< Ezekiyel 34 >
1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
And the word of the Lord came to me, saying:
2 “Ɗan mutum, ka yi annabci a kan makiyayan Isra’ila; ka yi annabci ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa kaiton makiyayan Isra’ila waɗanda suke kula da kansu ne kawai! Ashe, bai kamata makiyaya ne su lura da tumaki ba?
“Son of man, prophesy about the shepherds of Israel. Prophesy, and you shall say to the shepherds: Thus says the Lord God: Woe to the shepherds of Israel who feed themselves! Should not the flocks be fed by the shepherds?
3 Kuna cin kitsensu, kuna yi wa kanku tufafi da gashinsu, kukan yanka turkakkun, amma ba ku yi kiwon tumakin ba.
You consumed the milk, and you covered yourselves with the wool, and you killed what was fattened. But my flock you did not feed.
4 Ba ku ƙarfafa marasa ƙarfi ba, ko ku warkar da marasa lafiya ko ku ɗaura waɗanda suka ji rauni. Ba ku dawo da waɗanda suka yi makuwa ko ku nemi waɗanda suka ɓace ba. Amma sai kuka mallake su ƙarfi da yaji.
What was weak, you have not strengthened, and what was sick, you have not healed. What was broken, you have not bound, and what was cast aside, you have not led back again, and what was lost, you have not sought. Instead, you ruled over them with severity and with power.
5 Saboda haka suka warwatse domin babu makiyayi, kuma da suka warwatsu sai suka zama abincin namun jeji.
And my sheep were scattered, because there was no shepherd. And they became devoured by all the wild beasts of the field, and they were dispersed.
6 Tumakina suna ta yawo a kan dukan duwatsu da kuma kowane tudu. Sun watsu a dukan duniya, kuma ba wanda ya neme su.
My sheep have wandered to every mountain and to every exalted hill. And my flocks have been scattered across the face of the earth. And there was no one who sought them; there was no one, I say, who sought them.
7 “‘Saboda haka, ku makiyaya, ku ji maganar Ubangiji,
Because of this, O shepherds, listen to the word of the Lord:
8 Muddin ina raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, domin tumaki sun rasa makiyayi ta haka aka washe su suka kuma zama abincin dukan namun jeji, kuma domin makiyayana ba su nemi tumakina ba amma suka kula da kansu a maimakon tumakina,
As I live, says the Lord God, since my flocks have become a prey, and my sheep have been devoured by all the wild beasts of the field, since there was no shepherd, for my shepherds did not seek my flock, but instead the shepherds fed themselves, and they did not feed my flocks:
9 saboda haka, ya ku makiyaya, ku ji maganar Ubangiji,
because of this, O shepherds, listen to the word of the Lord:
10 Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gāba da makiyaya kuma zan nemi hakkin tumakina daga gare su. Zan hana su yin kiwon tumakin don kada makiyayan su ƙara yin kiwon kansu. Zan ƙwace tumakina daga bakunansu, ba kuwa za su ƙara zama abincinsu.
Thus says the Lord God: Behold, I myself will be over the shepherds. I will require my flock at their hand, and I will cause them to cease, so that they no longer refrain from feeding the flock. Neither will the shepherds feed themselves any more. And I will deliver my flock from their mouth; and it will no longer be food for them.
11 “‘Gama ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ni kaina zan nemi tumakina.
For thus says the Lord God: Behold, I myself will seek my sheep, and I myself will visit them.
12 Kamar yadda makiyayi yakan lura da tumakinsa da suka watse sa’ad da yake tare da su, haka zan lura da tumakina. Zan cece su daga dukan wuraren da aka watsar da su a ranar gizagizai da baƙin duhu.
Just as a shepherd visits his flock, in the day when he will be in the midst of his sheep that were scattered, so will I visit my sheep. And I will deliver them from all the places to which they had been scattered in the day of gloom and darkness.
13 Zan dawo da su daga al’ummai in kuma tattara su daga ƙasashe, zan kuma kawo su cikin ƙasarsu. Zan yi kiwonsu a kan duwatsun Isra’ila, a maɓulɓulai da kuma cikin wuraren zamansu a ƙasar.
And I will lead them away from the peoples, and I will gather them from the lands, and I will bring them into their own land. And I will pasture them on the mountains of Israel, by the rivers, and in all the settlements of the land.
14 Zan kula da su a wurin kiwo mai kyau, kuma ƙwanƙolin duwatsun Isra’ila ne zai zama wurin kiwonsu. Za su kwanta a wurin kiwo mai kyau, a can kuma za su yi kiwo a wurin kiwo mai kyau a kan duwatsun Isra’ila.
I will feed them in very fertile pastures, and their pastures will be on the lofty mountains of Israel. There they will rest on the green grass, and they will be fed in the fat pastures, on the mountains of Israel.
15 Ni kaina zan lura da tumakina in kuma sa su kwanta, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
I will feed my sheep, and I will cause them to lie down, says the Lord God.
16 Zan nemi ɓatattuna in kuma dawo da waɗanda suka yi makuwa. Zan ɗaura raunin waɗanda suka ji ciwo in kuma ƙarfafa marasa ƙarfi, amma zan hallaka ƙarfafa da kuma masu ƙiba. Zan yi kiwo tumaki da adalci.
I will seek what had been lost. And I will lead back again what had been cast aside. And I will bind up what had been broken. And I will strengthen what had been infirm. And I will preserve what was fat and strong. And I will feed them on judgment.
17 “‘Game da ku, tumakina, ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan hukunta tsakanin tunkiya da tunkiya, da tsakanin raguna da awaki.
But as for you, O my flocks, thus says the Lord God: Behold, I judge between cattle and cattle, among rams and among he-goats.
18 Bai isa ba a ce kun yi kiwo a wuri mai kyau? Sai kun tattake sauran wurin kiwonku da ƙafafunku tukuna? Bai isa ba a ce kun sha ruwa mai tsabta? Sai kun kuma gurɓata sauran da ƙafafunku?
Was it not enough for you to feed upon good pastures? For you even trample with your feet upon the remainder of your pastures. And when you drank the purist water, you disturbed the remainder with your feet.
19 Dole ne tumakina su ci abin da kuka tattake su kuma sha abin da kuka gurɓata da ƙafafunku?
And my sheep were pastured from what you had trampled with your feet, and they drank from what your feet had disturbed.
20 “‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce musu, duba, ni kaina zan hukunta tsakanin turkakkun tumaki da ramammun tumaki.
Because of this, thus says the Lord God to you: Behold, I myself am judging between the fat cattle and the lean.
21 Domin kun tunkuɗe marasa ƙarfi da kafaɗunku, kun kuma tunkuye su da ƙahoninku sai da suka gudu,
For you have pushed with your sides and shoulders, and you have threatened all the weak cattle with your horns, until they were scattered abroad.
22 zan cece tumakina ba za su ƙara zama ganima ba. Zan hukunta tsakanin tunkiya da tunkiya.
I will save my flock, and it will no longer be a prey, and I will judge between cattle and cattle.
23 Zan sa musu makiyaya guda, bawana Dawuda, zai kuwa lura da su; zai kula da su ya kuma zama makiyayinsu.
And I will raise up over them ONE SHEPHERD, who will feed them, my servant David. He himself will feed them, and he will be their shepherd.
24 Ni Ubangiji zan zama Allahnsu, bawana kuma Dawuda zai zama yerima a cikinsu. Ni Ubangiji na faɗa.
And I, the Lord, will be their God. And my servant David will be the leader in their midst. I, the Lord, have spoken.
25 “‘Zan yi alkawarin salama da su in kuma kawar wa ƙasar da namun jeji domin su zauna a hamada su kuma kwana a kurmi lafiya lau.
And I will make a covenant of peace with them. And I will cause the very harmful beasts to cease from the land. And those who are living in the desert will sleep securely in the forests.
26 Zan albarkace su in kuma sa tuduna kewaye da su. Zan zubo yayyafi a lokacinsa; za a kasance da yayyafin albarka.
And I will make them a blessing all around my hill. And I will send the rain in due time; there will be showers of blessing.
27 Itatuwan gona za su ba da’ya’yansu, ƙasa kuma za tă ba da amfaninta; mutane za su zauna lafiya a ƙasarsu. Za su san cewa ni ne Ubangiji, sa’ad da na karya karkiyarsu, na cece su daga hannun waɗanda suka bautar da su.
And the tree of the field will yield its fruit, and the land will yield its crop. And they will be in their own land without fear. And they shall know that I am the Lord, when I will have crushed the chains of their yoke, and when I will have rescued them from the hand of those who rule over them.
28 Ba za su ƙara zama ganimar al’ummai ba, ba kuwa namun jeji za su cinye su ba. Za su zauna lafiya, kuma babu wani da zai sa su ji tsoro.
And they will no longer be a prey to the Gentiles, nor will the wild beasts of the earth devour them. Instead, they will live in confidence without any terror.
29 Zan tanada musu ƙasar da aka sani don hatsinta, ba za su kuma ƙara zama abin da yunwa za tă fara musu a ƙasa ba ko su sha zargin sauran al’ummai.
And I will raise up for them a renowned branch. And they will be no longer be diminished by famine in the land, nor will they carry any longer the reproach of the Gentiles.
30 Sa’an nan za su san cewa ni, Ubangiji Allahnsu, ina tare da su kuma cewa su, gidan Isra’ila, mutanena ne, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
And they shall know that I, the Lord their God, am with them, and that they are my people, the house of Israel, says the Lord God.
31 Ku tumakina, tumakin wurin kiwona, mutanena ne, ni kuwa Allahnku ne, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”
For you are my flocks; the flocks of my pasture are men. And I am the Lord your God, says the Lord God.”