< Ezekiyel 33 >

1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
La parole de l'Éternel me fut adressée, en ces mots:
2 “Ɗan mutum, yi magana da mutanen ƙasarka ka faɗa musu cewa, ‘Sa’ad da na kawo takobi a kan ƙasar, mutanen ƙasar kuwa suka zaɓi ɗaya daga cikin mutanensu suka mai da shi mai tsaro,
Fils de l'homme, parle aux enfants de ton peuple, et dis-leur: Quand je ferai venir l'épée sur un pays, et que le peuple de ce pays prendra un homme parmi eux, et l'établira comme sentinelle,
3 ya kuma ga takobi yana zuwa a kan ƙasar ya kuwa busa ƙaho don yă faɗakar da mutane,
si, s'il voit l'épée venir sur le pays, il sonne de la trompette et avertit le peuple,
4 in wani ya ji busar amma bai kula ba, takobin zai zo ya ɗauki ransa, jininsa kuwa zai zauna a kansa.
alors celui qui entendra le son de la trompette et ne tiendra pas compte de l'avertissement, si l'épée vient et l'emporte, son sang sera sur sa tête.
5 Da yake ya ji ƙarar busar amma bai kula ba, jininsa zai zauna a kansa. Da a ce ya kula, da ya ceci kansa.
Il a entendu le son de la trompette et n'a pas pris garde. Son sang retombera sur lui, alors que s'il avait écouté l'avertissement, il aurait sauvé son âme.
6 Amma a ce mai tsaron ya ga takobi yana zuwa bai kuwa busa ƙaho don yă faɗakar da mutane ba sai takobi ya zo ya ɗauki ran waninsu, za a kawar da wannan mutum saboda zunubinsa, amma zan nemi hakkin jinin mutumin a kan mai tsaron.’
Mais si la sentinelle voit venir l'épée et ne sonne pas de la trompette, et que le peuple ne soit pas averti, et que l'épée vienne et prenne quelqu'un d'entre eux, il sera emmené dans son iniquité, mais son sang, je le demanderai de la main de la sentinelle ».
7 “Ɗan mutum, na mai da kai mai tsaro bisa gidan Isra’ila; saboda haka ka ji abin da zan faɗa ka kuma gargaɗe su.
« Et toi, fils de l'homme, je t'ai établi comme sentinelle de la maison d'Israël. Écoute donc la parole de ma bouche et donne-leur des avertissements de ma part.
8 Sa’ad da na ce wa mugu, ‘Ya mugun mutum, tabbatacce za ka mutu,’ kai kuma ba ka yi magana don ka juyar da shi daga hanyoyinsa ba, wannan mugun mutum zai mutu domin zunubinsa, zan kuma nemi hakkin jininsa a kanka.
Si je dis au méchant: 'Méchant, tu mourras', et que tu ne parles pas pour détourner le méchant de sa voie, ce méchant mourra dans son iniquité, et je demanderai son sang de ta main.
9 Amma in ka faɗakar da mugun mutumin don yă juye daga hanyoyinsa bai kuwa yi haka ba, zai mutu saboda zunubinsa, amma kai za ka kuɓutar da kanka.
Cependant, si tu avertis le méchant de sa voie pour qu'il s'en détourne, et qu'il ne s'en détourne pas, il mourra dans son iniquité, mais tu auras sauvé ton âme.
10 “Ɗan mutum, faɗa wa gidan Isra’ila, ‘Ga abin da kuke cewa, “Laifofinmu da zunubanmu suna nawaita mana, muna kuma lalacewa saboda su. Ta ƙaƙa za mu rayu?”’
« Toi, fils de l'homme, dis à la maison d'Israël: « Vous dites ceci: « Nos transgressions et nos péchés sont sur nous, et nous dépérissons en eux. Comment donc pourrions-nous vivre?
11 Ka faɗa musu, ‘Muddin ina raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, ba na jin daɗin mutuwar mugu, amma a maimako haka ya fi su juye daga hanyoyinsu su rayu. Ku juye! Ku juye daga mugayen hanyoyinku! Don me za ku mutu, ya gidan Isra’ila?’
Dis-leur: « Je suis vivant, dit le Seigneur Yahvé, je ne prends pas plaisir à la mort du méchant, mais à ce que le méchant se détourne de sa voie et vive ». Tournez-vous, tournez-vous de vos mauvaises voies! Car pourquoi mourrez-vous, maison d'Israël? »
12 “Saboda haka, ɗan mutum, ka faɗa wa mutanen ƙasarka, ‘Adalcin adali ba zai cece shi sa’ad da ya ƙi yin biyayya ba, kuma muguntar mugu ba za tă sa ya fāɗi sa’ad da ya juya daga gare ta ba. Adali, in ya yi zunubi, ba za a bari yă rayu saboda adalcinsa na dā ba.’
« Toi, fils de l'homme, dis aux enfants de ton peuple: 'La justice du juste ne le délivrera pas au jour de sa désobéissance. Et quant à la méchanceté du méchant, il ne tombera pas sous son poids le jour où il se détournera de sa méchanceté; et le juste ne pourra pas vivre sous son poids le jour où il péchera.
13 In na faɗa wa adali cewa tabbatacce zai rayu, amma sai ya dogara ga adalcinsa ya kuma aikata mugunta, babu ayyukan adalcinsa da za a tuna; zai mutu saboda muguntar da ya aikata.
Quand je dis au juste qu'il vivra, s'il se confie dans sa justice et commet l'iniquité, on ne se souviendra d'aucune de ses actions justes, mais il mourra dans l'iniquité qu'il a commise.
14 Kuma in na ce wa mugu, ‘Tabbatacce za ka mutu,’ amma sai ya juye daga zunubinsa ya kuma yi abin da yake gaskiya da kuma daidai,
De même, quand je dis au méchant: « Tu mourras », s'il se détourne de son péché et fait ce qui est licite et juste,
15 in ya mayar da jingina, ya mayar da abin da ya sata, ya kiyaye ƙa’idodin da suke ba da rai, ya daina yin mugunta, tabbatacce zai rayu; ba zai mutu ba.
s'il restitue le gage, s'il rend ce qu'il avait pris par brigandage, s'il marche dans les règles de la vie, sans commettre d'iniquité, il vivra. Il ne mourra pas.
16 Babu wani zunubin da ya aikata da za a tuna da shi. Ya yi abin da yake gaskiya da kuma daidai; tabbatacce zai rayu.
On ne se souviendra pas contre lui des péchés qu'il a commis. Il a fait ce qui est licite et juste. Il vivra.
17 “Duk da haka mutanen ƙasarka sun ce, ‘Hanyar Ubangiji ba daidai ba ce.’ Alhali kuwa tasu ce ba daidai ba.
"'Les enfants de ton peuple disent: « La voie de l'Éternel n'est pas juste »; mais eux, leur voie n'est pas juste.
18 In adali ya juye daga adalcinsa ya yi mugunta, zai mutu saboda haka.
Quand le juste se détourne de sa justice et commet l'iniquité, il en meurt.
19 Kuma in mugu ya juye daga muguntarsa ya aikata abin da yake gaskiya da kuma daidai, zai rayu ta yin haka.
Si le méchant se détourne de sa méchanceté et fait ce qui est licite et juste, il vivra par cela.
20 Duk da haka, ya gidan Isra’ila kun ce, ‘Hanyar Ubangiji ba daidai ba ce.’ Amma zan hukunta kowane ɗayanku gwargwadon ayyukansa.”
Et vous dites: « La voie du Seigneur n'est pas juste ». Maison d'Israël, je jugerai chacun de vous selon ses voies.'"
21 A shekara ta goma sha biyu ta zaman bautanmu, a wata na goma a rana ta biyar, wani mutumin da ya gudu daga Urushalima ya zo wurina ya ce, “Birnin ya fāɗi!”
La douzième année de notre captivité, au dixième mois, le cinquième jour du mois, un fuyard de Jérusalem vint me trouver, disant: « La ville a été vaincue! »
22 To a yamman da ya wuce kafin mutumin ya iso, hannun Ubangiji yana a kaina, ya kuma buɗe bakina kafin mutumin ya iso wurina da safe. Sai bakina ya buɗu ban kuma yi shiru ba.
Or la main de Yahvé avait été sur moi le soir, avant que celui qui s'était échappé n'arrive; et il m'avait ouvert la bouche jusqu'à ce qu'il vienne me voir le matin; et ma bouche s'ouvrit, et je ne fus plus muet.
23 Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
La parole de Yahvé me fut adressée, en ces termes:
24 “Ɗan mutum, mutanen da suke zama a waɗannan kufai a ƙasar Isra’ila suna cewa, ‘Ibrahim mutum ɗaya ne kaɗai, duk da haka Ibrahim ya mallaki ƙasar. Amma mu da muke da yawa; lalle an ba mu ƙasar ta zama mallakarmu.’
« Fils d'homme, ceux qui habitent les lieux déserts du pays d'Israël disent: « Abraham était un, et il a hérité du pays; mais nous, nous sommes nombreux. Le pays nous est donné en héritage.
25 Saboda haka ka faɗa musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa da yake kun ci nama da jini a cikinsa kuka kuma bauta wa gumakanku kuka zub da jini, kuna gani za ku mallaki ƙasar?
C'est pourquoi tu leur diras: « Le Seigneur Yahvé dit: « Vous mangez avec le sang, vous levez les yeux vers vos idoles et vous versez le sang. Devriez-vous donc posséder le pays?
26 Kun dogara ga takobinku, kuka aikata abubuwan banƙyama, kowannenku kuma ya ƙazantar da matar maƙwabcinsa. Kuna gani za ku mallaki ƙasar?’
Vous vous appuyez sur votre épée, vous commettez des abominations, et chacun de vous souille la femme de son prochain. C'est ainsi que vous posséderez le pays? »
27 “Ka faɗa musu wannan, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa muddin ina raye, waɗanda aka rage a kufai za su fāɗi ga takobi, waɗanda suke bayan gari kuwa namun jeji za su cinye su, waɗanda suke a mafaka da kogwannin duwatsu annoba za tă kashe su.
Tu leur diras: « Le Seigneur Yahvé dit: « Je suis vivant, et ceux qui sont dans les ruines tomberont par l'épée. Je livrerai à la dévoration des bêtes ceux qui seront en plein champ, et ceux qui seront dans les forteresses et dans les cavernes mourront de la peste.
28 Zan mai da ƙasar kango, kuma fariyar ƙarfinta zai ƙare, duwatsun Isra’ila za su zama kufai don kada wani ya ratsa su.
Je ferai du pays un objet de désolation et d'étonnement. L'orgueil de sa puissance cessera. Les montagnes d'Israël seront désolées, et personne n'y passera.
29 Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji, sa’ad da na mai da ƙasar kango saboda dukan abubuwan banƙyamar da suka yi.’
Alors ils sauront que je suis Yahvé, quand j'aurai fait du pays une solitude et un objet de désolation, à cause de toutes les abominations qu'ils ont commises. »''
30 “Game da kai kuma, ɗan mutum, mutanen ƙasarka suna magana da juna game da kai a katanga da kuma ƙofofin gidaje, suna ce wa juna, ‘Ku zo mu tafi mu ji maganar da ta zo daga wurin Ubangiji.’
« Quant à toi, fils de l'homme, les enfants de ton peuple parlent de toi sur les murs et à la porte des maisons, et ils se parlent les uns aux autres, chacun à son frère, en disant: 'Viens, je te prie, et écoute ce qu'est la parole qui vient de l'Éternel'.
31 Mutanena sukan zo wurinka, yadda suka saba su zauna a gabanka don su saurari maganarka, amma ba sa aiki da abin da suka ji. Da bakunansu suna nuna ƙauna, amma zukatansu cike da haɗama suke don ƙazamar riba.
Ils viennent à toi comme le peuple vient, et ils s'assoient devant toi comme mon peuple, et ils entendent tes paroles, mais ils ne les mettent pas en pratique; car de leur bouche ils montrent beaucoup d'amour, mais leur cœur va après leur gain.
32 Tabbatacce, gare su ba ka fi mai waƙar ƙauna da murya mai daɗi kana kuma yin kiɗa sosai ba, gama sukan ji maganarka amma ba sa amfani da ita.
Voici, tu es pour eux comme un chant très beau de celui qui a une voix agréable, et qui sait bien jouer d'un instrument; car ils entendent tes paroles, mais ils ne les mettent pas en pratique.
33 “Sa’ad da dukan wannan ya cika kuma zai cika ɗin, sa’an nan za su sani akwai annabi a tsakiyarsu.”
« Quand cela arrivera - attention, cela arrive - alors ils sauront qu'un prophète a été parmi eux. »

< Ezekiyel 33 >