< Ezekiyel 34 >
1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
HERRENs Ord kom til mig således:
2 “Ɗan mutum, ka yi annabci a kan makiyayan Isra’ila; ka yi annabci ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa kaiton makiyayan Isra’ila waɗanda suke kula da kansu ne kawai! Ashe, bai kamata makiyaya ne su lura da tumaki ba?
Menneskesøn, profeter mod Israels Hyrder, profeter og sig til dem: Så siger den Herre HERREN: Ve Israels Hyrder, som røgtede sig selv! Skal Hyrderne ikke røgte Hjorden?
3 Kuna cin kitsensu, kuna yi wa kanku tufafi da gashinsu, kukan yanka turkakkun, amma ba ku yi kiwon tumakin ba.
I fortærede Mælken, med Ulden klædte I eder, de fede Dyr slagtede I, men Hjorden røgtede I ikke;
4 Ba ku ƙarfafa marasa ƙarfi ba, ko ku warkar da marasa lafiya ko ku ɗaura waɗanda suka ji rauni. Ba ku dawo da waɗanda suka yi makuwa ko ku nemi waɗanda suka ɓace ba. Amma sai kuka mallake su ƙarfi da yaji.
de svage Dyr styrkede I ikke, de syge lægte I ikke, de sårede forbandt I ikke, de adsplittede bragte I ikke tilbage, de vildfarende opsøgte I ikke, men I styrede dem med Hårdhed og Grumhed.
5 Saboda haka suka warwatse domin babu makiyayi, kuma da suka warwatsu sai suka zama abincin namun jeji.
Derfor spredtes de, eftersom der ingen Hyrde var, og blev til Æde for alle Markens vilde Dyr; ja, de spredtes.
6 Tumakina suna ta yawo a kan dukan duwatsu da kuma kowane tudu. Sun watsu a dukan duniya, kuma ba wanda ya neme su.
Min Hjord flakkede om på alle Bjerge og på hver en høj Banke, og over hele Jorden spredtes min Hjord, og ingen spurgte eller ledte efter dem.
7 “‘Saboda haka, ku makiyaya, ku ji maganar Ubangiji,
Derfor, I Hyrder, hør HERRENs Ord!
8 Muddin ina raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, domin tumaki sun rasa makiyayi ta haka aka washe su suka kuma zama abincin dukan namun jeji, kuma domin makiyayana ba su nemi tumakina ba amma suka kula da kansu a maimakon tumakina,
Så sandtjeg lever, lyder det fra den Herre HERREN: Fordi min Hjord blev til Rov, fordi min Hjord blev til Æde for alle Markens vilde Dyr, eftersom der ingen Hyrde var, og Hyrderne ikke spurgte efter min Hjord, og fordi Hyrderne røgtede sig selv og ikke min Hjord,
9 saboda haka, ya ku makiyaya, ku ji maganar Ubangiji,
derfor, I Hyrder, hør HERRENs Ord!
10 Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gāba da makiyaya kuma zan nemi hakkin tumakina daga gare su. Zan hana su yin kiwon tumakin don kada makiyayan su ƙara yin kiwon kansu. Zan ƙwace tumakina daga bakunansu, ba kuwa za su ƙara zama abincinsu.
Så siger den Herre HERREN: Se, jeg, kommer over Hyrderne og kræver min Hjord af deres Hånd, og jeg sætter dem fra at vogte min Hjord; Hyrderne skal ikke mere kunne røgte sig selv; jeg redder min Hjord af deres Gab, så den ikke skal tjene dem til Æde.
11 “‘Gama ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ni kaina zan nemi tumakina.
Thi så siger den Herre HERREN: Se, jeg vil selv spørge efter min Hjord og tage mig af den.
12 Kamar yadda makiyayi yakan lura da tumakinsa da suka watse sa’ad da yake tare da su, haka zan lura da tumakina. Zan cece su daga dukan wuraren da aka watsar da su a ranar gizagizai da baƙin duhu.
Som en Hyrde tager sig af sin Hjord på Stormvejrets Dag, således tager jeg mig af min Hjord og redder den fra de Steder, hvorhen de spredtes på Skyernes og Mulmets Dag;
13 Zan dawo da su daga al’ummai in kuma tattara su daga ƙasashe, zan kuma kawo su cikin ƙasarsu. Zan yi kiwonsu a kan duwatsun Isra’ila, a maɓulɓulai da kuma cikin wuraren zamansu a ƙasar.
jeg fører dem bort fra Folkeslagene, samler dem fra Landene og bringer dem til deres Land, og jeg, røgter dem på Israels Bjerge, i Kløfterne og på alle Landets beboede Steder.
14 Zan kula da su a wurin kiwo mai kyau, kuma ƙwanƙolin duwatsun Isra’ila ne zai zama wurin kiwonsu. Za su kwanta a wurin kiwo mai kyau, a can kuma za su yi kiwo a wurin kiwo mai kyau a kan duwatsun Isra’ila.
På gode Græsgange vil jeg vogte dem, og på Israels Bjerghøjder skal deres Græsmarker være; der skal de lejre sig på gode Græsmarker, og i fede Græsgange skal de græsse på Israels Bjerge.
15 Ni kaina zan lura da tumakina in kuma sa su kwanta, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
Jeg vil selv røgte min Hjord og selv lade dem lejre sig, lyder det fra den Herre HERREN.
16 Zan nemi ɓatattuna in kuma dawo da waɗanda suka yi makuwa. Zan ɗaura raunin waɗanda suka ji ciwo in kuma ƙarfafa marasa ƙarfi, amma zan hallaka ƙarfafa da kuma masu ƙiba. Zan yi kiwo tumaki da adalci.
De vildfarende Dyr vil jeg opsøge, de adsplittede vil jeg bringe tilbage, de sårede vil jeg forbinde de svage vil jeg styrke, og de fede og kraftige vil jeg vogte; jeg vil røgte dem, som det er ret.
17 “‘Game da ku, tumakina, ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan hukunta tsakanin tunkiya da tunkiya, da tsakanin raguna da awaki.
Og I, min Hjord! Så siger den Herre HERREN: Se, jeg vil skifte. Ret mellem Får og Får, mellem Vædre og Bukke.
18 Bai isa ba a ce kun yi kiwo a wuri mai kyau? Sai kun tattake sauran wurin kiwonku da ƙafafunku tukuna? Bai isa ba a ce kun sha ruwa mai tsabta? Sai kun kuma gurɓata sauran da ƙafafunku?
Er det eder ikke nok at græsse på den bedste Græsgang, siden I nedtramper, hvad der er levnet af eders Græsgange? Er det eder ikke nok at drikke det klare Vand, siden I med eders Fødder plumrer, hvad der er levnet?
19 Dole ne tumakina su ci abin da kuka tattake su kuma sha abin da kuka gurɓata da ƙafafunku?
Min Hjord må græsse, hvad I har nedtrampet, og drikke, hvad I har plumret med eders Fødder!
20 “‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce musu, duba, ni kaina zan hukunta tsakanin turkakkun tumaki da ramammun tumaki.
Derfor, så siger den Herre HERREN: Se, jeg kommer for at skifte Ret mellem de fede og de magre Får.
21 Domin kun tunkuɗe marasa ƙarfi da kafaɗunku, kun kuma tunkuye su da ƙahoninku sai da suka gudu,
Fordi I med Side og Skulder skubbede alle de svage Dyr bort og stangede dem med eders Horn, til I fik dem drevet ud,
22 zan cece tumakina ba za su ƙara zama ganima ba. Zan hukunta tsakanin tunkiya da tunkiya.
derfor vil jeg hjælpe min Hjord, så den ikke mere skal blive til Rov, og skifte Ret mellem Får og Får.
23 Zan sa musu makiyaya guda, bawana Dawuda, zai kuwa lura da su; zai kula da su ya kuma zama makiyayinsu.
Jeg sætter een Hyrde over dem, min Tjener David, og han skal vogte dem; han skal vogte dem, og han skal være deres Hyrde.
24 Ni Ubangiji zan zama Allahnsu, bawana kuma Dawuda zai zama yerima a cikinsu. Ni Ubangiji na faɗa.
Og jeg, HERREN, vil være deres Gud, og min Tjener David skal være Fyrste iblandt dem, så sandt jeg, HERREN, har talet.
25 “‘Zan yi alkawarin salama da su in kuma kawar wa ƙasar da namun jeji domin su zauna a hamada su kuma kwana a kurmi lafiya lau.
Jeg vil slutte en Fredspagt med dem og udrydde de vilde Dyr at Landet, så de trygt kan bo i Ørkenen og sove i Skovene.
26 Zan albarkace su in kuma sa tuduna kewaye da su. Zan zubo yayyafi a lokacinsa; za a kasance da yayyafin albarka.
Og jeg gør dem og Landet rundt om min Høj til Velsignelse, og jeg sender Regn i rette Tid, mine Byger skal blive til Velsignelse.
27 Itatuwan gona za su ba da’ya’yansu, ƙasa kuma za tă ba da amfaninta; mutane za su zauna lafiya a ƙasarsu. Za su san cewa ni ne Ubangiji, sa’ad da na karya karkiyarsu, na cece su daga hannun waɗanda suka bautar da su.
Markens Træer skal give deres Frugt og Landet sin Afgrøde; trygt skal de bo på deres Jord, og de skal kende, at jeg er HERREN, når jeg bryder Stængerne på deres Åg og frelser dem af deres Hånd, som gjorde dem til Trælle.
28 Ba za su ƙara zama ganimar al’ummai ba, ba kuwa namun jeji za su cinye su ba. Za su zauna lafiya, kuma babu wani da zai sa su ji tsoro.
Ikke mere skal de blive til Rov for Folkene, og Landets vilde Dyr skal ikke æde dem; trygt skal de bo, uden at nogen skræmmer dem.
29 Zan tanada musu ƙasar da aka sani don hatsinta, ba za su kuma ƙara zama abin da yunwa za tă fara musu a ƙasa ba ko su sha zargin sauran al’ummai.
Jeg lader en Fredens Plantning vokse op for dem, og ingen skal rives bort af Hunger i Landet, og de skal ikke mere bære Folkenes Hån.
30 Sa’an nan za su san cewa ni, Ubangiji Allahnsu, ina tare da su kuma cewa su, gidan Isra’ila, mutanena ne, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
De skal kende, at jeg, HERREN deres Gud, er med dem, og at de er mit Folk, Israels Hus, lyder det fra den Herre HERREN
31 Ku tumakina, tumakin wurin kiwona, mutanena ne, ni kuwa Allahnku ne, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”
I er min Hjord, I er den Hjord, jeg røgter, og jeg er eders Gud, lyder det fra den Herre HERREN.