< Ezekiyel 31 >
1 A shekara ta goma sha ɗaya, a wata na uku a rana ta farko, maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Et il arriva en la onzième année, au troisième mois, au premier jour du mois, que la parole du Seigneur me fut adressée, disant:
2 “Ɗan mutum, faɗa wa Fir’auna sarkin Masar da jama’arsa cewa, “‘Da wa za a kwatanta girmanka?
Fils d’un homme, dis à Pharaon, roi d’Egypte, et à son peuple: À qui es-tu devenu semblable dans ta grandeur?
3 Ka dubi Assuriya, ta taɓa zama kamar al’ul a Lebanon da rassa masu kyau suna inuwartar da kurmi; ya yi tsayi ainun kansa ya kai cikin gizagizai.
Voilà qu’Assur était comme un cèdre sur le Liban, beau en ses branches, abondant en feuillage, et d’une hauteur très élevée, et entre des rameaux touffus montait sa cime.
4 Ruwa ya sa ya yi girma, zurfafan maɓulɓulai sun sa ya yi tsayi; rafuffuka suna gudu kewaye da tushensa yana aika da rafuffukansa zuwa dukan itatuwan kurmi.
Des eaux l’ont nourri; l’abîme l’a fait pousser en haut; ses fleuves coulaient autour de ses racines, et il a envoyé ses ruisseaux vers tous les arbres de la campagne.
5 Saboda haka ya yi tsayi fiye da sauran itatuwan kurmi; rassansa suka ƙaru suka yi tsayi, suka bazu saboda yalwar ruwaye.
À cause de cela, sa hauteur s’est élevée au-dessus de tous les arbres de la contrée, et ses branches se sont multipliées; et ses rameaux se sont élevés, arrosés par les grandes eaux.
6 Dukan tsuntsayen sararin sama suka yi sheƙa a rassansa, dukan namun jeji suka haihu a ƙarƙashin rassansa; dukan al’ummai suka zauna a inuwarsa.
Et, lorsqu’il eut étendu son ombre, tous les volatiles du ciel firent leur nid sur ses rameaux, et sous son feuillage toutes les bêtes des forêts déposèrent leurs petits, et sous son ombrage habitait une troupe de nations très nombreuses.
7 Yana da girma a kyau, da dogayen rassansa da ya baza, gama saiwoyinsa sun nutse can ƙasa har cikin yalwar ruwaye.
Et il était très beau dans sa grandeur et dans l’étendue de ses branches, car sa racine était près des grandes eaux.
8 Al’ul a cikin lambun Allah ba su kai shi ba, balle itatuwan kasharina su kai rassansa, ko itatuwan durumi su kai rassansa, ko itace a lambun Allah ya kai kyansa.
Les cèdres n’étaient pas plus élevés dans le paradis de Dieu, les sapins n’égalaient pas sa cime, et les platanes ne lui étaient pas égaux en feuillage; aucun arbre du paradis de Dieu ne fut comparable à lui et à sa beauté.
9 Na sa ya yi kyau da yalwar rassa, abin ƙyashi na dukan itatuwan Eden a lambun Allah.
Parce que je le fis si beau, et avec des feuilles si nombreuses et si épaisses, tous les arbres de délices, qui étaient dans le paradis de Dieu, lui ont porté envie.
10 “‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa domin ya yi tsayi, kansa kuma ya kai cikin gizagizai, kuma domin ya yi fariya saboda tsayinsa,
À cause de cela, voici ce que dit le Seigneur Dieu: Parce qu’il s’est élevé en hauteur, et qu’il a poussé sa cime verdoyante et touffue, et que son cœur s’est enorgueilli dans sa grandeur,
11 na miƙa shi ga mai mulkin al’ummai, don yă sāka masa gwargwadon muguntarsa. Na jefar da shi a gefe,
Je l’ai livré à la main de l’homme le plus fort des nations, qui agira comme il voudra; selon son impiété je l’ai rejeté.
12 kuma baƙi mafi mugunta na al’ummai suka sare shi suka bar shi. Rassansa sun fāɗi a kan duwatsun da suke cikin dukan kwaruruka; rassansa kuma sun kakkarye, sun fāɗi a cikin dukan magudanan ruwa na ƙasa. Dukan al’umman duniya suka fito daga ƙarƙashin inuwarsa suka bar shi.
Et des étrangers, et les hommes les plus cruels des nations le couperont par le pied, et le jetteront sur les montagnes; et dans toutes les vallées tomberont ses rameaux, et ses branches seront brisées sur tous les rochers de la terre; et tous les peuples de la terre se retireront de son ombrage et l’abandonneront.
13 Dukan tsuntsaye sararin sama suka zauna a itacen da ya fāɗi, dukan namun jeji kuma suna cikin rassansa.
Dans ses ruines ont habité tous les volatiles du ciel, et dans ses rameaux ont demeuré toutes les bêtes de la contrée.
14 Saboda haka ba wani daga cikin itatuwan da suke kusa da ruwan da zai taɓa yin fariyar tsawonsa, har kawunansu su kai cikin gizagizai. Ba wani daga cikin itatuwan da ya sha ruwa sosai da zai taɓa yi wannan tsayi; duk an bashe su ga mutuwa, zuwa can ƙasa, a cikin matattu, tare da waɗanda suka gangara zuwa rami.
C’est pour cette raison qu’aucun arbre planté sur les eaux ne s’élèvera dans sa hauteur, et il ne portera pas son sommet au milieu de rameaux touffus et feuillus, et aucun de ceux qui sont arrosés par les eaux ne se soutiendra dans son élévation, parce que tous ont été livrés à la mort, précipités au fond de la terre, au milieu des fils des hommes, avec ceux qui descendent dans la fosse.
15 “‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa a ranar da aka yi ƙasa da shi zuwa kabari na rufe zurfafa maɓulɓulai da makoki dominsa; na janye rafuffukansa, aka kuma hana yalwan ruwansa. Saboda shi na rufe Lebanon da baƙin ciki, dukan itatuwan kurmi suka bushe. (Sheol )
Voici ce que dit le Seigneur Dieu: Au jour qu’il est descendu aux enfers, j’ai fait faire un deuil, je l’ai couvert de l’abîme; et j’ai arrêté ses fleuves, et retenu les grandes eaux: le Liban a été attristé sur lui, et tous les arbres des champs ont été ébranlés. (Sheol )
16 Na sa al’ummai suka yi rawar jiki da jin ƙarar fāɗuwarsa sa’ad da na yi ƙasa da shi zuwa kabari tare da waɗanda suka gangara rami. Sai dukan itatuwan Eden, zaɓaɓɓu da kuma mafi kyau na Lebanon, dukan itatuwan da aka yi musu banruwa, sun ta’azantu a ƙarƙashin ƙasa. (Sheol )
Par le bruit de sa ruine, j’ai agité des nations, lorsque je le conduisais dans l’enfer avec ceux qui descendent dans la fosse; et ils se sont consolés au fond de la terre, tous les arbres de délices, beaux et magnifiques du Liban, tous ceux qui étaient arrosés par les eaux. (Sheol )
17 Waɗanda suka zauna a inuwarsa, dukan masu tarayyarsa a cikin al’ummai, su ma sun gangara zuwa kabari tare da shi, sun haɗu da waɗanda aka kashe da takobi. (Sheol )
Car eux-mêmes aussi descendront avec lui dans l’enfer parmi les tués par le glaive; et le bras de chacun d’eux restera immobile sous son ombrage au milieu des nations. (Sheol )
18 “‘Da wa cikin itatuwan Eden za a kwatanta da kai cikin girma da daraja? Duk da haka kai ma, za a yi ƙasa da kai tare da itatuwan Eden zuwa ƙarƙashin ƙasa; za ka kwanta a cikin marasa kaciya, tare da waɗanda aka kashe da takobi. “‘Fir’auna ke nan da dukan jama’arsa, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”
À qui as-tu été assimilé, ô illustre et sublime entre les arbres de délices? Voilà que tu as été précipité au plus profond de la terre avec les arbres de délices, tu dormiras au milieu des incirconcis, avec ceux qui ont été tués par le glaive; c’est là Pharaon lui-même et toute sa multitude, dit le Seigneur Dieu.