< Ezekiyel 34 >

1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
And the word of the Lord came vnto me, saying,
2 “Ɗan mutum, ka yi annabci a kan makiyayan Isra’ila; ka yi annabci ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa kaiton makiyayan Isra’ila waɗanda suke kula da kansu ne kawai! Ashe, bai kamata makiyaya ne su lura da tumaki ba?
Sonne of man, prophesie against the shepherdes of Israel, prophesie and say vnto them, Thus saieth the Lord God vnto the shepherds, Wo be vnto the shepherds of Israel, that feede them selues: should not the shepherds feede the flockes?
3 Kuna cin kitsensu, kuna yi wa kanku tufafi da gashinsu, kukan yanka turkakkun, amma ba ku yi kiwon tumakin ba.
Yee eate the fat, and yee clothe you with the wooll: yee kill them that are fed, but ye feede not the sheepe.
4 Ba ku ƙarfafa marasa ƙarfi ba, ko ku warkar da marasa lafiya ko ku ɗaura waɗanda suka ji rauni. Ba ku dawo da waɗanda suka yi makuwa ko ku nemi waɗanda suka ɓace ba. Amma sai kuka mallake su ƙarfi da yaji.
The weake haue ye not strengthened: the sicke haue ye not healed, neither haue ye bounde vp the broken, nor brought againe that which was driuen away, neither haue yee sought that which was lost, but with crueltie, and with rigour haue yee ruled them.
5 Saboda haka suka warwatse domin babu makiyayi, kuma da suka warwatsu sai suka zama abincin namun jeji.
And they were scattered without a shepherde: and when they were dispersed, they were deuoured of all the beastes of the fielde.
6 Tumakina suna ta yawo a kan dukan duwatsu da kuma kowane tudu. Sun watsu a dukan duniya, kuma ba wanda ya neme su.
My sheepe wandred through all the mountaines, and vpon euery hie hill: yea, my flocke was scattered through al the earth, and none did seeke or search after them.
7 “‘Saboda haka, ku makiyaya, ku ji maganar Ubangiji,
Therefore ye shepherds, heare the woorde of the Lord.
8 Muddin ina raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, domin tumaki sun rasa makiyayi ta haka aka washe su suka kuma zama abincin dukan namun jeji, kuma domin makiyayana ba su nemi tumakina ba amma suka kula da kansu a maimakon tumakina,
As I liue, sayeth the Lord God, surely because my flocke was spoyled, and my sheepe were deuoured of all the beasts of the fielde, hauing no shepherde, neither did my shepherdes seeke my sheepe, but the shepherdes fedde them selues, and fedde not my sheepe,
9 saboda haka, ya ku makiyaya, ku ji maganar Ubangiji,
Therefore, heare ye the word of the Lord, O ye shepherds.
10 Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gāba da makiyaya kuma zan nemi hakkin tumakina daga gare su. Zan hana su yin kiwon tumakin don kada makiyayan su ƙara yin kiwon kansu. Zan ƙwace tumakina daga bakunansu, ba kuwa za su ƙara zama abincinsu.
Thus saieth the Lord God, Behold, I come against the shepherds, and will require my sheepe at their hands, and cause them to cease from feeding the sheepe: neither shall the shepherds feede them selues any more: for I wil deliuer my sheepe from their mouthes, and they shall no more deuoure them.
11 “‘Gama ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ni kaina zan nemi tumakina.
For thus sayeth the Lord God, Beholde, I will search my sheepe, and seeke them out.
12 Kamar yadda makiyayi yakan lura da tumakinsa da suka watse sa’ad da yake tare da su, haka zan lura da tumakina. Zan cece su daga dukan wuraren da aka watsar da su a ranar gizagizai da baƙin duhu.
As a shepherd searcheth out his flocke, when he hath bene among his sheepe that are scattered, so wil I seeke out my sheepe and wil deliuer them out of all places, where they haue beene scattered in the cloudie and darke day,
13 Zan dawo da su daga al’ummai in kuma tattara su daga ƙasashe, zan kuma kawo su cikin ƙasarsu. Zan yi kiwonsu a kan duwatsun Isra’ila, a maɓulɓulai da kuma cikin wuraren zamansu a ƙasar.
And I will bring them out from the people, and gather them from the countreis, and will bring them to their owne lande, and feede them vpon the mountaines of Israel, by the riuers, and in all the inhabited places of the countrey.
14 Zan kula da su a wurin kiwo mai kyau, kuma ƙwanƙolin duwatsun Isra’ila ne zai zama wurin kiwonsu. Za su kwanta a wurin kiwo mai kyau, a can kuma za su yi kiwo a wurin kiwo mai kyau a kan duwatsun Isra’ila.
I will feede them in a good pasture, and vpon the hie mountaines of Israel shall their folde be: there shall they lie in a good folde and in fat pasture shall they feede vpon the mountaines of Israel.
15 Ni kaina zan lura da tumakina in kuma sa su kwanta, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
I will feede my sheepe, and bring them to their rest, sayth the Lord God.
16 Zan nemi ɓatattuna in kuma dawo da waɗanda suka yi makuwa. Zan ɗaura raunin waɗanda suka ji ciwo in kuma ƙarfafa marasa ƙarfi, amma zan hallaka ƙarfafa da kuma masu ƙiba. Zan yi kiwo tumaki da adalci.
I will seeke that which was lost, and bring againe that which was driue away, and will binde vp that which was broken, and will strengthen the weake but I wil destroy the fat and the strong, and I will feede them with iudgement.
17 “‘Game da ku, tumakina, ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan hukunta tsakanin tunkiya da tunkiya, da tsakanin raguna da awaki.
Also you my sheepe, Thus saieth the Lord God, behold, I iudge betweene sheepe, and sheepe, betweene the rammes and the goates.
18 Bai isa ba a ce kun yi kiwo a wuri mai kyau? Sai kun tattake sauran wurin kiwonku da ƙafafunku tukuna? Bai isa ba a ce kun sha ruwa mai tsabta? Sai kun kuma gurɓata sauran da ƙafafunku?
Seemeth it a small thing vnto you to haue eaten vp the good pasture, but yee must treade downe with your feete the residue of your pasture? and to haue drunke of the deepe waters, but yee must trouble the residue with your feete?
19 Dole ne tumakina su ci abin da kuka tattake su kuma sha abin da kuka gurɓata da ƙafafunku?
And my sheepe eate that which yee haue troden with your feete, and drinke that which ye haue troubled with your feete.
20 “‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce musu, duba, ni kaina zan hukunta tsakanin turkakkun tumaki da ramammun tumaki.
Therefore thus sayth the Lord God vnto them, behold, I, euen I wil iudge betweene the fat sheepe and the leane sheepe.
21 Domin kun tunkuɗe marasa ƙarfi da kafaɗunku, kun kuma tunkuye su da ƙahoninku sai da suka gudu,
Because ye haue thrust with side and with shoulder, and pusht al the weake with your hornes, till ye haue scattered them abroade,
22 zan cece tumakina ba za su ƙara zama ganima ba. Zan hukunta tsakanin tunkiya da tunkiya.
Therefore wil I helpe my sheepe, and they shall no more be spoyled, and I wil iudge betweene sheepe and sheepe.
23 Zan sa musu makiyaya guda, bawana Dawuda, zai kuwa lura da su; zai kula da su ya kuma zama makiyayinsu.
And I wil set vp a shepherd ouer them, and he shall feede them, euen my seruant Dauid, he shall feede them, and he shalbe their shepherd.
24 Ni Ubangiji zan zama Allahnsu, bawana kuma Dawuda zai zama yerima a cikinsu. Ni Ubangiji na faɗa.
And I the Lord will be their God, and my seruant Dauid shalbe the prince amog them. I the Lord haue spoken it.
25 “‘Zan yi alkawarin salama da su in kuma kawar wa ƙasar da namun jeji domin su zauna a hamada su kuma kwana a kurmi lafiya lau.
And I will make with them a couenant of peace, and will cause the euil beastes to cease out of the land: and they shall dwel safely in the wildernesse, and sleepe in the woods.
26 Zan albarkace su in kuma sa tuduna kewaye da su. Zan zubo yayyafi a lokacinsa; za a kasance da yayyafin albarka.
And I wil set them, as a blessing, euen roud about my mountaine: and I will cause rayne to come downe in due season, and there shalbe raine of blessing.
27 Itatuwan gona za su ba da’ya’yansu, ƙasa kuma za tă ba da amfaninta; mutane za su zauna lafiya a ƙasarsu. Za su san cewa ni ne Ubangiji, sa’ad da na karya karkiyarsu, na cece su daga hannun waɗanda suka bautar da su.
And the tree of the fielde shall yeeld her fruite, and the earth shall giue her fruite, and they shalbe safe in their land, and shall know that I am the Lord, when I haue broken the cordes of their yoke, and deliuered them out of the hands of those that serued themselues of them.
28 Ba za su ƙara zama ganimar al’ummai ba, ba kuwa namun jeji za su cinye su ba. Za su zauna lafiya, kuma babu wani da zai sa su ji tsoro.
And they shall no more be spoyled of the heathen, neither shall the beastes of the land deuoure them, but they shall dwell safely and none shall make them afrayd.
29 Zan tanada musu ƙasar da aka sani don hatsinta, ba za su kuma ƙara zama abin da yunwa za tă fara musu a ƙasa ba ko su sha zargin sauran al’ummai.
And I will rayse vp for them a plant of renoume, and they shalbe no more consumed with hunger in the land, neither beare the reproche of the heathen any more.
30 Sa’an nan za su san cewa ni, Ubangiji Allahnsu, ina tare da su kuma cewa su, gidan Isra’ila, mutanena ne, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
Thus shall they vnderstande, that I the Lord their God am with them, and that they, euen the house of Israel, are my people, sayth the Lord God.
31 Ku tumakina, tumakin wurin kiwona, mutanena ne, ni kuwa Allahnku ne, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”
And yee my sheepe, the sheepe of my pasture are men, and I am your God, saith the Lord God.

< Ezekiyel 34 >