.”
Un sacīs: šī zeme, kas bija postā, ir palikusi kā Ēdenes dārzs, un tās iztukšotās un izpostītās un sagruvušās pilsētas ir stipras un apdzīvotas.
36 Sa’an nan al’ummai kewaye da ku da suka rage za su san cewa Ni Ubangiji na sāke gina abin da aka lalace na kuma sāke shuka abin da yake kango. Ni Ubangiji na faɗa, kuma zan aikata.’
Tad tās tautas, kas atlikušas visapkārt ap jums, samanīs, ka Es, Tas Kungs, uztaisu sagruvušas vietas un apdēstu, kas ir izpostīts; Es, Tas Kungs, to esmu runājis, un Es to darīšu.
37 “Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa har yanzu zan ji roƙon gidan Isra’ila in kuma yi musu wannan. Zan sa mutanensu su yi yawa kamar tumaki,
Tā saka Tas Kungs Dievs: Es ļaušos atkal pielūgties no Israēla nama, ka Es tiem parādos; Es vairošu tos ļaudis kā ganāmu pulku.
38 yawansu ya yi kamar garken tumaki don hadaya a Urushalima a ƙayyadaddun lokuta bukukkuwarta. Haka biranen da suke kufai za su cika da ɗumbun mutane. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji.”
Tā kā tās svētās avis, kā Jeruzālemes avis savos svētkos, tā būs tās tukšās vietas ar cilvēkiem kā ar ganāmu pulku pilnas, un tie samanīs, ka Es esmu Tas Kungs.