< Ezekiyel 32 >

1 A shekara ta goma sha biyu, a wata na goma sha biyu a rana ta fari, maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Then it happened in the twelfth month of the twelfth year, on the first of the month, that the word of Yahweh came to me, saying,
2 “Ɗan mutum, ka yi makoki a kan Fir’auna sarkin Masar ka faɗa masa. “‘Kai kamar zaki ne a cikin al’ummai; kai kamar dodon ruwa a cikin tekuna kana ɓullowa cikin rafuffukanka, kana gurɓata ruwa da ƙafafunka kana kuma dama rafuffuka.
“Son of man, lift up a lament concerning Pharaoh the king of Egypt; say to him, 'You are like a young lion among the nations, but you are like a monster in the seas; you churn up the water, you stir up the waters with your feet and muddy their waters.
3 “‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Da taron jama’a masu yawa zan jefa abin kamun kifi a kanka, za su kuwa jawo ka da abin kamun kifi.
The Lord Yahweh says this: So I will spread my net over you in the assembly of many peoples, and they will lift you up in my net.
4 Zan jefar da kai a ƙasa zan jefa ka a fili. Zan sa dukan tsuntsayen sararin sama su zauna a kanka dukan namun jeji na duniya kuma za su ƙosar da kansu a kanka.
I will abandon you in the land. I will throw you into a field and cause all the birds of the heavens to settle on you; the hunger of all living animals on earth will be satisfied by you.
5 Zan baza namanka a kan duwatsu in kuma cika kwaruruka da gawarka.
For I will put your flesh on the mountains, and I will fill the valleys with your worm-filled corpse.
6 Zan jiƙa ƙasar da jininka mai gudu har zuwa duwatsu, magudanan ruwa za su cika da namanka.
Then I will pour your blood over the mountains, and the stream beds will be filled with your blood.
7 Sa’ad da na shafe ka, zan rufe sammai in duhunta taurarinsu; zan rufe rana da girgije, wata kuwa ba zai ba da haskensa ba.
Then when I extinguish you, I will cover the heavens and darken their stars; I will cover the sun with clouds, and the moon will not shine its light.
8 Dukan haskokin sammai za su zama duhu a kanka; zan kawo duhu a kan ƙasarka, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
All the shining lights in the heavens I will darken over you, and I will put darkness over your land—this is the Lord Yahweh's declaration.
9 Zan dami zukatan mutane masu yawa sa’ad da na kawo maka hallaka a cikin al’ummai, a cikin ƙasashen da ba ka taɓa sani ba.
So I will terrify the heart of many peoples in lands that you do not know, when I bring about your collapse among the nations, among lands that you have not known.
10 Zan sa mutane da yawa su giggice saboda abin da ya same ka, sarakunansu kuma za su yi rawar jiki saboda kai sa’ad da na kaɗa takobina a gabansu. A ranar fāɗuwarka kowannensu zai yi rawar jiki a kowane lokaci saboda ransa.
I will shock many peoples concerning you; their kings will shudder in horror concerning you when I swing my sword before them. Every moment each one will tremble because of you, on the day of your downfall.
11 “‘Gama ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Takobin sarkin Babilon zai auko maka.
For the Lord Yahweh says this: The sword of the king of Babylon will come against you.
12 Zan sa jama’arka su mutu ta wurin takuban ƙarfafan mutane, masu bantsoro na dukan al’ummai. Za su lalatar da girman kan Masar, su kuma tumɓuke dukan jama’arta.
I will cause your multitudes to fall by warriors' swords—each warrior a terror of nations. These warriors will devastate the pride of Egypt and destroy all of its multitudes.
13 Zan hallaka dukan dabbobinta da suke kusa da ruwaye masu yawa ƙafar mutum ba zai ƙara damunsa ko kofaton dabba ya gurɓata shi.
For I will destroy all the livestock from beside the plentiful waters; the foot of man will no longer stir the waters up, neither will the hooves of cattle stir them.
14 Sa’an nan zan sa ruwanta su kwanta in sa rafuffukanta su gudu kamar mai, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
Then I will calm their waters and make their rivers run like oil— this is the Lord Yahweh's declaration.
15 Sa’ad da na mai da Masar kufai na kuma raba ƙasar da abin da take cike da shi, sa’ad da na bugi dukan waɗanda suke cikinta, a sa’an nan ne za su san cewa ni ne Ubangiji.’
When I make the land of Egypt an abandoned place, when the land is made bare of all its fullness, when I attack all the inhabitants in her, they will know that I am Yahweh.
16 “Wannan ne makokin da za a yi mata.’Yan matan al’ummai za su rera shi; gama Masar da dukan jama’arta za su rera shi, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”
There will be a lament; the daughters of the nations will lament over her; they will lament over Egypt, over all her multitudes they will lament—this is the Lord Yahweh's declaration.'”
17 A shekara ta goma sha biyu, a rana ta goma sha biyar ga wata, maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Then it happened in the twelfth year, on the fifteenth day of the month, that the word of Yahweh came to me, saying,
18 “Ɗan mutum, yi kuka saboda jama’ar Masar ka kuma tura ta da’yan matan manyan al’ummai zuwa ƙarƙashin ƙasa, tare da waɗanda suka gangara zuwa rami.
“Son of man, weep for the multitudes of Egypt and bring them down— her and the daughters of majestic nations—to the lowest earth with those who have gone down to the pit.
19 Ka ce, ‘Kin fi sauran tagomashi ne? Ki gangara, ki kwanta cikin marasa kaciya.’
'Are you really more beautiful than anyone else? Go down and lie down with the uncircumcised.'
20 Za su fāɗi cikin waɗanda aka kashe da takobi. Takobin da an zāre; bari a ja ta a tafi tare da dukan jama’arta.
They will fall among those who were killed by the sword. The sword has been drawn! She has been given to the sword; they will seize her and her multitudes.
21 Daga cikin kabari manyan shugabanni za su yi maganar Masar da abokanta su ce, ‘Sun gangara sun kuma kwanta da marasa kaciya, tare da waɗanda aka kashe da takobi.’ (Sheol h7585)
The strongest of the warriors in Sheol will declare about Egypt and her allies, 'They have come down here! They will lie with the uncircumcised, with those who were killed by the sword.' (Sheol h7585)
22 “Assuriya tana can tare da dukan sojojinta; an kewaye ta da kaburburan dukan waɗanda aka kashe, dukan waɗanda suka mutu ta wurin takobi.
Assyria is there with all her assembly. Her graves surround her; all of them were killed by the sword.
23 Kaburburansu suna cikin zurfafan rami kuma sojojinta suna kwance kewaye da kabarinta. Dukan waɗanda suka haddasa tsoro a ƙasar masu rai sun mutu, an kashe su da takobi.
Those whose graves are set in the recesses of the pit are there, with all her assembly. Her graves surround all of those who were killed, who fell by the sword, those who brought terror on the land of the living.
24 “Elam tana can, tare da dukan jama’arta kewaye da kabarinta. Dukansu sun mutu, an kashe su da takobi. Dukan waɗanda suka haddasa tsoro a ƙasar masu rai sun gangara wurin marasa kaciya a duniyar da take ƙarƙashi. Suna shan kunya tare da waɗanda suka gangara zuwa rami.
Elam is there with all her multitudes. Her graves surround her; all of them were killed. Those who fell by the sword, who have gone down uncircumcised to the lowest parts of the earth, who brought their terrors on the land of the living and who carry their own shame, together with the ones going down to the pit.
25 An yi mata gado a cikin matattu, tare da dukan jama’arta kewaye da kabarinta. Dukansu marasa kaciya ne, da aka kashe da takobi. Domin tsoronsu ya bazu cikin ƙasar masu rai, suna shan kunya tare da waɗanda suka gangara zuwa rami; an kwantar da su tare da waɗanda aka kashe.
They set a bedroll for Elam and all her multitudes in the midst of the slain; her graves surround her. All of them are uncircumcised, pierced by the sword, because they had brought their terrors on the land of the living. So they carry their own shame, together with the ones going down to the pit among all those who have been killed, those who are going down to the pit. Elam is among all those who were killed.
26 “Meshek da Tubal suna can, tare da dukan jama’arsu kewaye da kaburburansu. Dukansu marasa kaciya ne, da aka kashe da takobi domin sun haddasa tsoronsu a ƙasar masu rai.
Meshech, Tubal, and all their multitudes are there! Their graves surround them. All of them are uncircumcised, killed by the sword, because they had brought their terrors on the land of the living.
27 Ba sun kwanta tare da sauran jarumawa marasa kaciyan da aka kashe, waɗanda suka gangara kabari tare da makaman yaƙinsu, waɗanda aka yi musu matashin kai da takubansu ba? Hukuncin zunubansu yana a bisa ƙasusuwansu, ko da yake tsoron waɗannan jarumawa ya manne cikin ƙasar masu rai. (Sheol h7585)
They do not lie with the fallen warriors of the uncircumcised who have gone down to Sheol with all their weapons of war, and with their swords placed under their heads and their iniquities over their bones. For they were the terror of warriors in the land of the living. (Sheol h7585)
28 “Kai kuma, ya Fir’auna, za a kakkarye ka za ka kuma kwanta a cikin marasa kaciya, tare da waɗanda aka kashe da takobi.
So you, Egypt, will be broken in the midst of the uncircumcised! You will lie alongside those who were pierced by the sword.
29 “Edom tana can, sarakunanta da dukan yerimanta; duk da ikonsu, sun kwanta tare da waɗanda aka kashe da takobi. Suna kwance tare da marasa kaciya, tare da waɗanda suka gangara zuwa rami.
Edom is there with her kings and all her leaders. They have been placed in their strength with those killed by the sword. With the uncircumcised they lie, with those who have gone down to the pit.
30 “Dukan yerima arewa da dukan Sidoniyawa suna can; sun gangara tare da waɗanda aka kashe cikin kunya duk da tsoron da suka haddasa ta wurin ikonsu. Sun kwanta tare da marasa kaciya tare da waɗanda aka kashe da takobi suna kuma shan kunya tare da waɗanda suka gangara zuwa rami.
The princes of the north are there—all of them and all the Sidonians who went down with the ones who had been pierced. They were powerful and made others to be afraid, but now they are there in shame, uncircumcised with those who were pierced by the sword. They carry their own shame, together with the ones going down to the pit.
31 “Fir’auna, shi da dukan sojojinsa, za su gan su zai kuma ta’azantu domin dukan jama’arsa da aka kashe da takobi, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
Pharaoh will look and be comforted about all his multitudes who were pierced by the sword—Pharaoh and all his army—this is the Lord Yahweh's declaration.
32 Ko da yake na sa ta haddasa tsoro a ƙasar masu rai, Fir’auna da dukan jama’arsa za su kwanta a cikin marasa kaciya, tare da waɗanda aka kashe da takobi, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”
I put him as my terrifying one in the land of the living, but he will be laid down in the midst of the uncircumcised, among those pierced by the sword, Pharaoh and all his multitudes—this is the Lord Yahweh's declaration.”

< Ezekiyel 32 >