< Ezekiyel 35 >

1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
And the word of the Lord was maad to me,
2 “Ɗan mutum, ka fuskanci Dutsen Seyir; ka yi annabci a kansa
and he seide, Thou, sone of man, sette thi face ayens the hil of Seir; and thou schalt profesie to it, and thou schalt seie to it,
3 ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gāba da kai, Dutsen Seyir, zan kuma miƙa hannuna gāba da kai in mai da kai kango.
The Lord God seith these thingis, Thou hil of Seir, lo! Y to thee; Y schal stretche forth myn hond on thee, and Y schal yyue thee desolat and forsakun.
4 Zan mai da garuruwanka kufai za ka kuma zama kango. Sa’an nan za ka san cewa ni ne Ubangiji.
Y schal distrie thi citees, and thou schalt be forsakun; and thou schalt wite, that Y am the Lord.
5 “‘Domin ka riƙe ƙiyayya ta tun dā, ka kuma ba da mutanen Isra’ila domin a kashe su da takobi a lokacin masifarsu, lokacin da adadin horonsu ya cika,
For thou were an enemye euerlastynge, and closidist togidere the sonis of Israel in to the hondis of swerd, in the tyme of her turment, in the tyme of the laste wickidnesse;
6 saboda haka muddin ina raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, zan sa a zub da jininka zan kuwa fafare ka. Da yake ba ka ƙi zub da jini ba, zub da jini zai fafare ka.
therfor Y lyue, seith the Lord God, for Y schal yyue thee to blood, and blood schal pursue thee; and sithen thou hatidist blood, blood schal pursue thee.
7 Zan mai da Dutsen Seyir kango in kuma yanke dukan waɗanda suke shiga da fita a cikinka.
And Y schal yyue the hil of Seir desolat and forsakun, and Y schal take awei fro it a goere and a comere ayen;
8 Zan cika duwatsunka da matattu; waɗanda aka kashe da takobi za su fāɗi a kan tuddanka, da cikin kwarurukanka, da cikin dukan kwazazzabanka.
and Y schal fille the hillis therof with the careyns of her slayn men. Men slayn by swerd schulen falle doun in thi litle hillis, and in thi valeys, and in thi strondis.
9 Zan mai da kai kango har abada; ba za a zauna a cikin garuruwanka ba. Sa’an nan za ka san cewa ni ne Ubangiji.
Y schal yyue thee in to euerlastynge wildirnessis, and thi citees schulen not be enhabitid; and ye schulen wite, that Y am the Lord God.
10 “‘Domin kun ce, “Waɗannan al’ummai biyu da ƙasashe za su zama namu za mu kuma mallake su,” ko da yake Ni Ubangiji ina a can,
For thou seidist, Twei folkis and twei londis schulen be myne, and Y schal welde tho bi eritage, whanne the Lord was there;
11 saboda haka muddin ina raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, zan sāka maka gwargwadon fushi da kuma kishin da ka nuna a ƙiyayyarsu da ka yi zan kuma sanar da kaina a cikinsu sa’ad da na hukunta ka.
therfor Y lyue, seith the Lord God, for Y schal do bi thi wraththe, and bi thin enuye, which thou didist, hatinge hem, and Y schal be made knowun bi hem, whanne Y schal deme thee;
12 Sa’an nan za ka san cewa Ni Ubangiji na ji duk abubuwan banzan da ka faɗa a kan duwatsun Isra’ila. Ka ce, “An mai da su kango an kuma ba mu su mu cinye.”
and thou schalt wite, that Y am the Lord. Y herde alle thi schenschipis, whiche thou spakist of the hillis of Israel, and seidist, The hillis of Israel ben forsakun, and ben youun to vs, for to deuoure.
13 Ka yi fariya a kaina, ka kuma yi magana a kaina ba gaggautawa, na ji shi sarai.
And ye han rise on me with youre mouth, and ye han deprauyd ayens me; Y herde youre wordis.
14 Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa yayinda dukan duniya take farin ciki, zan mai da kai kango.
The Lord God seith these thingis, While al the lond is glad, Y schal turne thee in to wildernesse.
15 Domin ka yi farin ciki sa’ad da gādon gidan Isra’ila ya zama kufai, haka zan yi da kai, ya Dutsen Seyir, kai da dukan Edom. Sa’an nan za ka san cewa ni ne Ubangiji.’”
As thou haddist ioie on the eritage of the hous of Israel, for it was distried, so Y schal do to thee; the hil of Seir schal be distried, and al Ydumee; and thei schulen wite, that Y am the Lord.

< Ezekiyel 35 >