< Ezekiyel 31 >

1 A shekara ta goma sha ɗaya, a wata na uku a rana ta farko, maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
II advint, dans la onzième année, le premier jour du troisième mois, que la parole de l’Eternel me fut adressée en ces termes:
2 “Ɗan mutum, faɗa wa Fir’auna sarkin Masar da jama’arsa cewa, “‘Da wa za a kwatanta girmanka?
"Fils de l’homme, dis à Pharaon, roi d’Egypte, et à sa cohue: A qui es-tu comparable dans ta grandeur?
3 Ka dubi Assuriya, ta taɓa zama kamar al’ul a Lebanon da rassa masu kyau suna inuwartar da kurmi; ya yi tsayi ainun kansa ya kai cikin gizagizai.
Voici, il était sur le Liban un cèdre superbe, aux belles branches, à la frondaison ombreuse, haut de stature; sa cime perçait les nuages.
4 Ruwa ya sa ya yi girma, zurfafan maɓulɓulai sun sa ya yi tsayi; rafuffuka suna gudu kewaye da tushensa yana aika da rafuffukansa zuwa dukan itatuwan kurmi.
Les eaux l’avaient fait croître, la source profonde l’avait développé, en faisant courir ses flots autour de sa plantation et en dirigeant ses canaux vers tous les arbres de la campagne.
5 Saboda haka ya yi tsayi fiye da sauran itatuwan kurmi; rassansa suka ƙaru suka yi tsayi, suka bazu saboda yalwar ruwaye.
Aussi, sa taille surpassait celle de tous les arbres de la campagne, ses branches s’étaient multipliées et ses rameaux, grâce à l’abondance des eaux, s’étaient allongés, car il les projetait au loin.
6 Dukan tsuntsayen sararin sama suka yi sheƙa a rassansa, dukan namun jeji suka haihu a ƙarƙashin rassansa; dukan al’ummai suka zauna a inuwarsa.
Dans ses branches nichaient tous les oiseaux du ciel, et sous ses rameaux mettaient bas' toutes les bêtes des champs. A son ombre demeuraient toutes les grandes nations.
7 Yana da girma a kyau, da dogayen rassansa da ya baza, gama saiwoyinsa sun nutse can ƙasa har cikin yalwar ruwaye.
Il était beau dans sa grandeur, par la longueur de ses rameaux, car sa racine baignait dans de grandes eaux.
8 Al’ul a cikin lambun Allah ba su kai shi ba, balle itatuwan kasharina su kai rassansa, ko itatuwan durumi su kai rassansa, ko itace a lambun Allah ya kai kyansa.
Les cèdres ne l’avaient pas éclipsé au jardin de Dieu, les cyprès n’étaient pas comparables à ses branches, et les platanes ne rivalisaient pas avec ses rameaux: aucun arbre du jardin de Dieu ne l’égalait en beauté.
9 Na sa ya yi kyau da yalwar rassa, abin ƙyashi na dukan itatuwan Eden a lambun Allah.
Je l’avais fait beau par la multitude de ses branches, et tous les arbres d’Eden, qui étaient au jardin de Dieu, le jalousaient.
10 “‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa domin ya yi tsayi, kansa kuma ya kai cikin gizagizai, kuma domin ya yi fariya saboda tsayinsa,
Donc, ainsi parle le Seigneur Dieu, puisque tu avais tant monté en hauteur, puisqu’il avait étendu sa cime au milieu des nuages, et que son coeur s’est enorgueilli de sa hauteur,
11 na miƙa shi ga mai mulkin al’ummai, don yă sāka masa gwargwadon muguntarsa. Na jefar da shi a gefe,
j’ai voulu le livrer aux mains d’un puissant parmi les nations, pour qu’il lui infligeât le traitement dû à sa méchanceté: je l’ai répudié.
12 kuma baƙi mafi mugunta na al’ummai suka sare shi suka bar shi. Rassansa sun fāɗi a kan duwatsun da suke cikin dukan kwaruruka; rassansa kuma sun kakkarye, sun fāɗi a cikin dukan magudanan ruwa na ƙasa. Dukan al’umman duniya suka fito daga ƙarƙashin inuwarsa suka bar shi.
Ils l’ont coupé, les étrangers, les plus violents des peuples, ils l’ont jeté là. Sur les montagnes et sur toutes les vallées sont tombées ses branches; ses rameaux se sont brisés dans tous les ravins de la terre. Ils se sont retirés de son ombre, tous les peuples de la terre, et ils l’ont abandonné.
13 Dukan tsuntsaye sararin sama suka zauna a itacen da ya fāɗi, dukan namun jeji kuma suna cikin rassansa.
Sur sa ruine habitent tous les oiseaux du ciel et sur ses rameaux se posent toutes les bêtes des champs,
14 Saboda haka ba wani daga cikin itatuwan da suke kusa da ruwan da zai taɓa yin fariyar tsawonsa, har kawunansu su kai cikin gizagizai. Ba wani daga cikin itatuwan da ya sha ruwa sosai da zai taɓa yi wannan tsayi; duk an bashe su ga mutuwa, zuwa can ƙasa, a cikin matattu, tare da waɗanda suka gangara zuwa rami.
pour qu’aucun des arbres plantés près des eaux ne s’enorgueillisse plus de sa haute taille, et qu’ils ne percent plus les nuages de leur cime et qu’ils ne se dressent plus dans leur hauteur, ces géants, tous ces buveurs d’eau, car tous ont été voués à là mort, précipités dans les régions souterraines, au milieu des fils de l’homme, auprès de ceux qui sont descendus dans la fosse."
15 “‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa a ranar da aka yi ƙasa da shi zuwa kabari na rufe zurfafa maɓulɓulai da makoki dominsa; na janye rafuffukansa, aka kuma hana yalwan ruwansa. Saboda shi na rufe Lebanon da baƙin ciki, dukan itatuwan kurmi suka bushe. (Sheol h7585)
Ainsi parle le Seigneur Dieu: "Le jour où il est descendu dans le Scheol, j’ai fait mener le deuil; à cause de lui j’ai recouvert la source profonde, j’en ai arrêté les fleuves, et les grandes eaux ont été retenues prisonnières; j’ai enténébré pour lui le Liban, et tous les arbres des champs ont été pris de langueur à cause de lui. (Sheol h7585)
16 Na sa al’ummai suka yi rawar jiki da jin ƙarar fāɗuwarsa sa’ad da na yi ƙasa da shi zuwa kabari tare da waɗanda suka gangara rami. Sai dukan itatuwan Eden, zaɓaɓɓu da kuma mafi kyau na Lebanon, dukan itatuwan da aka yi musu banruwa, sun ta’azantu a ƙarƙashin ƙasa. (Sheol h7585)
Au bruit de sa chute, j’ai fait tressaillir les peuples, quand je l’ai fait descendre dans le Scheol avec ceux qui descendent dans la fosse, et ils se sont consolés dans les régions souterraines, tous les arbres de l’Eden, les plus beaux, les meilleurs du Liban, tous les buveurs d’eau. (Sheol h7585)
17 Waɗanda suka zauna a inuwarsa, dukan masu tarayyarsa a cikin al’ummai, su ma sun gangara zuwa kabari tare da shi, sun haɗu da waɗanda aka kashe da takobi. (Sheol h7585)
Eux aussi sont descendus avec lui dans le Scheol auprès des victimes de l’épée; de même ses auxiliaires qui, s’asseyaient à son ombre parmi les nations. (Sheol h7585)
18 “‘Da wa cikin itatuwan Eden za a kwatanta da kai cikin girma da daraja? Duk da haka kai ma, za a yi ƙasa da kai tare da itatuwan Eden zuwa ƙarƙashin ƙasa; za ka kwanta a cikin marasa kaciya, tare da waɗanda aka kashe da takobi. “‘Fir’auna ke nan da dukan jama’arsa, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”
A qui donc pouvais-tu être comparé en gloire et en grandeur parmi les arbres de l’Eden? Et pourtant, tu seras précipité, avec les arbres de l’Eden, dans les régions souterraines, parmi les incirconcis; tu seras couché avec les victimes de l’épée. Voilà ce qu’est Pharaon avec toute sa cohue, dit le Seigneur Dieu."

< Ezekiyel 31 >