< Ezekiyel 34 >

1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Et la parole du Seigneur me fut adressée, disant:
2 “Ɗan mutum, ka yi annabci a kan makiyayan Isra’ila; ka yi annabci ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa kaiton makiyayan Isra’ila waɗanda suke kula da kansu ne kawai! Ashe, bai kamata makiyaya ne su lura da tumaki ba?
Fils d’un homme, prophétise sur les pasteurs d’Israël: prophétise, et tu diras aux pasteurs: Voici ce que dit le Seigneur Dieu: Malheur aux pasteurs d’Israël qui se paissaient eux-mêmes; n’est-ce pas les troupeaux que les pasteurs font paître?
3 Kuna cin kitsensu, kuna yi wa kanku tufafi da gashinsu, kukan yanka turkakkun, amma ba ku yi kiwon tumakin ba.
Vous mangiez le lait, et vous vous couvriez des laines, et ce qui était gras, vous l’égorgiez: mais mon troupeau, vous ne le paissiez pas.
4 Ba ku ƙarfafa marasa ƙarfi ba, ko ku warkar da marasa lafiya ko ku ɗaura waɗanda suka ji rauni. Ba ku dawo da waɗanda suka yi makuwa ko ku nemi waɗanda suka ɓace ba. Amma sai kuka mallake su ƙarfi da yaji.
Ce qui était faible, vous ne l’avez pas fortifié; et ce qui était malade, vous ne l’avez pas guéri; et ce qui a été brisé, vous ne l’avez pas lié; et ce qui était égaré, vous ne l’avez pas ramené; et ce qui était perdu, vous ne l’avez pas cherché; mais vous leur commandiez avec rigueur et avec empire.
5 Saboda haka suka warwatse domin babu makiyayi, kuma da suka warwatsu sai suka zama abincin namun jeji.
Et mes brebis ont été dispersées, parce qu’il n’y avait point de pasteur; et elles sont devenues la pâture de toutes les bêtes des champs, et elles ont été dispersées.
6 Tumakina suna ta yawo a kan dukan duwatsu da kuma kowane tudu. Sun watsu a dukan duniya, kuma ba wanda ya neme su.
Mes troupeaux ont erré sur toutes les montagnes et sur toute colline élevée; et sur toute la face de la terre mes troupeaux ont été dispersés, et il n’y avait personne qui les recherchât, il n’y avait personne, dis-je, qui les recherchât.
7 “‘Saboda haka, ku makiyaya, ku ji maganar Ubangiji,
À cause de cela, pasteurs, écoutez la parole du Seigneur.
8 Muddin ina raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, domin tumaki sun rasa makiyayi ta haka aka washe su suka kuma zama abincin dukan namun jeji, kuma domin makiyayana ba su nemi tumakina ba amma suka kula da kansu a maimakon tumakina,
Je vis, moi, dit le Seigneur Dieu: parce que mes troupeaux sont devenus une proie, et mes brebis la pâture de toutes les bêtes des champs, parce qu’il n’y avait pas de pasteur, car mes pasteurs n’ont pas cherché mon troupeau; mais les pasteurs se paissaient eux-mêmes, et mes troupeaux, ils ne les paissaient pas;
9 saboda haka, ya ku makiyaya, ku ji maganar Ubangiji,
À cause de cela, pasteurs, écoutez la parole du Seigneur.
10 Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gāba da makiyaya kuma zan nemi hakkin tumakina daga gare su. Zan hana su yin kiwon tumakin don kada makiyayan su ƙara yin kiwon kansu. Zan ƙwace tumakina daga bakunansu, ba kuwa za su ƙara zama abincinsu.
Voici ce que dit le Seigneur Dieu: Voilà que je viens moi-même vers ces pasteurs; je redemanderai mon troupeau à leur main, et j’empêcherai qu’ils ne paissent à l’avenir un troupeau, et que ces pasteurs ne se paissent eux-mêmes; et j’arracherai mon troupeau à leur bouche, et il ne sera plus leur nourriture.
11 “‘Gama ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ni kaina zan nemi tumakina.
Parce que voici ce que dit le Seigneur Dieu: Voilà que moi-même je rechercherai mes brebis, et que je les visiterai.
12 Kamar yadda makiyayi yakan lura da tumakinsa da suka watse sa’ad da yake tare da su, haka zan lura da tumakina. Zan cece su daga dukan wuraren da aka watsar da su a ranar gizagizai da baƙin duhu.
Comme un berger visite son troupeau au jour où il est au milieu de ses brebis disséminées; ainsi je visiterai mes brebis; et je les délivrerai de tous les lieux où elles avaient été dispersées dans un jour de nuage et d’obscurité;
13 Zan dawo da su daga al’ummai in kuma tattara su daga ƙasashe, zan kuma kawo su cikin ƙasarsu. Zan yi kiwonsu a kan duwatsun Isra’ila, a maɓulɓulai da kuma cikin wuraren zamansu a ƙasar.
Et je les retirerai d’entre les peuples, et je les rassemblerai de divers pays, et je les amènerai dans leur propre terre, et je les ferai paître sur les montagnes d’Israël, le long des ruisseaux, et dans tous les lieux habités du pays.
14 Zan kula da su a wurin kiwo mai kyau, kuma ƙwanƙolin duwatsun Isra’ila ne zai zama wurin kiwonsu. Za su kwanta a wurin kiwo mai kyau, a can kuma za su yi kiwo a wurin kiwo mai kyau a kan duwatsun Isra’ila.
C’est dans les pâturages les plus abondants que je les ferai paître, et sur les hautes montagnes d’Israël que seront leurs pâturages: là, elles se reposeront sur des herbes verdoyantes, et elles paîtront dans des pâturages gras, sur les montagnes d’Israël.
15 Ni kaina zan lura da tumakina in kuma sa su kwanta, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
C’est moi qui paîtrai mes brebis, moi qui les ferai reposer, dit le Seigneur Dieu.
16 Zan nemi ɓatattuna in kuma dawo da waɗanda suka yi makuwa. Zan ɗaura raunin waɗanda suka ji ciwo in kuma ƙarfafa marasa ƙarfi, amma zan hallaka ƙarfafa da kuma masu ƙiba. Zan yi kiwo tumaki da adalci.
Ce qui était perdu, je le rechercherai; et ce qui était égaré, je le ramènerai; et ce qui était brisé, je le lierai; et ce qui était faible, je le fortifierai; et ce qui était fort et gras, je le conserverai, et je les ferai paître avec discernement.
17 “‘Game da ku, tumakina, ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan hukunta tsakanin tunkiya da tunkiya, da tsakanin raguna da awaki.
Mais vous, mes troupeaux, voici ce que dit le Seigneur Dieu: Voilà que moi je juge entre troupeau et troupeau de béliers et de boucs.
18 Bai isa ba a ce kun yi kiwo a wuri mai kyau? Sai kun tattake sauran wurin kiwonku da ƙafafunku tukuna? Bai isa ba a ce kun sha ruwa mai tsabta? Sai kun kuma gurɓata sauran da ƙafafunku?
N’était-ce pas assez pour vous de paître en de bons pâturages? mais vous avez de plus foulé aux pieds les restes de vos pâturages, et lorsque vous buviez une eau très pure, vous troubliez le reste avec vos pieds.
19 Dole ne tumakina su ci abin da kuka tattake su kuma sha abin da kuka gurɓata da ƙafafunku?
Et mes brebis paissaient ce qui avait été foulé par vos pieds, et ce que vos pieds avaient troublé, elles le buvaient.
20 “‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce musu, duba, ni kaina zan hukunta tsakanin turkakkun tumaki da ramammun tumaki.
À cause de cela, voici ce que dit le Seigneur Dieu: Voilà que moi-même je juge entre une brebis grasse et une maigre;
21 Domin kun tunkuɗe marasa ƙarfi da kafaɗunku, kun kuma tunkuye su da ƙahoninku sai da suka gudu,
Parce que vous heurtiez des côtés et de l’épaule, et que vous choquiez de vos cornes toutes les brebis faibles, jusqu’à ce qu’elles fussent dispersées dehors;
22 zan cece tumakina ba za su ƙara zama ganima ba. Zan hukunta tsakanin tunkiya da tunkiya.
Je sauverai mon troupeau, il ne sera plus en proie, et je jugerai entre brebis et brebis.
23 Zan sa musu makiyaya guda, bawana Dawuda, zai kuwa lura da su; zai kula da su ya kuma zama makiyayinsu.
Et JE SUSCITERAI SUR ELLES UN PASTEUR UNIQUE qui les paisse, mon serviteur David; lui-même me les paîtra, et il sera pour elles un pasteur.
24 Ni Ubangiji zan zama Allahnsu, bawana kuma Dawuda zai zama yerima a cikinsu. Ni Ubangiji na faɗa.
Mais moi, le Seigneur, je serai leur Dieu, et mon serviteur David sera prince au milieu d’eux; c’est moi, le Seigneur, qui ai parlé.
25 “‘Zan yi alkawarin salama da su in kuma kawar wa ƙasar da namun jeji domin su zauna a hamada su kuma kwana a kurmi lafiya lau.
Et je ferai avec eux une alliance de paix, et j’exterminerai de la terre les bêtes très mauvaises; et ceux qui habitent dans le désert dormiront avec sécurité dans les forêts.
26 Zan albarkace su in kuma sa tuduna kewaye da su. Zan zubo yayyafi a lokacinsa; za a kasance da yayyafin albarka.
Et je les rendrai autour de ma colline une bénédiction; et j’amènerai la pluie en son temps; ce seront des pluies de bénédiction.
27 Itatuwan gona za su ba da’ya’yansu, ƙasa kuma za tă ba da amfaninta; mutane za su zauna lafiya a ƙasarsu. Za su san cewa ni ne Ubangiji, sa’ad da na karya karkiyarsu, na cece su daga hannun waɗanda suka bautar da su.
Et l’arbre des champs donnera son fruit, et la terre donnera son germe; et ils seront dans leur terre sans crainte; et ils sauront que je suis le Seigneur, lorsque j’aurai brisé les chaînes de leur joug, et que je les aurai arrachés de la main de ceux qui les tenaient sous leur empire.
28 Ba za su ƙara zama ganimar al’ummai ba, ba kuwa namun jeji za su cinye su ba. Za su zauna lafiya, kuma babu wani da zai sa su ji tsoro.
Et ils ne seront plus en proie aux nations, et les bêtes de la terre ne les dévoreront pas; mais ils habiteront avec confiance sans aucune crainte.
29 Zan tanada musu ƙasar da aka sani don hatsinta, ba za su kuma ƙara zama abin da yunwa za tă fara musu a ƙasa ba ko su sha zargin sauran al’ummai.
Et je leur susciterai un germe renommé, ils ne seront plus détruits par la famine sur la terre, et ils ne porteront plus l’opprobre des nations.
30 Sa’an nan za su san cewa ni, Ubangiji Allahnsu, ina tare da su kuma cewa su, gidan Isra’ila, mutanena ne, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
Et ils sauront que moi le Seigneur leur Dieu, je suis avec eux, et qu’eux-mêmes sont mon peuple, la maison d’Israël, dit le Seigneur Dieu.
31 Ku tumakina, tumakin wurin kiwona, mutanena ne, ni kuwa Allahnku ne, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”
Mais vous, mes troupeaux, les troupeaux de mon pâturage, vous êtes des hommes, et moi je suis le Seigneur votre Dieu, dit le Seigneur Dieu.

< Ezekiyel 34 >