< Ezekiyel 32 >

1 A shekara ta goma sha biyu, a wata na goma sha biyu a rana ta fari, maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
و در روز اول ماه دوازدهم از سال دوازدهم واقع شد که کلام خداوند برمن نازل شده، گفت:۱
2 “Ɗan mutum, ka yi makoki a kan Fir’auna sarkin Masar ka faɗa masa. “‘Kai kamar zaki ne a cikin al’ummai; kai kamar dodon ruwa a cikin tekuna kana ɓullowa cikin rafuffukanka, kana gurɓata ruwa da ƙafafunka kana kuma dama rafuffuka.
«ای پسر انسان برای فرعون پادشاه مصر مرثیه بخوان و او را بگو تو به شیرژیان امت‌ها مشابه می‌بودی، اما مانند اژدها دردریا هستی و آب را از بینی خود می‌جهانی و آبهارا به پایهای خود حرکت داده، نهرهای آنها راگل آلود می‌سازی.»۲
3 “‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Da taron jama’a masu yawa zan jefa abin kamun kifi a kanka, za su kuwa jawo ka da abin kamun kifi.
خداوند یهوه چنین می‌گوید: «دام خود را به واسطه گروهی از قوم های عظیم بر تو خواهم گسترانید و ایشان تورا در دام من بر خواهند کشید.۳
4 Zan jefar da kai a ƙasa zan jefa ka a fili. Zan sa dukan tsuntsayen sararin sama su zauna a kanka dukan namun jeji na duniya kuma za su ƙosar da kansu a kanka.
و تو را بر زمین ترک نموده، بر روی صحرا خواهم‌انداخت وهمه مرغان هوا را بر تو فرود آورده، جمیع حیوانات زمین را از تو سیر خواهم ساخت.۴
5 Zan baza namanka a kan duwatsu in kuma cika kwaruruka da gawarka.
وگوشت تو را بر کوهها نهاده، دره‌ها را از لاش تو پرخواهم کرد.۵
6 Zan jiƙa ƙasar da jininka mai gudu har zuwa duwatsu, magudanan ruwa za su cika da namanka.
و زمینی را که در آن شنا می‌کنی ازخون تو تا به کوهها سیراب می‌کنم که وادیها از توپر خواهد شد.۶
7 Sa’ad da na shafe ka, zan rufe sammai in duhunta taurarinsu; zan rufe rana da girgije, wata kuwa ba zai ba da haskensa ba.
و هنگامی که تو را منطفی گردانم، آسمان را خواهم پوشانید و ستارگانش راتاریک کرده، آفتاب را به ابرها مستور خواهم ساخت و ماه روشنایی خود را نخواهد داد.۷
8 Dukan haskokin sammai za su zama duhu a kanka; zan kawo duhu a kan ƙasarka, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
وخداوند یهوه می‌فرماید، که تمامی نیرهای درخشنده آسمان را برای تو سیاه کرده، تاریکی بر زمینت خواهم آورد.۸
9 Zan dami zukatan mutane masu yawa sa’ad da na kawo maka hallaka a cikin al’ummai, a cikin ƙasashen da ba ka taɓa sani ba.
و چون هلاکت تو را درمیان امت‌ها بر زمینهایی که ندانسته‌ای آورده باشم، آنگاه دلهای قوم های عظیم را محزون خواهم ساخت.۹
10 Zan sa mutane da yawa su giggice saboda abin da ya same ka, sarakunansu kuma za su yi rawar jiki saboda kai sa’ad da na kaɗa takobina a gabansu. A ranar fāɗuwarka kowannensu zai yi rawar jiki a kowane lokaci saboda ransa.
و قوم های عظیم را بر تومتحیر خواهم ساخت. و چون شمشیر خود راپیش روی ایشان جلوه دهم، پادشاهان ایشان به شدت دهشتناک خواهند شد. و در روز انهدام توهر یک از ایشان برای جان خود هر لحظه‌ای خواهند لرزید.»۱۰
11 “‘Gama ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Takobin sarkin Babilon zai auko maka.
زیرا خداوند یهوه چنین می‌گوید: «شمشیرپادشاه بابل بر تو خواهد آمد.۱۱
12 Zan sa jama’arka su mutu ta wurin takuban ƙarfafan mutane, masu bantsoro na dukan al’ummai. Za su lalatar da girman kan Masar, su kuma tumɓuke dukan jama’arta.
و به شمشیرهای جباران که جمیع ایشان از ستمکیشان امت هامی باشند، جمعیت تو را به زیر خواهم‌انداخت. وایشان غرور مصر را نابود ساخته، تمامی جمعیتش هلاک خواهند شد.۱۲
13 Zan hallaka dukan dabbobinta da suke kusa da ruwaye masu yawa ƙafar mutum ba zai ƙara damunsa ko kofaton dabba ya gurɓata shi.
و تمامی بهایم او را از کنارهای آبهای عظیم هلاک خواهم ساخت. و پای انسان دیگر آنها را گل آلودنخواهد ساخت. و سم بهایم آنها را گل آلودنخواهد ساخت.۱۳
14 Sa’an nan zan sa ruwanta su kwanta in sa rafuffukanta su gudu kamar mai, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
آنگاه خداوند یهوه می‌گوید: آبهای آنها را ساکت گردانیده، نهرهای آنها رامانند روغن جاری خواهم ساخت.۱۴
15 Sa’ad da na mai da Masar kufai na kuma raba ƙasar da abin da take cike da shi, sa’ad da na bugi dukan waɗanda suke cikinta, a sa’an nan ne za su san cewa ni ne Ubangiji.’
و چون زمین مصر را ویران کنم و آن زمین از هرچه در آن باشد خالی شود و چون جمیع ساکنانش را هلاک کنم، آنگاه خواهند دانست که من یهوه هستم.»۱۵
16 “Wannan ne makokin da za a yi mata.’Yan matan al’ummai za su rera shi; gama Masar da dukan jama’arta za su rera shi, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”
و خداوند یهوه می‌گوید: «مرثیه‌ای که ایشان خواهند خواند همین است. دختران امت‌ها این مرثیه را خواهند خواند. برای مصر و تمامی جمعیتش این مرثیه را خواهند خواند.»۱۶
17 A shekara ta goma sha biyu, a rana ta goma sha biyar ga wata, maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
و در روز پانزدهم ماه از سال دوازدهم واقع شد که کلام خداوند بر من نازل شده، گفت:۱۷
18 “Ɗan mutum, yi kuka saboda jama’ar Masar ka kuma tura ta da’yan matan manyan al’ummai zuwa ƙarƙashin ƙasa, tare da waɗanda suka gangara zuwa rami.
«ای پسر انسان برای جمعیت مصر ولوله نما و هم اورا و هم دختران امت های عظیم را با آنانی که به هاویه فرود می‌روند، به اسفلهای زمین فرود آور.۱۸
19 Ka ce, ‘Kin fi sauran tagomashi ne? Ki gangara, ki kwanta cikin marasa kaciya.’
از چه کس زیباتر هستی؟ فرود بیا و بانامختونان بخواب.۱۹
20 Za su fāɗi cikin waɗanda aka kashe da takobi. Takobin da an zāre; bari a ja ta a tafi tare da dukan jama’arta.
ایشان در میان مقتولان شمشیر خواهند افتاد. (مصر) به شمشیر تسلیم شده است. پس او را و تمامی جمعیتش رابکشید.۲۰
21 Daga cikin kabari manyan shugabanni za su yi maganar Masar da abokanta su ce, ‘Sun gangara sun kuma kwanta da marasa kaciya, tare da waɗanda aka kashe da takobi.’ (Sheol h7585)
اقویای جباران از میان عالم اموات اورا و انصار او را خطاب خواهند کرد. ایشان نامختون به شمشیر کشته شده، فرود آمده، خواهند خوابید. (Sheol h7585)۲۱
22 “Assuriya tana can tare da dukan sojojinta; an kewaye ta da kaburburan dukan waɗanda aka kashe, dukan waɗanda suka mutu ta wurin takobi.
«در آنجا آشور و تمامی جمعیت اوهستند. قبرهای ایشان گرداگرد ایشان است وجمیع ایشان کشته شده از شمشیر افتاده‌اند.۲۲
23 Kaburburansu suna cikin zurfafan rami kuma sojojinta suna kwance kewaye da kabarinta. Dukan waɗanda suka haddasa tsoro a ƙasar masu rai sun mutu, an kashe su da takobi.
که قبرهای ایشان به اسفلهای هاویه قرار داده شد وجمعیت ایشان به اطراف قبرهای ایشان‌اند.۲۳
24 “Elam tana can, tare da dukan jama’arta kewaye da kabarinta. Dukansu sun mutu, an kashe su da takobi. Dukan waɗanda suka haddasa tsoro a ƙasar masu rai sun gangara wurin marasa kaciya a duniyar da take ƙarƙashi. Suna shan kunya tare da waɗanda suka gangara zuwa rami.
در آنجاعیلام و تمامی جمعیتش هستند. قبرهای ایشان گرداگرد ایشان است و جمیع ایشان مقتول و ازشمشیر افتاده‌اند و به اسفلهای زمین نامختون فرود رفته‌اند، زیرا که در زمین زندگان باعث هیبت بوده‌اند. پس با آنانی که به هاویه فرود می‌روند، متحمل خجالت خویش خواهند بود.۲۴
25 An yi mata gado a cikin matattu, tare da dukan jama’arta kewaye da kabarinta. Dukansu marasa kaciya ne, da aka kashe da takobi. Domin tsoronsu ya bazu cikin ƙasar masu rai, suna shan kunya tare da waɗanda suka gangara zuwa rami; an kwantar da su tare da waɗanda aka kashe.
بستری برای او و تمامی جمعیتش در میان مقتولان قرارداده‌اند. قبرهای ایشان گرداگرد ایشان است وجمیع ایشان نامختون و مقتول شمشیرند. زیرا که در زمین زندگان باعث هیبت بودند. پس با آنانی که به هاویه فرود می‌روند، متحمل خجالت خویش خواهند بود. در میان کشتگان قرار داده شد.۲۵
26 “Meshek da Tubal suna can, tare da dukan jama’arsu kewaye da kaburburansu. Dukansu marasa kaciya ne, da aka kashe da takobi domin sun haddasa tsoronsu a ƙasar masu rai.
درآنجا ماشک و توبال و تمامی جمعیت آنهاهستند. قبرهای ایشان گرداگرد ایشان است وجمیع ایشان نامختون و مقتول شمشیرند. زیرا که در زمین زندگان باعث هیبت بودند.۲۶
27 Ba sun kwanta tare da sauran jarumawa marasa kaciyan da aka kashe, waɗanda suka gangara kabari tare da makaman yaƙinsu, waɗanda aka yi musu matashin kai da takubansu ba? Hukuncin zunubansu yana a bisa ƙasusuwansu, ko da yake tsoron waɗannan jarumawa ya manne cikin ƙasar masu rai. (Sheol h7585)
پس ایشان با جباران و نامختونانی که افتاده‌اند که با اسلحه جنگ خویش به هاویه فرود رفته‌اند، نخواهندخوابید. و ایشان شمشیرهای خود را زیر سرهای خود نهادند. و گناه ایشان بر استخوانهای ایشان خواهد بود. زیرا که در زمین زندگان باعث هیبت جباران بودند. (Sheol h7585)۲۷
28 “Kai kuma, ya Fir’auna, za a kakkarye ka za ka kuma kwanta a cikin marasa kaciya, tare da waɗanda aka kashe da takobi.
و اما تو در میان نامختونان شکسته شده، با مقتولان شمشیر خواهی خوابید.۲۸
29 “Edom tana can, sarakunanta da dukan yerimanta; duk da ikonsu, sun kwanta tare da waɗanda aka kashe da takobi. Suna kwance tare da marasa kaciya, tare da waɗanda suka gangara zuwa rami.
در آنجا ادوم و پادشاهانش و جمیع سرورانش هستند که در جبروت خود با مقتولان شمشیرقرار داده شدند. و ایشان با نامختونان و آنانی که به هاویه فرود می‌روند خواهند خوابید.۲۹
30 “Dukan yerima arewa da dukan Sidoniyawa suna can; sun gangara tare da waɗanda aka kashe cikin kunya duk da tsoron da suka haddasa ta wurin ikonsu. Sun kwanta tare da marasa kaciya tare da waɗanda aka kashe da takobi suna kuma shan kunya tare da waɗanda suka gangara zuwa rami.
در آنجاجمیع روسای شمال و همه صیدونیان هستند که با مقتولان فرود رفتند. از هیبتی که به جبروت خویش باعث آن بودند، خجل خواهند شد. پس با مقتولان شمشیر نامختون خواهند خوابید و باآنانی که به هاویه فرود می‌روند، متحمل خجالت خود خواهند شد.۳۰
31 “Fir’auna, shi da dukan sojojinsa, za su gan su zai kuma ta’azantu domin dukan jama’arsa da aka kashe da takobi, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
و خداوند یهوه می‌گوید که فرعون چون این را بیند درباره تمامی جمعیت خود خویشتن را تسلی خواهد داد و فرعون وتمامی لشکر او به شمشیر کشته خواهند شد.۳۱
32 Ko da yake na sa ta haddasa tsoro a ƙasar masu rai, Fir’auna da dukan jama’arsa za su kwanta a cikin marasa kaciya, tare da waɗanda aka kashe da takobi, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”
زیرا خداوند یهوه می‌گوید: من او را در زمین زندگان باعث هیبت گردانیدم. پس فرعون وتمامی جمعیت او را با مقتولان شمشیر در میان نامختونان خواهند خوابانید.»۳۲

< Ezekiyel 32 >