< Ezekiyel 36 >

1 “Ɗan mutum, ka yi annabci wa duwatsun Isra’ila ka ce, ‘Ya duwatsun Isra’ila, ku ji maganar Ubangiji.
Men du menneskesøn, profeter om Israels bjerge og sig: Israels bjerge, hør Herrens ord.
2 Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa abokin gāba yana magana game da ku cewa, “Yauwa! Tsofaffin tuddai sun zama mallakarmu yanzu.”’
Så siger den Herre HERREN: Fordi Fjenden sagde om eder: "Ha! Ørkener for stedse! De er blevet vor Ejendom!"
3 Saboda haka ka yi annabci ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa domin sun lalace ku suka kuma maishe ku kufai marar amfani a kowane gefe saboda ku zama mallakar sauran al’ummai da kuma abin magana da tsegumi ga mutane,
derfor skal du profetere og sige: Så siger den Herre HERREN: Fordi man har higet og snappet efter eder fra alle Sider, for at I skulde tilfalde Resten af Folkene som Ejendom, og fordi I er kommet i Folkemunde,
4 saboda haka, ya duwatsun Isra’ila, ku ji maganar Ubangiji Mai Iko Duka, ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana faɗa wa duwatsu da tuddai, wa kwazazzabai da kwaruruka, wa kufai da garuruwan da suka zama kango waɗanda aka washe aka wulaƙanta suka zama ganimar sauran al’ummai da suke kewaye da ku,
derfor, Israels Bjerge, hør HERRENs Ord: Så siger den Herre HERREN til Bjergene, Højene, kløfterne og Dalene, til de øde Tomter og de forladte Byer, som er blevet til Rov og til Spot for Resten af Folkene rundt om,
5 ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa cikin kishina mai ƙuna na yi magana gāba da sauran al’ummai, da kuma gāba da Edom, gama da farin ciki da reni a zukatansu suka mai da ƙasata mallakarsu don su washe wuraren kiwonta.’
derfor, så siger den Herre HERREN: Sandelig, i brændende Nidkærhed vil jeg tale mod Resten af Folkene og mod hele Edom, som med al Hjertets Glæde og Sjælens Ringeagt udså sig mit Land til Ejendom for at drive indbyggerne bort og gøre det til Rov.
6 Saboda haka ka yi annabci game da ƙasar Isra’ila ka kuma ce wa duwatsu da tuddai, wa kwazazzabai da kwaruruka, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ga shi, na yi magana da kishina da hasalata saboda sun sha zargi wurin al’ummai.
Profeter derfor om Israels Land og sig til Bjergene, Højene, Kløfteme og Dalene: Så siger den Herre HERREN: Se, jeg faler i Nidkærhed og Harme, fordi I bærer Folkenes Hån.
7 Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa na ɗaga hannuna sama na rantse cewa al’ummai da suke kewaye da ku za su sha ba’a.
Derfor, så siger den Herre HERREN: Jeg løfter min Hånd og sværger: Sandelig, Folkene rundt om eder skal selv bære deres Hån.
8 “‘Amma ku, ya duwatsun Isra’ila, za ku miƙa rassanku ku ba da amfani ga mutanena Isra’ila, gama ba da daɗewa ba za su komo gida.
Og I, Israels Bjerge, skal skyde Grene og bære Frugt for mit Folk Israel, thi de skal snart komme hjem.
9 Na damu da ku kuma zan dube ku da tausayi; za ku nome ku kuma shuka,
Thi se, jeg kommer og vender mig til eder, og I skal dyrkes og tilsås;
10 zan kuma riɓaɓɓanya mutane a kanku, dukan gidan Isra’ila ke nan. Za a zauna a birane a kuma sāke gina rusassun wurare.
jeg gør Mennesker, alt Israels Hus, mangfoldige på eder, Byerne skal bebos og Ruinerne genopbygges;
11 Zan sa mutane da dabbobi su yi yawa a kanku, za su kuma ba da’ya’ya su kuma yi yawa. Zan zaunar da mutane a kanku kamar dā zan kuma sa ku wadaita fiye da dā. Sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji.
jeg gør Mennesker og Dyr mangfoldige på eder, ja de skal blive mangfoldige og frugtbare; jeg lader eder bebos som i fordums Tider og gør det bedre for eder end i Fortiden; og I skal kende, at jeg er HERREN.
12 Zan sa mutanena Isra’ila su yi tafiya a kanku. Za su mallake ku, za ku kuma zama gādonsu; ba za ku ƙara sa su rasa’ya’yansu ba.
Jeg lader Mennesker, mit Folk Israel, færdes på eder; de skal tage dig i Eje, og du skal være deres Arvelod og ikke mere gøre dem barnløse.
13 “‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa domin mutane suna magana game da ku cewa, “Kun cinye mutane kuka kuma sa al’ummarku ta rasa’ya’yanta,”
Så siger den Herre HERREN: Fordi de siger til dig: "Du er en Menneskeæder, som gør dit Folk barnløst!"
14 saboda haka ba za ku ƙara cinye mutane ko ku sa al’ummarku ta rasa’ya’ya ba, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
derfor skal du ikke mere æde Mennesker eller gøre dit Folk barnløst, lyder det fra den Herre HERREN.
15 Ba zan ƙara bari ku ji maganar banza ta al’ummai ba, ba kuwa za ku ƙara shan ba’ar mutane ko in sa al’ummarku ta fāɗi ba, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”
Og jeg lader dig ikke mere høre Folkenes Hån, og du skal ikke mere bære Folkeslagenes Spot eller gøre dit Folk harnløst, lyder det fra den Herre HERREN.
16 Maganar Ubangiji ta sāke zuwa mini cewa,
HERRENs Ord kom til mig således:
17 “Ɗan mutum, sa’ad da mutanen Isra’ila suke zama a ƙasarsu, sun ƙazantar da ita ta wurin halinsu da kuma ayyukansu. Halinsu ya yi kamar rashin tsarkin mace a lokacin al’adarta a gabana.
Menneskesøn! Da Israels Slægt boedei deres Land, gjorde de det urent ved deres Færd og Gerninger; som en Kvindes renhed var deres Færd for mit Åsyn.
18 Saboda haka na husata da su domin sun yi kisankai a ƙasar kuma domin sun ƙazantar da ita da gumakansu.
Så udøste jeg min Vrede over dem for det Blods Skyld, de udgød i Landet, og fordi de gjorde det urent med deres Afgudsbilleder.
19 Na warwatsa su cikin al’ummai, suka kuwa warwatsu cikin dukan ƙasashe; na hukunta su gwargwadon halinsu da ayyukansu.
Jeg spredte dem blandt Folkene, og de strøedes ud i Landene; efter deres Færd og Gerninger dømte jeg dem.
20 Kuma ko’ina da suka tafi a cikin al’ummai sun ɓata sunana mai tsarki, gama an yi magana a kansu cewa, ‘Waɗannan mutanen Ubangiji ne, duk da haka dole su bar ƙasarsa.’
Således kom de til Folkene: hvor de kom hen, vanærede de mit hellige Navn, idet man sagde om dem: "De der er HERRENs Folk, og dog måtte de ud af hans Land!"
21 Na damu saboda sunana mai tsarki, wanda gidan Isra’ila ya ɓata a cikin al’ummai inda suka tafi.
Da ynkedes jeg over mit hellige Navn, som Israels Hus vanærede blandt de Folk, de kom til.
22 “Saboda haka ka faɗa musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ba dominku ba ne, ya gidan Isra’ila da nake yin waɗannan abubuwa, amma saboda sunana ne mai tsarki, wanda kuka ɓata a cikin al’ummai inda kuka tafi.
Sig derfor til Israels Hus: Så siger den Herre HERREN: Det er ikke for eders Skyld, jeg griber ind, Israels Hus, men for mit hellige Navns Skyld, som I har vanæret blandt de Folk, I kom til.
23 Zan nuna tsarkin girman sunana, wanda aka ɓata a cikin al’umma, sunana da kuka ɓata a cikinsu. Sa’an nan al’ummai za su san cewa ni ne Ubangiji, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, sa’ad da na nuna kaina mai tsarki ta wurinku a idanunsu.
Jeg vil hellige mit store Navn, som vanæres blandt Folkene, idet I har vanæret det iblandt dem; og Folkene skal kende, at jeg er HERREN, lyder det fra den Herre HERREN, når jeg helliger mig på eder for deres Øjne.
24 “‘Gama zan fitar da ku daga al’ummai; zan tattara ku daga dukan ƙasashe in komo da ku zuwa ƙasarku.
Jeg vil hente eder fra Folkene, samle eder fra alle Lande og bringe eder til eders Land.
25 Zan yayyafa muku ruwa mai tsabta, zan kuwa tsarkake ku daga dukan ƙazantarku daga kuma dukan gumakanku.
Da stænker jeg rent Vand på eder, så I bliver rene; jeg renser eder for al eders Urenhed og alle eders Afgudsbilleder.
26 Zan ba ku sabuwa zuciya in kuma sa sabon ruhu a cikinku; zan fid da zuciyar dutse in kuma ba ku zuciyar nama.
Jeg giver eder et nyt Hjerte, og en ny Ånd giver jeg i eders Indre; Stenhjertet tager jeg ud af eders Kød og giver eder et Kødhjerte.
27 Zan kuma sa Ruhuna a cikinku in kuma motsa ku ku bi ƙa’idodina ku kuma kiyaye dokokina.
Jeg giver min Ånd i eders Indre og virker, at I følger mine Vedtægter og tager Vare på at holde mine Lovbud,
28 Za ku zauna a ƙasar da na ba wa kakanninku; za ku zama mutanena, ni kuwa zan zama Allahnku.
I skal bo i det Land, jeg gav eders Fædre, og I skal være mit Folk, og jeg vil være eders Gud.
29 Zan cece ku daga dukan rashin tsabtarku. Zan sa hatsi ya yi yalwa ba zan kawo yunwa a kanku ba.
Jeg frelser eder fra al eders Urenbed; jeg kalder Kornet frem og mangfoldiggør det og sender ikke mere Hungersnød over eder.
30 Zan ƙara’ya’yan itatuwa da amfanin gona, saboda kada ku ƙara shan kunya a cikin al’ummai saboda yunwa.
Jeg mangfoldiggør Træernes Frugter og Markens Afgrøde, for at I ikke mere skal tage en Hungersnøds Skændsel på eder blandt Folkene.
31 Sa’an nan za ku tuna mugayen hanyoyinku da mugayen ayyukanku, za ku kuwa ji ƙyamar kanku saboda zunubanku da kuma ayyukanku na banƙyama.
Da skal I ihukomme eders onde Veje og eders Gerninger, som ikke var gode, og ledes ved eder selv over eders Misgerninger og Vederstyggeligheder.
32 Ina so ku san cewa ba na yi wannan saboda ku, in ji Ubangiji Mai Iko Duka. Ku ji kunya ku kuma giggita saboda halinku, ya gidan Isra’ila!
Ikke for eders Skyld griber jeg ind, lyder det fra den Herre HERREN, det være eder kundgjort! Skam jer og blues over eders Veje, Israels Hus!
33 “‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa a ranar da na tsarkake ku daga dukan zunubanku, zan sāke zaunar da ku a garuruwanku, a kuma sāke gina kufai.
Så siger den Herre HERREN: Den Dag jeg renser eder for alle eders Misgerninger, lader jeg Byerne bebos, og Ruinerne skal genopbygges;
34 Ƙasar da take kango a dā za ku nome ta a maimakon zama kango a idon dukan masu ratsawa a cikinta.
det ødelagte Land skal dyrkes, i Stedet for at det har været en Ødemark for alles Øjne, som kom forbi.
35 Za su ce, “Wannan ƙasar da take kango a dā ta zama kamar lambu Eden; biranen da dā suke kufai, kango da kuma aka lalata, yanzu suna da katanga ana kuma zama a ciki.”
Da skal man sige: "Dette Land, som var ødelagt, er blevet som Edens Have, og Byerne, som var omstyrtet, ødelagt og nedrevet, er befæstet og beboet."
36 Sa’an nan al’ummai kewaye da ku da suka rage za su san cewa Ni Ubangiji na sāke gina abin da aka lalace na kuma sāke shuka abin da yake kango. Ni Ubangiji na faɗa, kuma zan aikata.’
Og Folkene, der er tilhage rundt om eder, skal kende, at jeg, HERREN, har opbygget de nedrevne Byer og tilplantet det ødelagte Land; jeg, HERREN, har talet, og jeg fuldbyrder det.
37 “Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa har yanzu zan ji roƙon gidan Isra’ila in kuma yi musu wannan. Zan sa mutanensu su yi yawa kamar tumaki,
Så siger den Herre HERREN: Også dette vil jeg gøre for Israels Hus på deres Bøn: Jeg vil gøre dem mangfoldige som en Hjord af Mennesker;
38 yawansu ya yi kamar garken tumaki don hadaya a Urushalima a ƙayyadaddun lokuta bukukkuwarta. Haka biranen da suke kufai za su cika da ɗumbun mutane. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji.”
som en Hjord af Offerdyr, som Jerusalems Fårehjorde på dets Højtider skal de omstyrtede Byer blive fulde af Menneskehjorde; og de skal kende, at jeg er HERREN.

< Ezekiyel 36 >