< Ezekiyel 33 >

1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Ilizwi leNkosi lafika kimi futhi, lisithi:
2 “Ɗan mutum, yi magana da mutanen ƙasarka ka faɗa musu cewa, ‘Sa’ad da na kawo takobi a kan ƙasar, mutanen ƙasar kuwa suka zaɓi ɗaya daga cikin mutanensu suka mai da shi mai tsaro,
Ndodana yomuntu, khuluma kubantwana babantu bakho, uthi kubo: Ilizwe, lapho ngiletha inkemba phezu kwalo, labantu belizwe bathathe umuntu emingceleni yakibo, bambeke abe ngumlindi wabo,
3 ya kuma ga takobi yana zuwa a kan ƙasar ya kuwa busa ƙaho don yă faɗakar da mutane,
lapho ebona inkemba isiza phezu kwelizwe, avuthele uphondo, axwayise abantu,
4 in wani ya ji busar amma bai kula ba, takobin zai zo ya ɗauki ransa, jininsa kuwa zai zauna a kansa.
kuzakuthi loba ngubani ozwa umsindo wophondo, kodwa angaxwayi, lapho inkemba ifika, imsuse, igazi lakhe lizakuba phezu kwekhanda lakhe.
5 Da yake ya ji ƙarar busar amma bai kula ba, jininsa zai zauna a kansa. Da a ce ya kula, da ya ceci kansa.
Uzwile ukukhala kophondo, kodwa angaxwayi; igazi lakhe lizakuba phezu kwakhe. Kodwa oxwayayo uzawophula umphefumulo wakhe.
6 Amma a ce mai tsaron ya ga takobi yana zuwa bai kuwa busa ƙaho don yă faɗakar da mutane ba sai takobi ya zo ya ɗauki ran waninsu, za a kawar da wannan mutum saboda zunubinsa, amma zan nemi hakkin jinin mutumin a kan mai tsaron.’
Kodwa nxa umlindi ebona inkemba isiza, angavutheli uphondo, abantu bengaxwayiswa, aluba inkemba ifika, isuse umuntu phakathi kwabo, yena ususwa esesonweni sakhe, kodwa igazi lakhe ngizalibiza esandleni somlindi.
7 “Ɗan mutum, na mai da kai mai tsaro bisa gidan Isra’ila; saboda haka ka ji abin da zan faɗa ka kuma gargaɗe su.
Wena-ke, ndodana yomuntu, ngikubeke waba ngumlindi endlini kaIsrayeli; ngakho uzakuzwa ilizwi elivela emlonyeni wami, ubaxwayise ngokuvela kimi.
8 Sa’ad da na ce wa mugu, ‘Ya mugun mutum, tabbatacce za ka mutu,’ kai kuma ba ka yi magana don ka juyar da shi daga hanyoyinsa ba, wannan mugun mutum zai mutu domin zunubinsa, zan kuma nemi hakkin jininsa a kanka.
Uba ngisithi komubi: Mubi, uzakufa lokufa; uba wena ungakhulumi ukuxwayisa omubi atshiye indlela yakhe, lowo omubi uzafela esonweni sakhe, kodwa igazi lakhe ngizalibiza esandleni sakho.
9 Amma in ka faɗakar da mugun mutumin don yă juye daga hanyoyinsa bai kuwa yi haka ba, zai mutu saboda zunubinsa, amma kai za ka kuɓutar da kanka.
Kodwa wena uba umxwayisa omubi ngendlela yakhe ukuthi aphenduke kuyo; uba engaphenduki endleleni yakhe, yena uzafela ebubini bakhe, kodwa wena usuwophule umphefumulo wakho.
10 “Ɗan mutum, faɗa wa gidan Isra’ila, ‘Ga abin da kuke cewa, “Laifofinmu da zunubanmu suna nawaita mana, muna kuma lalacewa saboda su. Ta ƙaƙa za mu rayu?”’
Ngakho, wena ndodana yomuntu, tshono kuyo indlu kaIsrayeli: Likhuluma ngokunjalo lisithi: Ngoba iziphambeko zethu lezono zethu ziphezu kwethu, thina sicikizeke sikuzo, pho, sizaphila njani?
11 Ka faɗa musu, ‘Muddin ina raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, ba na jin daɗin mutuwar mugu, amma a maimako haka ya fi su juye daga hanyoyinsu su rayu. Ku juye! Ku juye daga mugayen hanyoyinku! Don me za ku mutu, ya gidan Isra’ila?’
Tshono kubo: Kuphila kwami, itsho iNkosi uJehova, isibili kangithokozi ngokufa komubi, kodwa ngokuthi omubi aphenduke endleleni yakhe aphile. Phendukani, phendukani ezindleleni zenu ezimbi; ngoba lizafelani, lina ndlu kaIsrayeli?
12 “Saboda haka, ɗan mutum, ka faɗa wa mutanen ƙasarka, ‘Adalcin adali ba zai cece shi sa’ad da ya ƙi yin biyayya ba, kuma muguntar mugu ba za tă sa ya fāɗi sa’ad da ya juya daga gare ta ba. Adali, in ya yi zunubi, ba za a bari yă rayu saboda adalcinsa na dā ba.’
Wena-ke, ndodana yomuntu, tshono ebantwaneni babantu bakiniuthi: Ukulunga kolungileyo kakuyikumophula ngosuku lwesiphambeko sakhe; mayelana lenkohlakalo yokhohlakeleyo, kayikuwa ngayo ngosuku azaphenduka ngalo enkohlakalweni yakhe; lolungileyo kayikuba lakho ukuphila ngokulunga kwakhe ngosuku ona ngalo.
13 In na faɗa wa adali cewa tabbatacce zai rayu, amma sai ya dogara ga adalcinsa ya kuma aikata mugunta, babu ayyukan adalcinsa da za a tuna; zai mutu saboda muguntar da ya aikata.
Lapho ngizakutsho kolungileyo ukuthi uzaphila isibili; uba yena ethembela ekulungeni kwakhe, enze isiphambeko, konke ukulunga kwakhe kakuyikukhunjulwa; kodwa ngenxa yobubi bakhe abenzileyo, uzabufela.
14 Kuma in na ce wa mugu, ‘Tabbatacce za ka mutu,’ amma sai ya juye daga zunubinsa ya kuma yi abin da yake gaskiya da kuma daidai,
Futhi uba ngisitsho kokhohlakeleyo ukuthi: Uzakufa lokufa; uba ephenduka esonweni sakhe, enze isahlulelo lokulungileyo,
15 in ya mayar da jingina, ya mayar da abin da ya sata, ya kiyaye ƙa’idodin da suke ba da rai, ya daina yin mugunta, tabbatacce zai rayu; ba zai mutu ba.
okhohlakeleyo ebuyisela isibambiso, abhadale impango, ahambe ngezimiso zempilo, ukuthi angenzi isiphambeko, uzaphila isibili, kayikufa.
16 Babu wani zunubin da ya aikata da za a tuna da shi. Ya yi abin da yake gaskiya da kuma daidai; tabbatacce zai rayu.
Kakukho lasinye sezono zakhe azenzileyo esizakhunjulwa kuye; wenzile isahlulelo lokulungileyo; uzaphila isibili.
17 “Duk da haka mutanen ƙasarka sun ce, ‘Hanyar Ubangiji ba daidai ba ce.’ Alhali kuwa tasu ce ba daidai ba.
Kodwa abantwana babantu bakini bathi: Indlela yeNkosi kayilingani; kanti ngeyabo indlela engalinganiyo.
18 In adali ya juye daga adalcinsa ya yi mugunta, zai mutu saboda haka.
Nxa olungileyo ephenduka ekulungeni kwakhe, enze isiphambeko, uzakufa ngenxa yaso.
19 Kuma in mugu ya juye daga muguntarsa ya aikata abin da yake gaskiya da kuma daidai, zai rayu ta yin haka.
Kodwa uba okhohlakeleyo ephenduka kunkohlakalo yakhe, enze isahlulelo lokulungileyo, yena uzaphila ngakho.
20 Duk da haka, ya gidan Isra’ila kun ce, ‘Hanyar Ubangiji ba daidai ba ce.’ Amma zan hukunta kowane ɗayanku gwargwadon ayyukansa.”
Kanti lithi: Indlela yeNkosi kayilingani. Wena ndlu kaIsrayeli, ngizalahlulela, ngulowo lalowo njengendlela zakhe.
21 A shekara ta goma sha biyu ta zaman bautanmu, a wata na goma a rana ta biyar, wani mutumin da ya gudu daga Urushalima ya zo wurina ya ce, “Birnin ya fāɗi!”
Kwasekusithi ngomnyaka wetshumi lambili wokuthunjwa kwethu, ngenyanga yetshumi, ngolwesihlanu lwenyanga, owayephunyukile eJerusalema wafika kimi esithi: Umuzi usutshayiwe.
22 To a yamman da ya wuce kafin mutumin ya iso, hannun Ubangiji yana a kaina, ya kuma buɗe bakina kafin mutumin ya iso wurina da safe. Sai bakina ya buɗu ban kuma yi shiru ba.
Kwathi isandla seNkosi saba phezu kwami kusihlwa, ophunyukileyo engakafiki, savula umlomo wami, waze wafika kimi ekuseni. Ngokunjalo umlomo wami wavuleka, kangabe ngisaba yisimungulu.
23 Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Ilizwi leNkosi laselifika kimi, lisithi:
24 “Ɗan mutum, mutanen da suke zama a waɗannan kufai a ƙasar Isra’ila suna cewa, ‘Ibrahim mutum ɗaya ne kaɗai, duk da haka Ibrahim ya mallaki ƙasar. Amma mu da muke da yawa; lalle an ba mu ƙasar ta zama mallakarmu.’
Ndodana yomuntu, abahlali balawomanxiwa elizwe lakoIsrayeli bakhuluma besithi: UAbrahama wayemunye, wadla ilifa lelizwe; kodwa thina sibanengi; ilizwe silinikiwe ukuba yilifa.
25 Saboda haka ka faɗa musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa da yake kun ci nama da jini a cikinsa kuka kuma bauta wa gumakanku kuka zub da jini, kuna gani za ku mallaki ƙasar?
Ngakho tshono kubo: Itsho njalo iNkosi uJehova: Lidla okulegazi, liphakamisele amehlo enu ezithombeni zenu, lichithe igazi; kambe lizakudla ilifa lelizwe yini?
26 Kun dogara ga takobinku, kuka aikata abubuwan banƙyama, kowannenku kuma ya ƙazantar da matar maƙwabcinsa. Kuna gani za ku mallaki ƙasar?’
Lima phezu kwenkemba yenu, lenze isinengiso, lingcolise, ngulowo lalowo umfazi kamakhelwane wakhe; kambe lizakudla ilifa lelizwe yini?
27 “Ka faɗa musu wannan, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa muddin ina raye, waɗanda aka rage a kufai za su fāɗi ga takobi, waɗanda suke bayan gari kuwa namun jeji za su cinye su, waɗanda suke a mafaka da kogwannin duwatsu annoba za tă kashe su.
Tshono njalo kubo: Itsho njalo iNkosi uJehova: Kuphila kwami, isibili labo abasemanxiweni bazakuwa ngenkemba; lalowo osegcekeni ngizamnikela ezilweni ukuthi zimudle, lalabo abasezinqabeni labasezimbalwini bazakufa ngomatshayabhuqe wesifo.
28 Zan mai da ƙasar kango, kuma fariyar ƙarfinta zai ƙare, duwatsun Isra’ila za su zama kufai don kada wani ya ratsa su.
Ngoba ngizalenza ilizwe libe lunxiwa lencithakalo, lokuziqhenya kwamandla alo kuzaphela, lezintaba zakoIsrayeli zibe yinkangala, ukuze kungabi khona odlulayo.
29 Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji, sa’ad da na mai da ƙasar kango saboda dukan abubuwan banƙyamar da suka yi.’
Khona bazakwazi ukuthi ngiyiNkosi, lapho sengenze ilizwe laba yinkangala lesesabiso ngenxa yawo wonke amanyala abo abawenzileyo.
30 “Game da kai kuma, ɗan mutum, mutanen ƙasarka suna magana da juna game da kai a katanga da kuma ƙofofin gidaje, suna ce wa juna, ‘Ku zo mu tafi mu ji maganar da ta zo daga wurin Ubangiji.’
Wena-ke, ndodana yomuntu, abantwana babantu bakini basakhuluma ngawe ngasemidulwini laseminyango yezindlu, njalo omunye ekhuluma komunye, ngulowo lalowo kumfowabo, besithi: Wozani, ngiyacela, lizwe ukuthi yilizwi bani eliphuma eNkosini.
31 Mutanena sukan zo wurinka, yadda suka saba su zauna a gabanka don su saurari maganarka, amma ba sa aiki da abin da suka ji. Da bakunansu suna nuna ƙauna, amma zukatansu cike da haɗama suke don ƙazamar riba.
Njalo bayeza kuwe njengokuza kwabantu, bahlale phambi kwakho njengabantu bami, bezwe amazwi akho, kodwa bangawenzi; ngoba ngomlomo wabo babonakalisa uthando olukhulu, kodwa inhliziyo yabo ilandela inzuzo yabo embi.
32 Tabbatacce, gare su ba ka fi mai waƙar ƙauna da murya mai daɗi kana kuma yin kiɗa sosai ba, gama sukan ji maganarka amma ba sa amfani da ita.
Khangela-ke, kubo unjengengoma ethandekayo, ilizwi elimnandi, lowazi kuhle ukutshaya ichacho; ngoba besizwa amazwi akho kodwa bengawenzi.
33 “Sa’ad da dukan wannan ya cika kuma zai cika ɗin, sa’an nan za su sani akwai annabi a tsakiyarsu.”
Kodwa ekufikeni kwalokhu (khangela, kuzafika), khona bazakwazi ukuthi bekukhona umprofethi phakathi kwabo.

< Ezekiyel 33 >