< Ezekiyel 31 >
1 A shekara ta goma sha ɗaya, a wata na uku a rana ta farko, maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Et en l'année onzième, le troisième mois, le premier jour du mois, la parole du Seigneur me vint, disant:
2 “Ɗan mutum, faɗa wa Fir’auna sarkin Masar da jama’arsa cewa, “‘Da wa za a kwatanta girmanka?
Fils de l'homme, dis au Pharaon, roi d'Égypte, et à son peuple: À qui t'es-tu comparé en ton orgueil?
3 Ka dubi Assuriya, ta taɓa zama kamar al’ul a Lebanon da rassa masu kyau suna inuwartar da kurmi; ya yi tsayi ainun kansa ya kai cikin gizagizai.
Voilà qu'Assur était un cyprès du Liban, et il était beau par ses branches, par la hauteur de sa tige et par sa cime s'élevant au milieu des nuées.
4 Ruwa ya sa ya yi girma, zurfafan maɓulɓulai sun sa ya yi tsayi; rafuffuka suna gudu kewaye da tushensa yana aika da rafuffukansa zuwa dukan itatuwan kurmi.
Les eaux l'avaient nourri; l'abîme l'avait fait croître en conduisant ses fleuves autour de ses racines, et ses ondes se répandaient vers tous les arbres des champs.
5 Saboda haka ya yi tsayi fiye da sauran itatuwan kurmi; rassansa suka ƙaru suka yi tsayi, suka bazu saboda yalwar ruwaye.
Aussi dépassait-il en hauteur tous les arbres des champs, et ses rameaux s'étaient déployés, grâce à l'abondance des eaux.
6 Dukan tsuntsayen sararin sama suka yi sheƙa a rassansa, dukan namun jeji suka haihu a ƙarƙashin rassansa; dukan al’ummai suka zauna a inuwarsa.
Tous les oiseaux du ciel faisaient leurs nids dans ses branches, et toutes les bêtes des champs mettaient bas sous son feuillage, une multitude de nations habitaient sous son ombre.
7 Yana da girma a kyau, da dogayen rassansa da ya baza, gama saiwoyinsa sun nutse can ƙasa har cikin yalwar ruwaye.
Il était beau par sa grandeur et par la multitude de ses rameaux; car ses racines étaient arrosées d'une eau abondante.
8 Al’ul a cikin lambun Allah ba su kai shi ba, balle itatuwan kasharina su kai rassansa, ko itatuwan durumi su kai rassansa, ko itace a lambun Allah ya kai kyansa.
Tels sont les cyprès du paradis de Dieu; les pins ne peuvent lui être comparés pour leurs rejetons; les sapins ne peuvent lui être comparés pour leurs rameaux; nul autre arbre du paradis de Dieu ne lui ressemble en beauté,
9 Na sa ya yi kyau da yalwar rassa, abin ƙyashi na dukan itatuwan Eden a lambun Allah.
Pour la multitude de ses rameaux. Et les arbres du paradis de délices de Dieu lui portaient envie.
10 “‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa domin ya yi tsayi, kansa kuma ya kai cikin gizagizai, kuma domin ya yi fariya saboda tsayinsa,
À cause de cela, voici ce que dit le Seigneur: En punition de ce que tu as tant grandi, de ce que tu as élevé ta cime au milieu des nuées, et que je l'ai vu se glorifier ainsi,
11 na miƙa shi ga mai mulkin al’ummai, don yă sāka masa gwargwadon muguntarsa. Na jefar da shi a gefe,
Je l'ai livré aux mains du prince des nations, et il a préparé sa ruine.
12 kuma baƙi mafi mugunta na al’ummai suka sare shi suka bar shi. Rassansa sun fāɗi a kan duwatsun da suke cikin dukan kwaruruka; rassansa kuma sun kakkarye, sun fāɗi a cikin dukan magudanan ruwa na ƙasa. Dukan al’umman duniya suka fito daga ƙarƙashin inuwarsa suka bar shi.
Et des hommes de pestilence, des étrangers, venus des nation l'ont détruit, et ils l'ont abattu sur les montagnes; ses rameaux sont tombés dans tous les vallons; sa tige a été brisée dans toutes les plaines de la terre, et tous les peuples des nations se sont retirés de son ombre, et ils l'ont rasé au niveau du sol.
13 Dukan tsuntsaye sararin sama suka zauna a itacen da ya fāɗi, dukan namun jeji kuma suna cikin rassansa.
Sur ses ruines se sont reposés tous les oiseaux du ciel, et toutes les bêtes des champs se sont blotties sous ses grosses branches;
14 Saboda haka ba wani daga cikin itatuwan da suke kusa da ruwan da zai taɓa yin fariyar tsawonsa, har kawunansu su kai cikin gizagizai. Ba wani daga cikin itatuwan da ya sha ruwa sosai da zai taɓa yi wannan tsayi; duk an bashe su ga mutuwa, zuwa can ƙasa, a cikin matattu, tare da waɗanda suka gangara zuwa rami.
Afin que nul des arbres qui croissent au bord des eaux ne se glorifiât de sa grandeur. Ils ont élevé leur cime au milieu des nues; mais ils ne se maintiendront pas en leur élévation; tous ces arbres, baignés des eaux, ont tous été donnés à la mort; ils iront tous au fond de la terre, au milieu des fils des hommes, avec ceux qui descendent à l'abîme.
15 “‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa a ranar da aka yi ƙasa da shi zuwa kabari na rufe zurfafa maɓulɓulai da makoki dominsa; na janye rafuffukansa, aka kuma hana yalwan ruwansa. Saboda shi na rufe Lebanon da baƙin ciki, dukan itatuwan kurmi suka bushe. (Sheol )
Et voici ce que dit le Seigneur Maître: Le jour où cet arbre est descendu aux enfers, l'abîme a pleuré sur lui. Et j'ai suspendu le cours de tous ses fleuves, et j'ai arrêté les grandes eaux qui l'arrosaient; et le Liban, à cause de lui, s'est couvert de ténèbres, et tous les arbres se sont affaissés de douleur. (Sheol )
16 Na sa al’ummai suka yi rawar jiki da jin ƙarar fāɗuwarsa sa’ad da na yi ƙasa da shi zuwa kabari tare da waɗanda suka gangara rami. Sai dukan itatuwan Eden, zaɓaɓɓu da kuma mafi kyau na Lebanon, dukan itatuwan da aka yi musu banruwa, sun ta’azantu a ƙarƙashin ƙasa. (Sheol )
Au bruit de sa chute, les nations ont tremblé; car je l'ai fait descendre aux enfers avec ceux qui étaient tombés dans l'abîme; et tous les arbres de délices de la terre le consolaient, et tous les beaux arbres du Liban arrosés par les eaux. (Sheol )
17 Waɗanda suka zauna a inuwarsa, dukan masu tarayyarsa a cikin al’ummai, su ma sun gangara zuwa kabari tare da shi, sun haɗu da waɗanda aka kashe da takobi. (Sheol )
Et ceux-là aussi sont descendus avec lui aux enfers, parmi les morts frappés par le glaive; et sa race, qui demeurait sous son abri, a péri au milieu de sa vie. (Sheol )
18 “‘Da wa cikin itatuwan Eden za a kwatanta da kai cikin girma da daraja? Duk da haka kai ma, za a yi ƙasa da kai tare da itatuwan Eden zuwa ƙarƙashin ƙasa; za ka kwanta a cikin marasa kaciya, tare da waɗanda aka kashe da takobi. “‘Fir’auna ke nan da dukan jama’arsa, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”
À quoi te comparer? Descends; sois entraîné, avec tous les arbres de délices, au plus profond de la terre; tu seras étendu au milieu des incirconcis avec les morts frappés par le glaive. Tel sera le Pharaon, telle sera la multitude qui faisait sa force, dit le Seigneur Maître.