< Ezekiyel 33 >

1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Again the word of Jehovah came to me, saying:
2 “Ɗan mutum, yi magana da mutanen ƙasarka ka faɗa musu cewa, ‘Sa’ad da na kawo takobi a kan ƙasar, mutanen ƙasar kuwa suka zaɓi ɗaya daga cikin mutanensu suka mai da shi mai tsaro,
Son of man, speak to the children of thy people, and say to them, When I bring the sword upon a land, and the people of the land take a man out of their whole number, and set him for their watchman,
3 ya kuma ga takobi yana zuwa a kan ƙasar ya kuwa busa ƙaho don yă faɗakar da mutane,
and he seeth the sword coming on the land, and bloweth the trumpet, and warneth the people,
4 in wani ya ji busar amma bai kula ba, takobin zai zo ya ɗauki ransa, jininsa kuwa zai zauna a kansa.
then whoever heareth the sound of the trumpet, and taketh not warning, and the sword cometh and taketh him away, his blood shall be upon his own head.
5 Da yake ya ji ƙarar busar amma bai kula ba, jininsa zai zauna a kansa. Da a ce ya kula, da ya ceci kansa.
He heard the sound of the trumpet, and took not warning. His blood shall be upon him. But he that taketh warning shall save his life.
6 Amma a ce mai tsaron ya ga takobi yana zuwa bai kuwa busa ƙaho don yă faɗakar da mutane ba sai takobi ya zo ya ɗauki ran waninsu, za a kawar da wannan mutum saboda zunubinsa, amma zan nemi hakkin jinin mutumin a kan mai tsaron.’
But if the watchman see the sword coming, and blow not the trumpet, and the people be not warned, and the sword come and take away any person from among them, he is taken away for his iniquity, but his blood will I require at the watchman's hand.
7 “Ɗan mutum, na mai da kai mai tsaro bisa gidan Isra’ila; saboda haka ka ji abin da zan faɗa ka kuma gargaɗe su.
So thou, son of man, I have set thee a watchman to the house of Israel, that thou shouldst hear the word from my mouth, and warn them from me.
8 Sa’ad da na ce wa mugu, ‘Ya mugun mutum, tabbatacce za ka mutu,’ kai kuma ba ka yi magana don ka juyar da shi daga hanyoyinsa ba, wannan mugun mutum zai mutu domin zunubinsa, zan kuma nemi hakkin jininsa a kanka.
When I say to the wicked, “O wicked man, thou shalt surely die!” and thou speakest not to warn the wicked from his way, that wicked man shall die for his iniquity, but his blood will I require at thy hand.
9 Amma in ka faɗakar da mugun mutumin don yă juye daga hanyoyinsa bai kuwa yi haka ba, zai mutu saboda zunubinsa, amma kai za ka kuɓutar da kanka.
Yet if thou warn the wicked of his way, to turn from it, and he turneth not from his way, he shall die for his iniquity, but thou hast delivered thyself.
10 “Ɗan mutum, faɗa wa gidan Isra’ila, ‘Ga abin da kuke cewa, “Laifofinmu da zunubanmu suna nawaita mana, muna kuma lalacewa saboda su. Ta ƙaƙa za mu rayu?”’
Thou, therefore, O son of man, say to the house of Israel: Rightly do ye say, “Our transgressions and our sins are upon us, and through them we pine away. How then can we live?”
11 Ka faɗa musu, ‘Muddin ina raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, ba na jin daɗin mutuwar mugu, amma a maimako haka ya fi su juye daga hanyoyinsu su rayu. Ku juye! Ku juye daga mugayen hanyoyinku! Don me za ku mutu, ya gidan Isra’ila?’
Say to them, As I live, saith the Lord Jehovah, I have no pleasure in the death of the wicked, but that the wicked turn from his way and live; turn ye, turn ye, from your evil ways! for why will ye die, O house of Israel?
12 “Saboda haka, ɗan mutum, ka faɗa wa mutanen ƙasarka, ‘Adalcin adali ba zai cece shi sa’ad da ya ƙi yin biyayya ba, kuma muguntar mugu ba za tă sa ya fāɗi sa’ad da ya juya daga gare ta ba. Adali, in ya yi zunubi, ba za a bari yă rayu saboda adalcinsa na dā ba.’
Thou also, son of man, say to the sons of thy people, The righteousness of the righteous shall not deliver him in the day of his transgression; and through his wickedness shall not the wicked man fall in the day when he turneth from his wickedness; neither shall the righteous be able to live in the day when he sinneth.
13 In na faɗa wa adali cewa tabbatacce zai rayu, amma sai ya dogara ga adalcinsa ya kuma aikata mugunta, babu ayyukan adalcinsa da za a tuna; zai mutu saboda muguntar da ya aikata.
When I say concerning the righteous, “He shall surely live,” and he trusteth in his righteousness, and doeth iniquity, all his righteousness shall not be remembered, but for his iniquity which he hath committed shall he die.
14 Kuma in na ce wa mugu, ‘Tabbatacce za ka mutu,’ amma sai ya juye daga zunubinsa ya kuma yi abin da yake gaskiya da kuma daidai,
Again, when I say concerning the wicked, “He shall surely die,” and he turneth from his sin, and doeth that which is just and right,
15 in ya mayar da jingina, ya mayar da abin da ya sata, ya kiyaye ƙa’idodin da suke ba da rai, ya daina yin mugunta, tabbatacce zai rayu; ba zai mutu ba.
and the wicked restoreth the pledge, giveth back that which he hath taken by violence, and walketh in the statutes of life without committing iniquity, he shall surely live, he shall not die.
16 Babu wani zunubin da ya aikata da za a tuna da shi. Ya yi abin da yake gaskiya da kuma daidai; tabbatacce zai rayu.
None of his sins which he hath committed shall be mentioned to him; he hath done that which is just and right; he shall surely live.
17 “Duk da haka mutanen ƙasarka sun ce, ‘Hanyar Ubangiji ba daidai ba ce.’ Alhali kuwa tasu ce ba daidai ba.
And yet the sons of thy people say, “The way of the Lord is not right!” But it is their way which is not right.
18 In adali ya juye daga adalcinsa ya yi mugunta, zai mutu saboda haka.
When the righteous man turneth from his righteousness, and committeth iniquity, he dieth because of it.
19 Kuma in mugu ya juye daga muguntarsa ya aikata abin da yake gaskiya da kuma daidai, zai rayu ta yin haka.
And when the wicked turneth from his wickedness, and doeth that which is just and right, he shall live thereby.
20 Duk da haka, ya gidan Isra’ila kun ce, ‘Hanyar Ubangiji ba daidai ba ce.’ Amma zan hukunta kowane ɗayanku gwargwadon ayyukansa.”
And yet ye say, “The way of the Lord is not right!” O house of Israel, I will judge you every one according to his ways!
21 A shekara ta goma sha biyu ta zaman bautanmu, a wata na goma a rana ta biyar, wani mutumin da ya gudu daga Urushalima ya zo wurina ya ce, “Birnin ya fāɗi!”
And it came to pass in the twelfth year of our captivity, in the tenth month, on the fifth day of the month, that one who had escaped from Jerusalem came to me, saying, “The city is smitten!”
22 To a yamman da ya wuce kafin mutumin ya iso, hannun Ubangiji yana a kaina, ya kuma buɗe bakina kafin mutumin ya iso wurina da safe. Sai bakina ya buɗu ban kuma yi shiru ba.
Now the hand of Jehovah had been upon me in the evening before he that had escaped came; and he opened my mouth, until he came to me in the morning; he opened my mouth, so that I was no longer dumb.
23 Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
And the word of Jehovah came to me, saying:
24 “Ɗan mutum, mutanen da suke zama a waɗannan kufai a ƙasar Isra’ila suna cewa, ‘Ibrahim mutum ɗaya ne kaɗai, duk da haka Ibrahim ya mallaki ƙasar. Amma mu da muke da yawa; lalle an ba mu ƙasar ta zama mallakarmu.’
Son of man, they that inhabit those wastes in the land of Israel say, “Abraham was but one, and he inherited the land; but we are many; to us is the land given for an inheritance.”
25 Saboda haka ka faɗa musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa da yake kun ci nama da jini a cikinsa kuka kuma bauta wa gumakanku kuka zub da jini, kuna gani za ku mallaki ƙasar?
Therefore say to them, Thus saith the Lord Jehovah: Ye eat with the blood, and life up your eyes to your idols, and shed blood; and shall ye possess the land?
26 Kun dogara ga takobinku, kuka aikata abubuwan banƙyama, kowannenku kuma ya ƙazantar da matar maƙwabcinsa. Kuna gani za ku mallaki ƙasar?’
Ye trust to your swords, ye commit abomination, and ye defile, every one, his neighbor's wife; and shall ye possess the land?
27 “Ka faɗa musu wannan, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa muddin ina raye, waɗanda aka rage a kufai za su fāɗi ga takobi, waɗanda suke bayan gari kuwa namun jeji za su cinye su, waɗanda suke a mafaka da kogwannin duwatsu annoba za tă kashe su.
Say thou thus to them: Thus saith the Lord Jehovah: As I live, surely they that are in the wastes shall fall by the sword, and him that is in the open country will I give to the beasts to be devoured, and they that are in the forts and caves shall fall by the pestilence.
28 Zan mai da ƙasar kango, kuma fariyar ƙarfinta zai ƙare, duwatsun Isra’ila za su zama kufai don kada wani ya ratsa su.
And I will make the land an utter desolation; and the pride of her strength shall cease; and the mountains of Israel shall be desolate, so that none shall pass through.
29 Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji, sa’ad da na mai da ƙasar kango saboda dukan abubuwan banƙyamar da suka yi.’
Then shall they know that I am Jehovah, when I have made the land an utter desolation, on account of all the abominations which they practise.
30 “Game da kai kuma, ɗan mutum, mutanen ƙasarka suna magana da juna game da kai a katanga da kuma ƙofofin gidaje, suna ce wa juna, ‘Ku zo mu tafi mu ji maganar da ta zo daga wurin Ubangiji.’
As for thee, O son of man, the sons of thy people speak concerning thee by the walls, and in the doors of houses; and speak one to another, every man to his neighbor, saying, “Come, I pray you, and hear what is the word that goeth forth from Jehovah.”
31 Mutanena sukan zo wurinka, yadda suka saba su zauna a gabanka don su saurari maganarka, amma ba sa aiki da abin da suka ji. Da bakunansu suna nuna ƙauna, amma zukatansu cike da haɗama suke don ƙazamar riba.
And they come to thee, as the people assembleth, and they sit before thee, as my people, and they hear thy words: but will not do them; for with their mouth they do what is lovely, but their heart goeth after gain.
32 Tabbatacce, gare su ba ka fi mai waƙar ƙauna da murya mai daɗi kana kuma yin kiɗa sosai ba, gama sukan ji maganarka amma ba sa amfani da ita.
And behold, thou art to them as a very lovely song of one that hath a pleasant voice, and can play well on an instrument; for they hear thy words, but do them not.
33 “Sa’ad da dukan wannan ya cika kuma zai cika ɗin, sa’an nan za su sani akwai annabi a tsakiyarsu.”
But when this cometh to pass, (and behold, it shall come to pass, ) then shall they know that a prophet hath been among them.

< Ezekiyel 33 >