< Ezekiyel 32 >
1 A shekara ta goma sha biyu, a wata na goma sha biyu a rana ta fari, maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
La douzième année, le premier jour du douzième mois, la parole de l'Éternel me fut adressée, en ces termes:
2 “Ɗan mutum, ka yi makoki a kan Fir’auna sarkin Masar ka faɗa masa. “‘Kai kamar zaki ne a cikin al’ummai; kai kamar dodon ruwa a cikin tekuna kana ɓullowa cikin rafuffukanka, kana gurɓata ruwa da ƙafafunka kana kuma dama rafuffuka.
Fils de l'homme, prononce une complainte sur Pharaon, roi d'Égypte, et dis-lui: Tu semblais un lionceau parmi les nations; pareil au crocodile dans les mers, tu t'élançais dans tes fleuves; avec tes pieds tu troublais les eaux, et tu remplissais de boue leurs flots.
3 “‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Da taron jama’a masu yawa zan jefa abin kamun kifi a kanka, za su kuwa jawo ka da abin kamun kifi.
Ainsi a dit le Seigneur, l'Éternel: J'étendrai mes filets sur toi, par une multitude nombreuse de peuples, qui te tireront dans mes filets.
4 Zan jefar da kai a ƙasa zan jefa ka a fili. Zan sa dukan tsuntsayen sararin sama su zauna a kanka dukan namun jeji na duniya kuma za su ƙosar da kansu a kanka.
Je t'abandonnerai sur la terre, et te jetterai à la surface des champs; je ferai reposer sur toi tous les oiseaux des cieux, et je rassasierai de toi les bêtes de toute la terre.
5 Zan baza namanka a kan duwatsu in kuma cika kwaruruka da gawarka.
Je mettrai ta chair sur les montagnes, et de tes débris je remplirai les vallées.
6 Zan jiƙa ƙasar da jininka mai gudu har zuwa duwatsu, magudanan ruwa za su cika da namanka.
J'abreuverai de ton sang la terre où tu nages, jusqu'aux montagnes, et les ravins seront remplis de toi.
7 Sa’ad da na shafe ka, zan rufe sammai in duhunta taurarinsu; zan rufe rana da girgije, wata kuwa ba zai ba da haskensa ba.
Quand je t'éteindrai, je couvrirai les cieux, et j'obscurcirai leurs étoiles; je couvrirai le soleil de nuages, et la lune ne donnera plus sa lumière.
8 Dukan haskokin sammai za su zama duhu a kanka; zan kawo duhu a kan ƙasarka, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
A cause de toi, j'obscurcirai tous les luminaires qui éclairent les cieux, et je répandrai les ténèbres sur ton pays, dit le Seigneur, l'Éternel.
9 Zan dami zukatan mutane masu yawa sa’ad da na kawo maka hallaka a cikin al’ummai, a cikin ƙasashen da ba ka taɓa sani ba.
Je ferai frémir le cœur de beaucoup de peuples, quand j'annoncerai ta ruine parmi les nations, dans des pays que tu n'as point connus.
10 Zan sa mutane da yawa su giggice saboda abin da ya same ka, sarakunansu kuma za su yi rawar jiki saboda kai sa’ad da na kaɗa takobina a gabansu. A ranar fāɗuwarka kowannensu zai yi rawar jiki a kowane lokaci saboda ransa.
Je remplirai de stupeur beaucoup de peuples à ton sujet, et leurs rois seront éperdus à cause de toi, quand je brandirai devant eux mon épée. Ils trembleront à tout instant, chacun pour sa vie, au jour de ta ruine.
11 “‘Gama ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Takobin sarkin Babilon zai auko maka.
Car ainsi a dit le Seigneur, l'Éternel: L'épée du roi de Babylone fondra sur toi;
12 Zan sa jama’arka su mutu ta wurin takuban ƙarfafan mutane, masu bantsoro na dukan al’ummai. Za su lalatar da girman kan Masar, su kuma tumɓuke dukan jama’arta.
J'abattrai ta multitude par l'épée des hommes forts, tous les plus terribles d'entre les nations; ils détruiront l'orgueil de l'Égypte, et toute sa multitude sera anéantie.
13 Zan hallaka dukan dabbobinta da suke kusa da ruwaye masu yawa ƙafar mutum ba zai ƙara damunsa ko kofaton dabba ya gurɓata shi.
Je ferai périr tout son bétail près des grandes eaux; nul pied d'homme ne les troublera plus, aucun sabot de bête ne les troublera plus.
14 Sa’an nan zan sa ruwanta su kwanta in sa rafuffukanta su gudu kamar mai, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
Alors j'apaiserai ses eaux, et je ferai couler ses fleuves comme l'huile, dit le Seigneur, l'Éternel.
15 Sa’ad da na mai da Masar kufai na kuma raba ƙasar da abin da take cike da shi, sa’ad da na bugi dukan waɗanda suke cikinta, a sa’an nan ne za su san cewa ni ne Ubangiji.’
Quand je réduirai le pays d'Égypte en désolation, et que le pays sera dénué de tout ce dont il était rempli, quand je frapperai tous ses habitants, ils sauront que je suis l'Éternel.
16 “Wannan ne makokin da za a yi mata.’Yan matan al’ummai za su rera shi; gama Masar da dukan jama’arta za su rera shi, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”
Telle est la complainte; les filles des nations la chanteront d'une voix plaintive; elles la chanteront pour plaindre l'Égypte et toute sa multitude, dit le Seigneur, l'Éternel.
17 A shekara ta goma sha biyu, a rana ta goma sha biyar ga wata, maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
La douzième année, le quinzième jour du mois, la parole de l'Éternel me fut adressée, en ces termes:
18 “Ɗan mutum, yi kuka saboda jama’ar Masar ka kuma tura ta da’yan matan manyan al’ummai zuwa ƙarƙashin ƙasa, tare da waɗanda suka gangara zuwa rami.
Fils de l'homme, fais une lamentation sur la multitude de l'Égypte. Précipite-la, elle et les filles des nations puissantes, dans les profondeurs de la terre, avec ceux qui descendent dans la fosse!
19 Ka ce, ‘Kin fi sauran tagomashi ne? Ki gangara, ki kwanta cikin marasa kaciya.’
Vaux-tu mieux que d'autres? Descends, et couche-toi parmi les incirconcis!
20 Za su fāɗi cikin waɗanda aka kashe da takobi. Takobin da an zāre; bari a ja ta a tafi tare da dukan jama’arta.
Ils tomberont au milieu de ceux que l'épée a blessés à mort. L'épée est tirée. Entraînez-la avec toute sa multitude
21 Daga cikin kabari manyan shugabanni za su yi maganar Masar da abokanta su ce, ‘Sun gangara sun kuma kwanta da marasa kaciya, tare da waɗanda aka kashe da takobi.’ (Sheol )
Les plus vaillants héros lui parlent au sein du séjour des morts, avec ceux qui furent ses auxiliaires; ils sont descendus et couchés, les incirconcis que l'épée blessa à mort. (Sheol )
22 “Assuriya tana can tare da dukan sojojinta; an kewaye ta da kaburburan dukan waɗanda aka kashe, dukan waɗanda suka mutu ta wurin takobi.
Là est Assur et toute sa multitude, et autour de lui ses tombeaux; tous ont été blessés, et sont tombés par l'épée.
23 Kaburburansu suna cikin zurfafan rami kuma sojojinta suna kwance kewaye da kabarinta. Dukan waɗanda suka haddasa tsoro a ƙasar masu rai sun mutu, an kashe su da takobi.
Ses tombeaux se trouvent dans les profondeurs de la fosse, et sa multitude est rangée à l'entour; tous ont été blessés à mort, et sont tombés par l'épée, eux qui répandaient la terreur dans la terre des vivants.
24 “Elam tana can, tare da dukan jama’arta kewaye da kabarinta. Dukansu sun mutu, an kashe su da takobi. Dukan waɗanda suka haddasa tsoro a ƙasar masu rai sun gangara wurin marasa kaciya a duniyar da take ƙarƙashi. Suna shan kunya tare da waɗanda suka gangara zuwa rami.
Là est Élam et toute sa multitude, à l'entour de son tombeau. Tous sont blessés à mort, et sont tombés par l'épée; ils sont descendus incirconcis dans les profondeurs de la terre, eux qui répandaient la terreur sur la terre des vivants; ils portent leur ignominie avec ceux qui descendent dans la fosse.
25 An yi mata gado a cikin matattu, tare da dukan jama’arta kewaye da kabarinta. Dukansu marasa kaciya ne, da aka kashe da takobi. Domin tsoronsu ya bazu cikin ƙasar masu rai, suna shan kunya tare da waɗanda suka gangara zuwa rami; an kwantar da su tare da waɗanda aka kashe.
Au milieu des blessés à mort, on a mis sa couche, avec toute sa multitude; tout autour, ses tombeaux. Tous ces incirconcis sont blessés à mort par l'épée, car ils répandaient la terreur dans la terre des vivants; ils portent leur ignominie avec ceux qui descendent dans la fosse; on les a mis parmi les blessés à mort.
26 “Meshek da Tubal suna can, tare da dukan jama’arsu kewaye da kaburburansu. Dukansu marasa kaciya ne, da aka kashe da takobi domin sun haddasa tsoronsu a ƙasar masu rai.
Là sont Méshec, Tubal et toute leur multitude: tout autour, leurs tombeaux; tous ces incirconcis sont blessés à mort par l'épée, car ils répandaient la terreur dans la terre des vivants.
27 Ba sun kwanta tare da sauran jarumawa marasa kaciyan da aka kashe, waɗanda suka gangara kabari tare da makaman yaƙinsu, waɗanda aka yi musu matashin kai da takubansu ba? Hukuncin zunubansu yana a bisa ƙasusuwansu, ko da yake tsoron waɗannan jarumawa ya manne cikin ƙasar masu rai. (Sheol )
Mais ils ne sont point couchés avec les vaillants hommes, tombés d'entre les incirconcis, qui sont descendus au Sépulcre avec leurs armes de guerre, et sous la tête desquels on a mis leurs épées. Leurs iniquités couvrent leurs ossements, car ils furent la terreur des hommes vaillants sur la terre des vivants. (Sheol )
28 “Kai kuma, ya Fir’auna, za a kakkarye ka za ka kuma kwanta a cikin marasa kaciya, tare da waɗanda aka kashe da takobi.
Toi aussi, tu seras brisé au milieu des incirconcis, et tu seras couché avec ceux que l'épée a blessés à mort.
29 “Edom tana can, sarakunanta da dukan yerimanta; duk da ikonsu, sun kwanta tare da waɗanda aka kashe da takobi. Suna kwance tare da marasa kaciya, tare da waɗanda suka gangara zuwa rami.
Là est Édom, ses rois et ses princes, qui malgré leur vaillance ont été mis au nombre de ceux que l'épée a blessés à mort; ils sont couchés avec les incirconcis, et avec ceux qui descendent dans la fosse.
30 “Dukan yerima arewa da dukan Sidoniyawa suna can; sun gangara tare da waɗanda aka kashe cikin kunya duk da tsoron da suka haddasa ta wurin ikonsu. Sun kwanta tare da marasa kaciya tare da waɗanda aka kashe da takobi suna kuma shan kunya tare da waɗanda suka gangara zuwa rami.
Là sont tous les princes du nord, et tous les Sidoniens, qui sont descendus avec les blessés à mort, malgré la terreur qu'inspirait leur vaillance; ils sont confus, étendus, ces incirconcis, avec ceux que l'épée a blessés à mort, et ils portent leur ignominie, avec ceux qui descendent dans la fosse.
31 “Fir’auna, shi da dukan sojojinsa, za su gan su zai kuma ta’azantu domin dukan jama’arsa da aka kashe da takobi, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
Pharaon les verra, et se consolera de toute sa multitude; Pharaon et toute son armée seront blessés à mort par l'épée, dit le Seigneur, l'Éternel;
32 Ko da yake na sa ta haddasa tsoro a ƙasar masu rai, Fir’auna da dukan jama’arsa za su kwanta a cikin marasa kaciya, tare da waɗanda aka kashe da takobi, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”
Car je répandrai ma terreur sur la terre des vivants. Pharaon et toute sa multitude seront couchés au milieu des incirconcis, avec ceux que l'épée a blessés à mort, dit le Seigneur, l'Éternel.