< Ezekiyel 35 >

1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Yahweh gave me another message. He said,
2 “Ɗan mutum, ka fuskanci Dutsen Seyir; ka yi annabci a kansa
“You human, turn toward Edom and prophesy what will happen to its people. Say that this is what Yahweh says to them:
3 ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gāba da kai, Dutsen Seyir, zan kuma miƙa hannuna gāba da kai in mai da kai kango.
‘You who live near Seir Mountain [in Edom], I am opposed to you, and I will use my power [MTY] to strike you and cause your country to become a wasteland.
4 Zan mai da garuruwanka kufai za ka kuma zama kango. Sa’an nan za ka san cewa ni ne Ubangiji.
I will cause your country to be ruined and desolate. When that happens, people will know that I, Yahweh, [have the power to do what I say that I will do].
5 “‘Domin ka riƙe ƙiyayya ta tun dā, ka kuma ba da mutanen Isra’ila domin a kashe su da takobi a lokacin masifarsu, lokacin da adadin horonsu ya cika,
You have always been enemies of the Israeli people. You [rejoiced] when they experienced a great disaster: [their enemies attacked them with] swords, when I punished them [for the sins that they had committed].
6 saboda haka muddin ina raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, zan sa a zub da jininka zan kuwa fafare ka. Da yake ba ka ƙi zub da jini ba, zub da jini zai fafare ka.
Therefore, I, Yahweh the Lord, declare that as surely as I am alive, I will allow [your enemies] to slaughter [MTY] you and continue to slaughter you. You were happy when [LIT] others were slaughtered;
7 Zan mai da Dutsen Seyir kango in kuma yanke dukan waɗanda suke shiga da fita a cikinka.
so I will cause Seir Mountain to be abandoned/deserted, and I will get rid of anyone who enters it or leaves it.
8 Zan cika duwatsunka da matattu; waɗanda aka kashe da takobi za su fāɗi a kan tuddanka, da cikin kwarurukanka, da cikin dukan kwazazzabanka.
I will cause your mountains to be filled with [the corpses of] those who have been killed. The corpses of those who have been killed by [your enemies’] swords will lie on your hills and in your valleys and in all your ravines.
9 Zan mai da kai kango har abada; ba za a zauna a cikin garuruwanka ba. Sa’an nan za ka san cewa ni ne Ubangiji.
I will cause your land to be deserted forever. No one will live in your towns again. When that happens, you will know that I, Yahweh, [have the power to do what I say that I will do].
10 “‘Domin kun ce, “Waɗannan al’ummai biyu da ƙasashe za su zama namu za mu kuma mallake su,” ko da yake Ni Ubangiji ina a can,
You people said, “Israel and Judah will become ours. We will take over their territory!” You said that even though I, Yahweh, was still there [and protecting them].
11 saboda haka muddin ina raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, zan sāka maka gwargwadon fushi da kuma kishin da ka nuna a ƙiyayyarsu da ka yi zan kuma sanar da kaina a cikinsu sa’ad da na hukunta ka.
Therefore, I, Yahweh the Lord, declare that as surely as I am alive, I will punish [MTY] you for being angry with my people, envying them, and hating them.
12 Sa’an nan za ka san cewa Ni Ubangiji na ji duk abubuwan banzan da ka faɗa a kan duwatsun Isra’ila. Ka ce, “An mai da su kango an kuma ba mu su mu cinye.”
Then you will know that I, Yahweh, have heard all the disgusting things that you have said about the mountains in Israel. You said that they have been ruined/devastated, and that they have been given to you to occupy [MET].
13 Ka yi fariya a kaina, ka kuma yi magana a kaina ba gaggautawa, na ji shi sarai.
When you insulted me, I heard all that you said about me.
14 Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa yayinda dukan duniya take farin ciki, zan mai da kai kango.
So this is what I, Yahweh the Lord, say: You people who live on Seir Mountain and in all the other places in Edom, when I cause your land to become desolate, everyone in the entire world will rejoice.
15 Domin ka yi farin ciki sa’ad da gādon gidan Isra’ila ya zama kufai, haka zan yi da kai, ya Dutsen Seyir, kai da dukan Edom. Sa’an nan za ka san cewa ni ne Ubangiji.’”
You were happy when the land [MTY] of the Israeli people became desolate, so I will cause your land to become desolate. When that happens, people will know that I, Yahweh, [have the power to do what I say that I will do].’”

< Ezekiyel 35 >