< Ezekiyel 33 >

1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Et la parole de l'Éternel me fut adressée en ces mots:
2 “Ɗan mutum, yi magana da mutanen ƙasarka ka faɗa musu cewa, ‘Sa’ad da na kawo takobi a kan ƙasar, mutanen ƙasar kuwa suka zaɓi ɗaya daga cikin mutanensu suka mai da shi mai tsaro,
Fils de l'homme, parle aux enfants de ton peuple et dis-leur: Si je faisais venir l'épée sur un pays, et que le peuple du pays prît dans son sein un homme dont ils fissent leur sentinelle,
3 ya kuma ga takobi yana zuwa a kan ƙasar ya kuwa busa ƙaho don yă faɗakar da mutane,
et qui, voyant venir l'épée sur le pays, sonnât de la trompette, pour avertir le peuple;
4 in wani ya ji busar amma bai kula ba, takobin zai zo ya ɗauki ransa, jininsa kuwa zai zauna a kansa.
si quelqu'un, entendant le son de la trompette, ne recevait pas l'avertissement, et que l'épée vînt et le surprît, son sang pèserait sur sa tête:
5 Da yake ya ji ƙarar busar amma bai kula ba, jininsa zai zauna a kansa. Da a ce ya kula, da ya ceci kansa.
il a ouï le son de la trompette, et n'a pas reçu l'avertissement, son sang pèse sur sa tête. Mais s'il reçoit l'avertissement, il sauvera son âme.
6 Amma a ce mai tsaron ya ga takobi yana zuwa bai kuwa busa ƙaho don yă faɗakar da mutane ba sai takobi ya zo ya ɗauki ran waninsu, za a kawar da wannan mutum saboda zunubinsa, amma zan nemi hakkin jinin mutumin a kan mai tsaron.’
Que si la sentinelle voyant venir l'épée, ne sonne pas de la trompette, et que, sans que le peuple soit averti, l'épée arrive et ôte la vie à un seul homme, cet homme périra par suite de son crime, mais je redemanderai son sang à la sentinelle.
7 “Ɗan mutum, na mai da kai mai tsaro bisa gidan Isra’ila; saboda haka ka ji abin da zan faɗa ka kuma gargaɗe su.
Or, fils de l'homme, je t'ai établi sentinelle pour la maison d'Israël, afin que de ma bouche tu entendes la parole, et que tu les avertisses de ma part.
8 Sa’ad da na ce wa mugu, ‘Ya mugun mutum, tabbatacce za ka mutu,’ kai kuma ba ka yi magana don ka juyar da shi daga hanyoyinsa ba, wannan mugun mutum zai mutu domin zunubinsa, zan kuma nemi hakkin jininsa a kanka.
Si je dis à l'impie: Impie, tu mourras! et que tu ne parles pas pour détourner par tes avis l'impie de sa voie, cet impie mourra par suite de son crime, mais je te redemanderai son sang.
9 Amma in ka faɗakar da mugun mutumin don yă juye daga hanyoyinsa bai kuwa yi haka ba, zai mutu saboda zunubinsa, amma kai za ka kuɓutar da kanka.
Mais si par tes avis tu as cherché à détourner l'impie de sa voie, pour qu'il la quitte, s'il ne la quitte pas, il mourra par suite de son crime; mais toi, tu auras sauvé ton âme.
10 “Ɗan mutum, faɗa wa gidan Isra’ila, ‘Ga abin da kuke cewa, “Laifofinmu da zunubanmu suna nawaita mana, muna kuma lalacewa saboda su. Ta ƙaƙa za mu rayu?”’
Donc, fils de l'homme, dis à la maison d'Israël: Vous dites: « Nous sommes sous le poids de nos péchés et de nos crimes, et c'est par eux que nous périssons; comment donc pourrions-nous vivre? »
11 Ka faɗa musu, ‘Muddin ina raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, ba na jin daɗin mutuwar mugu, amma a maimako haka ya fi su juye daga hanyoyinsu su rayu. Ku juye! Ku juye daga mugayen hanyoyinku! Don me za ku mutu, ya gidan Isra’ila?’
Dis-leur: Par ma vie, dit le Seigneur, l'Éternel, je ne prends point plaisir à la mort de l'impie, mais à ce que l'impie renonce à sa voie, et qu'il vive. Quittez, quittez vos mauvaises voies! Pourquoi voudriez-vous la mort, maison d'Israël?
12 “Saboda haka, ɗan mutum, ka faɗa wa mutanen ƙasarka, ‘Adalcin adali ba zai cece shi sa’ad da ya ƙi yin biyayya ba, kuma muguntar mugu ba za tă sa ya fāɗi sa’ad da ya juya daga gare ta ba. Adali, in ya yi zunubi, ba za a bari yă rayu saboda adalcinsa na dā ba.’
Et toi, fils de l'homme, dis aux enfants de ton peuple: La justice du juste ne le sauvera pas au jour qu'il péchera; et l'impiété de l'impie ne sera pas pour lui une cause de ruine, au jour qu'il abandonnera son impiété, de même que le juste n'aura pas dans sa justice une cause de vie, le jour qu'il deviendra pécheur.
13 In na faɗa wa adali cewa tabbatacce zai rayu, amma sai ya dogara ga adalcinsa ya kuma aikata mugunta, babu ayyukan adalcinsa da za a tuna; zai mutu saboda muguntar da ya aikata.
Si je dis du juste: Qu'il ait la vie! et que, se confiant en sa justice, il fasse le mal, il ne lui sera point tenu compte de toute sa justice, et il mourra par suite du mal qu'il a fait.
14 Kuma in na ce wa mugu, ‘Tabbatacce za ka mutu,’ amma sai ya juye daga zunubinsa ya kuma yi abin da yake gaskiya da kuma daidai,
Mais si je dis de l'impie: Qu'il meure! et que, renonçant à ses péchés, il agisse selon le droit et la justice,
15 in ya mayar da jingina, ya mayar da abin da ya sata, ya kiyaye ƙa’idodin da suke ba da rai, ya daina yin mugunta, tabbatacce zai rayu; ba zai mutu ba.
rendant le gage, restituant ce qu'il a pris, se conduisant selon les commandements qui donnent la vie, sans faire rien qui soit mal; il vivra, ne mourra point.
16 Babu wani zunubin da ya aikata da za a tuna da shi. Ya yi abin da yake gaskiya da kuma daidai; tabbatacce zai rayu.
De tous les péchés qu'il aura commis, il ne sera point tenu compte contre lui: il a fait ce qui est droit et juste; il vivra.
17 “Duk da haka mutanen ƙasarka sun ce, ‘Hanyar Ubangiji ba daidai ba ce.’ Alhali kuwa tasu ce ba daidai ba.
Cependant les enfants de ton peuple disent: « La voie du Seigneur n'est pas droite; » mais c'est votre voie qui n'est pas droite.
18 In adali ya juye daga adalcinsa ya yi mugunta, zai mutu saboda haka.
Quand le juste renonce à sa justice et fait le mal, il en meurt.
19 Kuma in mugu ya juye daga muguntarsa ya aikata abin da yake gaskiya da kuma daidai, zai rayu ta yin haka.
Et quand l'impie renonce à son impiété et fait ce qui est droit et juste, par là il obtient la vie.
20 Duk da haka, ya gidan Isra’ila kun ce, ‘Hanyar Ubangiji ba daidai ba ce.’ Amma zan hukunta kowane ɗayanku gwargwadon ayyukansa.”
Et vous dites: « La voie du Seigneur n'est pas droite! » Je vous jugerai chacun de vous selon la voie que vous suivez, maison d'Israël.
21 A shekara ta goma sha biyu ta zaman bautanmu, a wata na goma a rana ta biyar, wani mutumin da ya gudu daga Urushalima ya zo wurina ya ce, “Birnin ya fāɗi!”
Et la douzième année, le dixième mois, le cinquième jour du mois, depuis notre déportation, un homme qui s'était échappé de Jérusalem, arriva auprès de moi et dit: La ville est prise!
22 To a yamman da ya wuce kafin mutumin ya iso, hannun Ubangiji yana a kaina, ya kuma buɗe bakina kafin mutumin ya iso wurina da safe. Sai bakina ya buɗu ban kuma yi shiru ba.
Or la main de l'Éternel s'était fait sentir à moi la veille de l'arrivée de ce fugitif, et m'avait ouvert la bouche quand il arriva auprès de moi le matin; et ainsi, ma bouche s'ouvrit, et je ne fus plus muet.
23 Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Et la parole de l'Éternel me fut adressée en ces mots:
24 “Ɗan mutum, mutanen da suke zama a waɗannan kufai a ƙasar Isra’ila suna cewa, ‘Ibrahim mutum ɗaya ne kaɗai, duk da haka Ibrahim ya mallaki ƙasar. Amma mu da muke da yawa; lalle an ba mu ƙasar ta zama mallakarmu.’
Fils de l'homme, les habitants de ces ruines dans le pays d'Israël disent: « Abraham était un seul homme, et il a obtenu la propriété du pays; or nous sommes nombreux; la propriété du pays nous est dévolue. »
25 Saboda haka ka faɗa musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa da yake kun ci nama da jini a cikinsa kuka kuma bauta wa gumakanku kuka zub da jini, kuna gani za ku mallaki ƙasar?
C'est pourquoi, dis-leur: Ainsi parle le Seigneur, l'Éternel: Vous mettez du sang dans ce que vous mangez, et vous levez les yeux vers vos idoles, et vous répandez le sang; et vous posséderiez le pays!
26 Kun dogara ga takobinku, kuka aikata abubuwan banƙyama, kowannenku kuma ya ƙazantar da matar maƙwabcinsa. Kuna gani za ku mallaki ƙasar?’
Vous vous appuyez sur votre épée; vous, femmes, vous commettez des abominations; vous déshonorez la femme l'un de l'autre; et vous posséderiez le pays!
27 “Ka faɗa musu wannan, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa muddin ina raye, waɗanda aka rage a kufai za su fāɗi ga takobi, waɗanda suke bayan gari kuwa namun jeji za su cinye su, waɗanda suke a mafaka da kogwannin duwatsu annoba za tă kashe su.
Parle-leur ainsi: Ainsi parle le Seigneur, l'Éternel: Oui, par ma vie, ceux qui sont dans les ruines périront par l'épée, et ceux qui sont dans les champs, je les livrerai en proie aux bêtes féroces, et ceux qui sont dans les forts et dans les cavernes, mourront de la peste.
28 Zan mai da ƙasar kango, kuma fariyar ƙarfinta zai ƙare, duwatsun Isra’ila za su zama kufai don kada wani ya ratsa su.
Et du pays je ferai un désert et une solitude, et leur insolent orgueil prendra fin, et les montagnes d'Israël deviendront un désert que personne ne traverse.
29 Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji, sa’ad da na mai da ƙasar kango saboda dukan abubuwan banƙyamar da suka yi.’
Alors ils sauront que je suis l'Éternel, quand je ferai du pays un désert et une solitude à cause de toutes les abominations qu'ils ont commises.
30 “Game da kai kuma, ɗan mutum, mutanen ƙasarka suna magana da juna game da kai a katanga da kuma ƙofofin gidaje, suna ce wa juna, ‘Ku zo mu tafi mu ji maganar da ta zo daga wurin Ubangiji.’
Quant à toi, fils de l'homme, les enfants de ton peuple s'entretiennent de toi entre les murs et dans les portes de leurs maisons, et ils se parlent l'un à l'autre, chacun à son frère, et disent: « Venez donc, et écoutez quelle parole émane de l'Éternel! »
31 Mutanena sukan zo wurinka, yadda suka saba su zauna a gabanka don su saurari maganarka, amma ba sa aiki da abin da suka ji. Da bakunansu suna nuna ƙauna, amma zukatansu cike da haɗama suke don ƙazamar riba.
Et ils viennent à toi, comme un concours de peuple, et s'assoient devant toi, comme étant mon peuple, et ils écoutent tes paroles, mais ils ne les mettent point en pratique: mais ils font ce qui leur plaît, et leur cœur s'attache à leur cupidité.
32 Tabbatacce, gare su ba ka fi mai waƙar ƙauna da murya mai daɗi kana kuma yin kiɗa sosai ba, gama sukan ji maganarka amma ba sa amfani da ita.
Et voici, tu es pour eux comme un chant agréable par la beauté de la voix et l'harmonie de la musique; ils écoutent tes paroles, mais ne les mettent point en pratique.
33 “Sa’ad da dukan wannan ya cika kuma zai cika ɗin, sa’an nan za su sani akwai annabi a tsakiyarsu.”
Mais quand viendront [les maux], et voici, ils arrivent! ils comprendront qu'il y avait un prophète au milieu d'eux.

< Ezekiyel 33 >