< Ezekiyel 33 >

1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
La parole de l'Eternel me fut encore [adressée], en disant:
2 “Ɗan mutum, yi magana da mutanen ƙasarka ka faɗa musu cewa, ‘Sa’ad da na kawo takobi a kan ƙasar, mutanen ƙasar kuwa suka zaɓi ɗaya daga cikin mutanensu suka mai da shi mai tsaro,
Fils d'homme, parle aux enfants de ton peuple, et leur dis: quand je ferai venir l'épée sur quelque pays, et que le peuple du pays aura choisi quelqu'un d'entre eux, et l'aura établi pour leur servir de sentinelle;
3 ya kuma ga takobi yana zuwa a kan ƙasar ya kuwa busa ƙaho don yă faɗakar da mutane,
Et que lui voyant venir l'épée sur le pays, aura sonné du cor, et aura averti le peuple;
4 in wani ya ji busar amma bai kula ba, takobin zai zo ya ɗauki ransa, jininsa kuwa zai zauna a kansa.
Si [le peuple] ayant bien ouï le son du cor, ne se tient pas sur ses gardes, et qu'ensuite l'épée vienne, et le dépêche, son sang sera sur sa tête.
5 Da yake ya ji ƙarar busar amma bai kula ba, jininsa zai zauna a kansa. Da a ce ya kula, da ya ceci kansa.
Car il a ouï le son du cor, et ne s'est point tenu sur ses gardes; son sang donc sera sur lui-même; mais s'il se tient sur ses gardes, il sauvera sa vie.
6 Amma a ce mai tsaron ya ga takobi yana zuwa bai kuwa busa ƙaho don yă faɗakar da mutane ba sai takobi ya zo ya ɗauki ran waninsu, za a kawar da wannan mutum saboda zunubinsa, amma zan nemi hakkin jinin mutumin a kan mai tsaron.’
Que si la sentinelle voit venir l'épée, et qu'elle ne sonne point du cor, en sorte que le peuple ne se tienne point sur ses gardes, et qu'ensuite l'épée survienne, et ôte la vie à quelqu'un d'entre eux; celui-ci aura bien été surpris dans son iniquité, mais je redemanderai son sang de la main de la sentinelle.
7 “Ɗan mutum, na mai da kai mai tsaro bisa gidan Isra’ila; saboda haka ka ji abin da zan faɗa ka kuma gargaɗe su.
Toi donc, fils d'homme, je t'ai établi pour sentinelle à la maison d'Israël; tu écouteras donc la parole de ma bouche, et tu les avertiras de ma part.
8 Sa’ad da na ce wa mugu, ‘Ya mugun mutum, tabbatacce za ka mutu,’ kai kuma ba ka yi magana don ka juyar da shi daga hanyoyinsa ba, wannan mugun mutum zai mutu domin zunubinsa, zan kuma nemi hakkin jininsa a kanka.
Quand j'aurai dit au méchant: méchant, tu mourras de mort; et que tu n'auras point parlé au méchant pour [l']avertir [de se détourner] de sa voie, ce méchant mourra dans son iniquité; mais je redemanderai son sang de ta main.
9 Amma in ka faɗakar da mugun mutumin don yă juye daga hanyoyinsa bai kuwa yi haka ba, zai mutu saboda zunubinsa, amma kai za ka kuɓutar da kanka.
Mais si tu as averti le méchant de se détourner de sa voie, et qu'il ne se soit point détourné de sa voie, il mourra dans son iniquité; mais toi tu auras délivré ton âme.
10 “Ɗan mutum, faɗa wa gidan Isra’ila, ‘Ga abin da kuke cewa, “Laifofinmu da zunubanmu suna nawaita mana, muna kuma lalacewa saboda su. Ta ƙaƙa za mu rayu?”’
Toi donc, fils d'homme, dis à la maison d'Israël: vous avez parlé ainsi, en disant: puisque nos crimes et nos péchés sont sur nous, et que nous périssons à cause d'eux, comment pourrions-nous vivre?
11 Ka faɗa musu, ‘Muddin ina raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, ba na jin daɗin mutuwar mugu, amma a maimako haka ya fi su juye daga hanyoyinsu su rayu. Ku juye! Ku juye daga mugayen hanyoyinku! Don me za ku mutu, ya gidan Isra’ila?’
Dis-leur: je suis vivant, dit le Seigneur l'Eternel, que je ne prends point plaisir en la mort du méchant, mais plutôt que le méchant se détourne de sa voie, et qu'il vive. Détournez-vous, détournez-vous de votre méchante voie; et pourquoi mourriez-vous, maison d'Israël?
12 “Saboda haka, ɗan mutum, ka faɗa wa mutanen ƙasarka, ‘Adalcin adali ba zai cece shi sa’ad da ya ƙi yin biyayya ba, kuma muguntar mugu ba za tă sa ya fāɗi sa’ad da ya juya daga gare ta ba. Adali, in ya yi zunubi, ba za a bari yă rayu saboda adalcinsa na dā ba.’
Toi donc, fils d'homme, dis aux enfants de ton peuple: la justice du juste ne le délivrera point, au jour qu'il aura péché, et le méchant ne tombera point par sa méchanceté, au jour qu'il s'en sera détourné; et le juste ne pourra pas vivre par sa justice, au jour qu'il aura péché.
13 In na faɗa wa adali cewa tabbatacce zai rayu, amma sai ya dogara ga adalcinsa ya kuma aikata mugunta, babu ayyukan adalcinsa da za a tuna; zai mutu saboda muguntar da ya aikata.
Quand j'aurai dit au juste qu'il vivra certainement, et que lui, se confiant sur sa justice, aura commis l'iniquité, on ne se souviendra plus d'aucune de ses justices, mais il mourra dans son iniquité qu'il aura commise.
14 Kuma in na ce wa mugu, ‘Tabbatacce za ka mutu,’ amma sai ya juye daga zunubinsa ya kuma yi abin da yake gaskiya da kuma daidai,
Aussi quand j'aurai dit au méchant: tu mourras de mort; s'il se détourne de son péché, et qu'il fasse ce qui est juste et droit;
15 in ya mayar da jingina, ya mayar da abin da ya sata, ya kiyaye ƙa’idodin da suke ba da rai, ya daina yin mugunta, tabbatacce zai rayu; ba zai mutu ba.
[Si] le méchant rend le gage, et qu'il restitue ce qu'il aura ravi, et qu'il marche dans les statuts de la vie, sans commettre d'iniquité, certainement il vivra, il ne mourra point.
16 Babu wani zunubin da ya aikata da za a tuna da shi. Ya yi abin da yake gaskiya da kuma daidai; tabbatacce zai rayu.
On ne se souviendra plus des péchés qu'il aura commis; il a fait ce qui est juste et droit; certainement il vivra.
17 “Duk da haka mutanen ƙasarka sun ce, ‘Hanyar Ubangiji ba daidai ba ce.’ Alhali kuwa tasu ce ba daidai ba.
Or les enfants de ton peuple ont dit: la voie du Seigneur n'est pas bien réglée; [mais] c'est plutôt leur voie qui n'est pas bien réglée.
18 In adali ya juye daga adalcinsa ya yi mugunta, zai mutu saboda haka.
Quand le juste se détournera de sa justice, et qu'il commettra l'iniquité, il mourra pour ces choses-là.
19 Kuma in mugu ya juye daga muguntarsa ya aikata abin da yake gaskiya da kuma daidai, zai rayu ta yin haka.
Et quand le méchant se détournera de sa méchanceté, et qu'il fera ce qui est juste et droit, il vivra pour ces choses-là.
20 Duk da haka, ya gidan Isra’ila kun ce, ‘Hanyar Ubangiji ba daidai ba ce.’ Amma zan hukunta kowane ɗayanku gwargwadon ayyukansa.”
Et vous avez dit: la voie du Seigneur n'est pas bien réglée! Je vous jugerai, maison d'Israël, chacun selon sa voie.
21 A shekara ta goma sha biyu ta zaman bautanmu, a wata na goma a rana ta biyar, wani mutumin da ya gudu daga Urushalima ya zo wurina ya ce, “Birnin ya fāɗi!”
Or il arriva en la douzième année de notre captivité, au cinquième jour du dixième mois, que quelqu'un qui était échappé de Jérusalem vint vers moi, en disant: la ville a été prise.
22 To a yamman da ya wuce kafin mutumin ya iso, hannun Ubangiji yana a kaina, ya kuma buɗe bakina kafin mutumin ya iso wurina da safe. Sai bakina ya buɗu ban kuma yi shiru ba.
Et la main de l'Eternel avait été sur moi le soir avant que celui qui était échappé vînt, et [l'Eternel] avait ouvert ma bouche, en attendant que cet homme vînt le matin vers moi; et ma bouche ayant été ouverte, je ne me tus plus.
23 Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Et la parole de l'Eternel me fut [adressée], en disant:
24 “Ɗan mutum, mutanen da suke zama a waɗannan kufai a ƙasar Isra’ila suna cewa, ‘Ibrahim mutum ɗaya ne kaɗai, duk da haka Ibrahim ya mallaki ƙasar. Amma mu da muke da yawa; lalle an ba mu ƙasar ta zama mallakarmu.’
Fils d'homme, ceux qui habitent en ces lieux déserts, sur la terre d'Israël, discourent, en disant: Abraham était seul, et il a possédé le pays; mais nous sommes un grand nombre de gens; et le pays nous a été donné en héritage.
25 Saboda haka ka faɗa musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa da yake kun ci nama da jini a cikinsa kuka kuma bauta wa gumakanku kuka zub da jini, kuna gani za ku mallaki ƙasar?
C'est pourquoi tu leur diras: ainsi a dit le Seigneur l'Eternel: vous mangez la chair avec le sang, et vous levez vos yeux vers vos idoles, et vous répandez le sang; et vous posséderiez le pays?
26 Kun dogara ga takobinku, kuka aikata abubuwan banƙyama, kowannenku kuma ya ƙazantar da matar maƙwabcinsa. Kuna gani za ku mallaki ƙasar?’
Vous vous appuyez sur votre épée; vous commettez abomination, et vous souillez chacun de vous la femme de son prochain; et vous posséderiez le pays?
27 “Ka faɗa musu wannan, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa muddin ina raye, waɗanda aka rage a kufai za su fāɗi ga takobi, waɗanda suke bayan gari kuwa namun jeji za su cinye su, waɗanda suke a mafaka da kogwannin duwatsu annoba za tă kashe su.
Tu leur diras ainsi: ainsi a dit le Seigneur l'Eternel: je suis vivant, que ceux qui sont en ces lieux déserts tomberont par l'épée, et que je livrerai aux bêtes celui qui est par les champs, afin qu'elles le mangent; et que ceux qui sont dans les forteresses, et dans les cavernes, mourront de mortalité.
28 Zan mai da ƙasar kango, kuma fariyar ƙarfinta zai ƙare, duwatsun Isra’ila za su zama kufai don kada wani ya ratsa su.
Ainsi je réduirai le pays en désolation et en désert, tellement que l'orgueil de sa force sera aboli, et les montagnes d'Israël seront désolées, en sorte qu'il n'y passera plus personne.
29 Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji, sa’ad da na mai da ƙasar kango saboda dukan abubuwan banƙyamar da suka yi.’
Et ils connaîtront que je suis l'Eternel, quand j'aurai réduit leur pays en désolation et en désert, à cause de toutes leurs abominations qu'ils ont commises.
30 “Game da kai kuma, ɗan mutum, mutanen ƙasarka suna magana da juna game da kai a katanga da kuma ƙofofin gidaje, suna ce wa juna, ‘Ku zo mu tafi mu ji maganar da ta zo daga wurin Ubangiji.’
Et quant à toi, fils d'homme, les enfants de ton peuple causent de toi auprès des murailles, et aux entrées des maisons, et parlent l'un à l'autre chacun avec son prochain, en disant: venez maintenant, et écoutez quelle est la parole qui est procédée de l'Eternel.
31 Mutanena sukan zo wurinka, yadda suka saba su zauna a gabanka don su saurari maganarka, amma ba sa aiki da abin da suka ji. Da bakunansu suna nuna ƙauna, amma zukatansu cike da haɗama suke don ƙazamar riba.
Et ils viennent vers toi comme en foule, et mon peuple s'assied devant toi, et ils écoutent tes paroles, mais ils ne les mettent point en effet; ils les répètent comme si c'était une chanson profane, mais leur cœur marche toujours après leur gain déshonnête.
32 Tabbatacce, gare su ba ka fi mai waƙar ƙauna da murya mai daɗi kana kuma yin kiɗa sosai ba, gama sukan ji maganarka amma ba sa amfani da ita.
Et voici tu leur es comme un homme qui leur chante une chanson profane avec une belle voix, qui résonne bien; car ils écoutent bien tes paroles, mais ils ne les mettent point en effet.
33 “Sa’ad da dukan wannan ya cika kuma zai cika ɗin, sa’an nan za su sani akwai annabi a tsakiyarsu.”
Mais quand cela sera arrivé (et le voici qui vient), ils sauront qu'il y a eu un Prophète au milieu d'eux.

< Ezekiyel 33 >