< Ezekiyel 31 >

1 A shekara ta goma sha ɗaya, a wata na uku a rana ta farko, maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Sürgünlüğümüzün on birinci yılı, üçüncü ayın birinci günü RAB bana şöyle seslendi:
2 “Ɗan mutum, faɗa wa Fir’auna sarkin Masar da jama’arsa cewa, “‘Da wa za a kwatanta girmanka?
“İnsanoğlu, firavuna ve halkına de ki, “‘Görkemde kim seninle boy ölçüşebilir?
3 Ka dubi Assuriya, ta taɓa zama kamar al’ul a Lebanon da rassa masu kyau suna inuwartar da kurmi; ya yi tsayi ainun kansa ya kai cikin gizagizai.
Asur'a bak! Lübnan'da bir sedir ağacıydı, Ormana gölge salan güzel dalları vardı. Çok yüksekti, tepesi bulutlara erişiyordu.
4 Ruwa ya sa ya yi girma, zurfafan maɓulɓulai sun sa ya yi tsayi; rafuffuka suna gudu kewaye da tushensa yana aika da rafuffukansa zuwa dukan itatuwan kurmi.
Sular ağacı besledi, Derin su kaynakları büyüttü. Akarsular dikili olduğu yerin çevresine akıyor, Kanalları kırdaki bütün ağaçlara erişiyordu.
5 Saboda haka ya yi tsayi fiye da sauran itatuwan kurmi; rassansa suka ƙaru suka yi tsayi, suka bazu saboda yalwar ruwaye.
Kırdaki bütün ağaçlardan daha çok büyüdü. Bol su verildiği için Dal budak saldı, dalları uzadı.
6 Dukan tsuntsayen sararin sama suka yi sheƙa a rassansa, dukan namun jeji suka haihu a ƙarƙashin rassansa; dukan al’ummai suka zauna a inuwarsa.
Kuşlar dallarına yuva yaptı, Yabanıl hayvanlar dalları altında yavruladı, Büyük uluslar gölgesinde yaşadı.
7 Yana da girma a kyau, da dogayen rassansa da ya baza, gama saiwoyinsa sun nutse can ƙasa har cikin yalwar ruwaye.
Güzellikte eşsizdi. Dalları giderek uzadı, Çünkü kökleri bol su alıyordu.
8 Al’ul a cikin lambun Allah ba su kai shi ba, balle itatuwan kasharina su kai rassansa, ko itatuwan durumi su kai rassansa, ko itace a lambun Allah ya kai kyansa.
Tanrı'nın bahçesindeki sedir ağaçlarından hiçbiri Onunla boy ölçüşemezdi, Çam ağaçları dalları kadar bile değildi. Çınarlar onun dallarıyla boy ölçüşemezdi. Tanrı'nın bahçesindeki ağaçların hiçbiri Onun kadar güzel değildi.
9 Na sa ya yi kyau da yalwar rassa, abin ƙyashi na dukan itatuwan Eden a lambun Allah.
Sık dallarla o sedir ağacını güzelleştirdim. Tanrı'nın bahçesi Aden'deki bütün ağaçlar onu kıskandı.
10 “‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa domin ya yi tsayi, kansa kuma ya kai cikin gizagizai, kuma domin ya yi fariya saboda tsayinsa,
“‘Bu yüzden Egemen RAB şöyle diyor: Ağaç büyüyüp boy attığı, tepesi bulutlara eriştiği, büyüklüğünden ötürü gurura kapıldığı için
11 na miƙa shi ga mai mulkin al’ummai, don yă sāka masa gwargwadon muguntarsa. Na jefar da shi a gefe,
ben de onu kovdum, ulusların önderinin eline teslim ettim. Ona kötülüğü uyarınca davranacak.
12 kuma baƙi mafi mugunta na al’ummai suka sare shi suka bar shi. Rassansa sun fāɗi a kan duwatsun da suke cikin dukan kwaruruka; rassansa kuma sun kakkarye, sun fāɗi a cikin dukan magudanan ruwa na ƙasa. Dukan al’umman duniya suka fito daga ƙarƙashin inuwarsa suka bar shi.
Yabancı ulusların en acımasızı onu kesip yalnız bıraktı. Dalları dağlara, derelere düştü; ülkenin vadilerinde kesilmiş duruyor. Yeryüzündeki bütün uluslar gölgesinden çekilip onu bıraktılar.
13 Dukan tsuntsaye sararin sama suka zauna a itacen da ya fāɗi, dukan namun jeji kuma suna cikin rassansa.
Bütün kuşlar devrik ağaca kondu, yabanıl hayvanlar dalları arasına yerleşti.
14 Saboda haka ba wani daga cikin itatuwan da suke kusa da ruwan da zai taɓa yin fariyar tsawonsa, har kawunansu su kai cikin gizagizai. Ba wani daga cikin itatuwan da ya sha ruwa sosai da zai taɓa yi wannan tsayi; duk an bashe su ga mutuwa, zuwa can ƙasa, a cikin matattu, tare da waɗanda suka gangara zuwa rami.
Öyle ki, suların yakınında yetişen hiçbir ağaç böylesi büyüyüp boy atmasın, tepesini bulutlara eriştirmesin; bol suyla sulanan hiçbir ağaç bu denli yükselmesin. Çünkü hepsi ölüm çukuruna inen insanlarla birlikte ölüme, yerin derinliklerine gidecek.
15 “‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa a ranar da aka yi ƙasa da shi zuwa kabari na rufe zurfafa maɓulɓulai da makoki dominsa; na janye rafuffukansa, aka kuma hana yalwan ruwansa. Saboda shi na rufe Lebanon da baƙin ciki, dukan itatuwan kurmi suka bushe. (Sheol h7585)
“‘Egemen RAB şöyle diyor: Sedir ağacı ölüler diyarına indiği gün, ona yas tutsunlar diye derin su kaynaklarını kapattım. Irmaklarını durdurdum, gür sularının önünü kestim. O ağaç yüzünden Lübnan'ı karanlığa boğdum, bütün orman ağaçlarını kuruttum. (Sheol h7585)
16 Na sa al’ummai suka yi rawar jiki da jin ƙarar fāɗuwarsa sa’ad da na yi ƙasa da shi zuwa kabari tare da waɗanda suka gangara rami. Sai dukan itatuwan Eden, zaɓaɓɓu da kuma mafi kyau na Lebanon, dukan itatuwan da aka yi musu banruwa, sun ta’azantu a ƙarƙashin ƙasa. (Sheol h7585)
Ölüm çukuruna inenlerle birlikte onu ölüler diyarına indirdiğimde, yıkılışının gürültüsünden ulusları titrettim. O zaman Aden Bahçesi'ndeki bütün ağaçlar, Lübnan'ın en seçkin, en iyi, bol sulanan ağaçları yerin derinliklerinde avunç buldu. (Sheol h7585)
17 Waɗanda suka zauna a inuwarsa, dukan masu tarayyarsa a cikin al’ummai, su ma sun gangara zuwa kabari tare da shi, sun haɗu da waɗanda aka kashe da takobi. (Sheol h7585)
Gölgesinde yaşayanlar, uluslar arasında onu destekleyenler de onunla birlikte ölüler diyarına, kılıçla öldürülmüşlerin yanına indiler. (Sheol h7585)
18 “‘Da wa cikin itatuwan Eden za a kwatanta da kai cikin girma da daraja? Duk da haka kai ma, za a yi ƙasa da kai tare da itatuwan Eden zuwa ƙarƙashin ƙasa; za ka kwanta a cikin marasa kaciya, tare da waɗanda aka kashe da takobi. “‘Fir’auna ke nan da dukan jama’arsa, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”
“‘Aden ağaçlarından hangisi görkem ve yücelikte seninle boy ölçüşebilir? Ama sen de Aden ağaçlarıyla birlikte yerin derinliklerine indirilecek, sünnetsizlere, kılıçla öldürülmüşlere katılacaksın. “‘İşte firavunla halkının sonu böyle olacaktır.’ Egemen RAB böyle diyor.”

< Ezekiyel 31 >