< Ezekiyel 36 >

1 “Ɗan mutum, ka yi annabci wa duwatsun Isra’ila ka ce, ‘Ya duwatsun Isra’ila, ku ji maganar Ubangiji.
And thou son of man, prophesy to the mountains of Israel, and say: Ye mountains of Israel, hear the word of the Lord:
2 Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa abokin gāba yana magana game da ku cewa, “Yauwa! Tsofaffin tuddai sun zama mallakarmu yanzu.”’
Thus saith the Lord God: Because the enemy hath said of you: Aha, the everlasting heights are given to us for an inheritance.
3 Saboda haka ka yi annabci ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa domin sun lalace ku suka kuma maishe ku kufai marar amfani a kowane gefe saboda ku zama mallakar sauran al’ummai da kuma abin magana da tsegumi ga mutane,
Therefore prophesy, and say: Thus saith the Lord God: Because you have been desolate, and trodden under foot on every side, and made an inheritance to the rest of the nations, and are become the subject of the talk, and the reproach of the people:
4 saboda haka, ya duwatsun Isra’ila, ku ji maganar Ubangiji Mai Iko Duka, ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana faɗa wa duwatsu da tuddai, wa kwazazzabai da kwaruruka, wa kufai da garuruwan da suka zama kango waɗanda aka washe aka wulaƙanta suka zama ganimar sauran al’ummai da suke kewaye da ku,
Therefore, ye mountains of Israel, hear the word of the Lord God: Thus saith the Lord God to the mountains, and to the hills, to the brooks, and to the valleys, and to desolate places, and ruinous walls, and to the cities that are forsaken, that are spoiled, and derided by the rest of the nations round about.
5 ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa cikin kishina mai ƙuna na yi magana gāba da sauran al’ummai, da kuma gāba da Edom, gama da farin ciki da reni a zukatansu suka mai da ƙasata mallakarsu don su washe wuraren kiwonta.’
Therefore thus saith the Lord God: In the fire of my zeal I have spoken of the rest of the nations, and of all Edom, who have taken my land to themselves, for an inheritance with joy, and with all the heart, and with the mind: and have cast it out to lay it waste.
6 Saboda haka ka yi annabci game da ƙasar Isra’ila ka kuma ce wa duwatsu da tuddai, wa kwazazzabai da kwaruruka, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ga shi, na yi magana da kishina da hasalata saboda sun sha zargi wurin al’ummai.
Prophesy therefore concerning the land of Israel, and say to the mountains, and to the hills, to the ridges, and to the valleys: Thus saith the Lord God: Behold I have spoken in my zeal, and in my indignation, because you have borne the shame of the Gentiles.
7 Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa na ɗaga hannuna sama na rantse cewa al’ummai da suke kewaye da ku za su sha ba’a.
Therefore thus saith the Lord God: I have lifted up my hand, that the Gentiles who are round about you, shall themselves bear their shame.
8 “‘Amma ku, ya duwatsun Isra’ila, za ku miƙa rassanku ku ba da amfani ga mutanena Isra’ila, gama ba da daɗewa ba za su komo gida.
But as for you, O mountains of Israel, shoot ye forth your branches, and yield your fruit to my people of Israel: for they are at hand to come.
9 Na damu da ku kuma zan dube ku da tausayi; za ku nome ku kuma shuka,
For lo I am for you, and I will turn to you, and you shall be ploughed and sown.
10 zan kuma riɓaɓɓanya mutane a kanku, dukan gidan Isra’ila ke nan. Za a zauna a birane a kuma sāke gina rusassun wurare.
And I will multiply men upon you, and all the house of Israel: and the cities shall be inhabited, and the ruinous places shall be repaired.
11 Zan sa mutane da dabbobi su yi yawa a kanku, za su kuma ba da’ya’ya su kuma yi yawa. Zan zaunar da mutane a kanku kamar dā zan kuma sa ku wadaita fiye da dā. Sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji.
And I will make you abound with men and with beasts: and they shall be multiplied, and increased: and I will settle you as from the beginning, and will give you greater gifts, than you had from the beginning: and you shall know that I am the Lord.
12 Zan sa mutanena Isra’ila su yi tafiya a kanku. Za su mallake ku, za ku kuma zama gādonsu; ba za ku ƙara sa su rasa’ya’yansu ba.
And I will bring men upon you, my people Israel, and they shall possess thee for their inheritance: and thou shalt be their inheritance, and shalt no more henceforth be without them.
13 “‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa domin mutane suna magana game da ku cewa, “Kun cinye mutane kuka kuma sa al’ummarku ta rasa’ya’yanta,”
Thus saith the Lord God: Because they say of you: Thou art a devourer of men, and one that suffocatest thy nation:
14 saboda haka ba za ku ƙara cinye mutane ko ku sa al’ummarku ta rasa’ya’ya ba, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
Therefore thou shalt devour men no more, nor destroy thy nation any more, saith the Lord God:
15 Ba zan ƙara bari ku ji maganar banza ta al’ummai ba, ba kuwa za ku ƙara shan ba’ar mutane ko in sa al’ummarku ta fāɗi ba, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”
Neither will I cause men to hear in thee the shame of the nations any more, nor shalt thou bear the reproach of the people, nor lose thy nation any more, saith the Lord God.
16 Maganar Ubangiji ta sāke zuwa mini cewa,
And the word of the Lord came to me, saying:
17 “Ɗan mutum, sa’ad da mutanen Isra’ila suke zama a ƙasarsu, sun ƙazantar da ita ta wurin halinsu da kuma ayyukansu. Halinsu ya yi kamar rashin tsarkin mace a lokacin al’adarta a gabana.
Son of man, when the house of Israel dwelt in their own land, they defiled it with their ways, and with their doings: their way was before me like the uncleanness of a menstruous woman.
18 Saboda haka na husata da su domin sun yi kisankai a ƙasar kuma domin sun ƙazantar da ita da gumakansu.
And I poured out my indignation upon them for the blood which they had shed upon the land, and with their idols they defiled it.
19 Na warwatsa su cikin al’ummai, suka kuwa warwatsu cikin dukan ƙasashe; na hukunta su gwargwadon halinsu da ayyukansu.
And I scattered them among the nations, and they are dispersed through the countries: I have judged them according to their ways, and their devices.
20 Kuma ko’ina da suka tafi a cikin al’ummai sun ɓata sunana mai tsarki, gama an yi magana a kansu cewa, ‘Waɗannan mutanen Ubangiji ne, duk da haka dole su bar ƙasarsa.’
And when they entered among the nations whither they went, they profaned my holy name, when it was said of them: This is the people of the Lord, and they are come forth out of his land.
21 Na damu saboda sunana mai tsarki, wanda gidan Isra’ila ya ɓata a cikin al’ummai inda suka tafi.
And I have regarded my own holy name, which the house of Israel hath profaned among the nations to which they went in.
22 “Saboda haka ka faɗa musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ba dominku ba ne, ya gidan Isra’ila da nake yin waɗannan abubuwa, amma saboda sunana ne mai tsarki, wanda kuka ɓata a cikin al’ummai inda kuka tafi.
Therefore thou shalt say to the house of Israel: Thus saith the Lord God: It is not for your sake that I will do this, O house of Israel, but for my holy name’s sake, which you have profaned among the nations whither you went.
23 Zan nuna tsarkin girman sunana, wanda aka ɓata a cikin al’umma, sunana da kuka ɓata a cikinsu. Sa’an nan al’ummai za su san cewa ni ne Ubangiji, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, sa’ad da na nuna kaina mai tsarki ta wurinku a idanunsu.
And I will sanctify my great name, which was profaned among the Gentiles, which you have profaned in the midst of them: that the Gentiles may know that I am the Lord, saith the Lord of hosts, when I shall be sanctified in you before their eyes.
24 “‘Gama zan fitar da ku daga al’ummai; zan tattara ku daga dukan ƙasashe in komo da ku zuwa ƙasarku.
For I will take you from among the Gentiles, and will gather you together out of all the countries, and will bring you into your own land.
25 Zan yayyafa muku ruwa mai tsabta, zan kuwa tsarkake ku daga dukan ƙazantarku daga kuma dukan gumakanku.
And I will pour upon you clean water, and you shall be cleansed from all your filthiness, and I will cleanse you from all your idols.
26 Zan ba ku sabuwa zuciya in kuma sa sabon ruhu a cikinku; zan fid da zuciyar dutse in kuma ba ku zuciyar nama.
And I will give you a new heart, and put a new spirit within you: and I will take away the stony heart out of your flesh, and will give you a heart of flesh.
27 Zan kuma sa Ruhuna a cikinku in kuma motsa ku ku bi ƙa’idodina ku kuma kiyaye dokokina.
And I will put my spirit in the midst of you: and I will cause you to walk in my commandments, and to keep my judgments, and do them.
28 Za ku zauna a ƙasar da na ba wa kakanninku; za ku zama mutanena, ni kuwa zan zama Allahnku.
And you shall dwell in the land which I gave to your fathers, and you shall be my people, and I will be your God.
29 Zan cece ku daga dukan rashin tsabtarku. Zan sa hatsi ya yi yalwa ba zan kawo yunwa a kanku ba.
And I will save you from all your uncleannesses: and I will call for corn, and will multiply it, and will lay no famine upon you.
30 Zan ƙara’ya’yan itatuwa da amfanin gona, saboda kada ku ƙara shan kunya a cikin al’ummai saboda yunwa.
And I will multiply the fruit of the tree, and the increase of the held, that you bear no more the reproach of famine among the nations.
31 Sa’an nan za ku tuna mugayen hanyoyinku da mugayen ayyukanku, za ku kuwa ji ƙyamar kanku saboda zunubanku da kuma ayyukanku na banƙyama.
And you shall remember your wicked ways, and your doings that were not good: and your iniquities, and your wicked deeds shall displease you.
32 Ina so ku san cewa ba na yi wannan saboda ku, in ji Ubangiji Mai Iko Duka. Ku ji kunya ku kuma giggita saboda halinku, ya gidan Isra’ila!
It is not for your sakes that I will do this, saith the Lord God, be it known to you: be confounded, and ashamed at your own ways, O house of Israel.
33 “‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa a ranar da na tsarkake ku daga dukan zunubanku, zan sāke zaunar da ku a garuruwanku, a kuma sāke gina kufai.
Thus saith the Lord God: In the day that I shall cleanse you from all your iniquities, and shall cause the cities to be inhabited, and shall repair the ruinous places,
34 Ƙasar da take kango a dā za ku nome ta a maimakon zama kango a idon dukan masu ratsawa a cikinta.
And the desolate land shall be tilled, which before was waste in the sight of all that passed by,
35 Za su ce, “Wannan ƙasar da take kango a dā ta zama kamar lambu Eden; biranen da dā suke kufai, kango da kuma aka lalata, yanzu suna da katanga ana kuma zama a ciki.”
They shall say: This land that was untilled is become as a garden of pleasure: and the cities that were abandoned, and desolate, and destroyed, are peopled and fenced.
36 Sa’an nan al’ummai kewaye da ku da suka rage za su san cewa Ni Ubangiji na sāke gina abin da aka lalace na kuma sāke shuka abin da yake kango. Ni Ubangiji na faɗa, kuma zan aikata.’
And the nations, that shall be left round about you, shall know that I the Lord have built up what was destroyed, and planted what was desolate, that I the Lord have spoken and done it.
37 “Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa har yanzu zan ji roƙon gidan Isra’ila in kuma yi musu wannan. Zan sa mutanensu su yi yawa kamar tumaki,
Thus saith the Lord God: Moreover in this shall the house of Israel find me, that I will do it for them: I will multiply them as a flock of men,
38 yawansu ya yi kamar garken tumaki don hadaya a Urushalima a ƙayyadaddun lokuta bukukkuwarta. Haka biranen da suke kufai za su cika da ɗumbun mutane. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji.”
As a holy dock, as the flock of Jerusalem in her solemn feasts: so shall the waste cities be full of flocks of men: and they shall know that I am the Lord.

< Ezekiyel 36 >