< Ezekiyel 33 >
1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
A message from the Lord came to me, saying,
2 “Ɗan mutum, yi magana da mutanen ƙasarka ka faɗa musu cewa, ‘Sa’ad da na kawo takobi a kan ƙasar, mutanen ƙasar kuwa suka zaɓi ɗaya daga cikin mutanensu suka mai da shi mai tsaro,
“Son of man, tell your people: If I brought an army to attack a country, the people there would choose one of them to be their watchman.
3 ya kuma ga takobi yana zuwa a kan ƙasar ya kuwa busa ƙaho don yă faɗakar da mutane,
When he saw the army advancing to attack the country, he would blow the trumpet to warn everyone.
4 in wani ya ji busar amma bai kula ba, takobin zai zo ya ɗauki ransa, jininsa kuwa zai zauna a kansa.
So if you hear the trumpet but don't pay attention to the warning, and you're killed in the attack, you will be responsible for your own death.
5 Da yake ya ji ƙarar busar amma bai kula ba, jininsa zai zauna a kansa. Da a ce ya kula, da ya ceci kansa.
Since you heard the trumpet but didn't pay attention to the warning, then you will be responsible for your own death. If you had paid attention the warning, you could have saved your life.
6 Amma a ce mai tsaron ya ga takobi yana zuwa bai kuwa busa ƙaho don yă faɗakar da mutane ba sai takobi ya zo ya ɗauki ran waninsu, za a kawar da wannan mutum saboda zunubinsa, amma zan nemi hakkin jinin mutumin a kan mai tsaron.’
But if the watchman saw the attack coming and didn't blow the trumpet to warn everyone, and someone is killed, then that person will die in their sins, but I will hold the watchman responsible for their death.
7 “Ɗan mutum, na mai da kai mai tsaro bisa gidan Isra’ila; saboda haka ka ji abin da zan faɗa ka kuma gargaɗe su.
Son of man, I have appointed you as a watchman for the people of Israel. Listen to what I tell you and warn them for me.
8 Sa’ad da na ce wa mugu, ‘Ya mugun mutum, tabbatacce za ka mutu,’ kai kuma ba ka yi magana don ka juyar da shi daga hanyoyinsa ba, wannan mugun mutum zai mutu domin zunubinsa, zan kuma nemi hakkin jininsa a kanka.
If I tell the wicked ‘You're wicked; you're going to die’; but you don't warn them to change what they're doing, then they'll die in their sins and I will hold your responsible for their deaths.
9 Amma in ka faɗakar da mugun mutumin don yă juye daga hanyoyinsa bai kuwa yi haka ba, zai mutu saboda zunubinsa, amma kai za ka kuɓutar da kanka.
But if you warn the wicked to change what they're doing, and they don't, they will die in their sins, but you will save your own life.
10 “Ɗan mutum, faɗa wa gidan Isra’ila, ‘Ga abin da kuke cewa, “Laifofinmu da zunubanmu suna nawaita mana, muna kuma lalacewa saboda su. Ta ƙaƙa za mu rayu?”’
Son of man, tell the people of Israel that this is what they've been saying, ‘We recognize our sins and wrongs, and they weigh on us, wearing us out. How can we go on living?’
11 Ka faɗa musu, ‘Muddin ina raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, ba na jin daɗin mutuwar mugu, amma a maimako haka ya fi su juye daga hanyoyinsu su rayu. Ku juye! Ku juye daga mugayen hanyoyinku! Don me za ku mutu, ya gidan Isra’ila?’
Tell them: As I live, declares the Lord God, it brings me no pleasure when wicked people die. I wish they would stop sinning and live! Stop! Stop sinning! Why should you die, people of Israel?
12 “Saboda haka, ɗan mutum, ka faɗa wa mutanen ƙasarka, ‘Adalcin adali ba zai cece shi sa’ad da ya ƙi yin biyayya ba, kuma muguntar mugu ba za tă sa ya fāɗi sa’ad da ya juya daga gare ta ba. Adali, in ya yi zunubi, ba za a bari yă rayu saboda adalcinsa na dā ba.’
So, son of man, tell your people: All the good things a good person has done won't save them when they sin; while the bad things a bad person has done won't be a problem for them if they stop sinning. But good people won't live if they start sinning.
13 In na faɗa wa adali cewa tabbatacce zai rayu, amma sai ya dogara ga adalcinsa ya kuma aikata mugunta, babu ayyukan adalcinsa da za a tuna; zai mutu saboda muguntar da ya aikata.
If I tell a good person that they will live and then they rely on their goodness and start sinning, then none of the good things they did will be remembered; he will die because of the sins.
14 Kuma in na ce wa mugu, ‘Tabbatacce za ka mutu,’ amma sai ya juye daga zunubinsa ya kuma yi abin da yake gaskiya da kuma daidai,
But if I tell a bad person, ‘You're going to die’ and they stop sinning and do what is good and right,
15 in ya mayar da jingina, ya mayar da abin da ya sata, ya kiyaye ƙa’idodin da suke ba da rai, ya daina yin mugunta, tabbatacce zai rayu; ba zai mutu ba.
if they return security given for a loan, pay back what they've stolen, and follows my laws about how to live, not doing wrong—then they will live; they won't die.
16 Babu wani zunubin da ya aikata da za a tuna da shi. Ya yi abin da yake gaskiya da kuma daidai; tabbatacce zai rayu.
None of their sins will be remembered; they have done what is good and right and so they will live.
17 “Duk da haka mutanen ƙasarka sun ce, ‘Hanyar Ubangiji ba daidai ba ce.’ Alhali kuwa tasu ce ba daidai ba.
However, your people are complaining, ‘What the Lord does isn't right.’ But it's what they're doing that isn't right.
18 In adali ya juye daga adalcinsa ya yi mugunta, zai mutu saboda haka.
If a good person stops doing good and sins, they will die because of it.
19 Kuma in mugu ya juye daga muguntarsa ya aikata abin da yake gaskiya da kuma daidai, zai rayu ta yin haka.
On the other hand, if a bad person turns from their sins and they do what is good and right, they will live as a result.
20 Duk da haka, ya gidan Isra’ila kun ce, ‘Hanyar Ubangiji ba daidai ba ce.’ Amma zan hukunta kowane ɗayanku gwargwadon ayyukansa.”
So how can you say, ‘What the Lord does isn't right’? Well, I'm going to judge each of you depending on what you've done, people of Israel.”
21 A shekara ta goma sha biyu ta zaman bautanmu, a wata na goma a rana ta biyar, wani mutumin da ya gudu daga Urushalima ya zo wurina ya ce, “Birnin ya fāɗi!”
On the fifth day of the tenth month of the twelfth year of our exile, a refugee who'd escaped from Jerusalem arrived and told me, “The city has been captured!”
22 To a yamman da ya wuce kafin mutumin ya iso, hannun Ubangiji yana a kaina, ya kuma buɗe bakina kafin mutumin ya iso wurina da safe. Sai bakina ya buɗu ban kuma yi shiru ba.
The previous evening before the messenger arrived the Lord had touched me so I could speak again. This was before the man came to see me in the morning. I wasn't mute any longer—I could speak again.
23 Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
A message from the Lord came to me, saying,
24 “Ɗan mutum, mutanen da suke zama a waɗannan kufai a ƙasar Isra’ila suna cewa, ‘Ibrahim mutum ɗaya ne kaɗai, duk da haka Ibrahim ya mallaki ƙasar. Amma mu da muke da yawa; lalle an ba mu ƙasar ta zama mallakarmu.’
“Son of man, people living among the ruins in Israel are saying, ‘Abraham was only one man, but the country was given to him to own. There's plenty of us, so the country should belong to us.’
25 Saboda haka ka faɗa musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa da yake kun ci nama da jini a cikinsa kuka kuma bauta wa gumakanku kuka zub da jini, kuna gani za ku mallaki ƙasar?
So tell them that this is what the Lord God says: You eat meat with the blood still in it. You go and worship your idols. You commit murder. Do you really think the country should belong to you?
26 Kun dogara ga takobinku, kuka aikata abubuwan banƙyama, kowannenku kuma ya ƙazantar da matar maƙwabcinsa. Kuna gani za ku mallaki ƙasar?’
You rely on your swords to get your way. You have done some disgusting things. You're all having sex with each other's wives. Should the country belong to you?
27 “Ka faɗa musu wannan, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa muddin ina raye, waɗanda aka rage a kufai za su fāɗi ga takobi, waɗanda suke bayan gari kuwa namun jeji za su cinye su, waɗanda suke a mafaka da kogwannin duwatsu annoba za tă kashe su.
Tell them that this is what the Lord God says: As I live, in the people living among the ruins will be killed by the sword. Those living in the countryside will be eaten by wild animals. Those living in the fortresses and caves will die from disease.
28 Zan mai da ƙasar kango, kuma fariyar ƙarfinta zai ƙare, duwatsun Isra’ila za su zama kufai don kada wani ya ratsa su.
I will turn the country into a wasteland, and power you are so proud of will be ended. The mountains of Israel will become wild places that no one will want to travel through.
29 Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji, sa’ad da na mai da ƙasar kango saboda dukan abubuwan banƙyamar da suka yi.’
Then the people will acknowledge that I am the Lord, when I have turned the country into a wasteland because of all the disgusting things they have done.
30 “Game da kai kuma, ɗan mutum, mutanen ƙasarka suna magana da juna game da kai a katanga da kuma ƙofofin gidaje, suna ce wa juna, ‘Ku zo mu tafi mu ji maganar da ta zo daga wurin Ubangiji.’
Son of man, your people are talking about you out in the streets and in the doorways of their houses. They encourage one another, saying, ‘Come on! Let's go and hear a message from the Lord!’
31 Mutanena sukan zo wurinka, yadda suka saba su zauna a gabanka don su saurari maganarka, amma ba sa aiki da abin da suka ji. Da bakunansu suna nuna ƙauna, amma zukatansu cike da haɗama suke don ƙazamar riba.
So my people come and visit you like they usually do. They sit and listen to the message you share, but they don't do anything about it. Even though they talk about love, all they're thinking about is how to cheat others.
32 Tabbatacce, gare su ba ka fi mai waƙar ƙauna da murya mai daɗi kana kuma yin kiɗa sosai ba, gama sukan ji maganarka amma ba sa amfani da ita.
In fact, to them you're just someone who sings love songs with a lovely voice and who is a fine musician. They listen to the message you share, but they don't do anything about it.
33 “Sa’ad da dukan wannan ya cika kuma zai cika ɗin, sa’an nan za su sani akwai annabi a tsakiyarsu.”
So when what you say does happen (and it will), then they will realize that they did have a prophet among them.”