< Ezekiyel 30 >

1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
La parole de l'Eternel me fut encore [adressée], en disant:
2 “Ɗan mutum, ka yi annabci ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Yi kuka kana cewa, “Kaito saboda wannan rana!”
Fils d'homme, prophétise, et dis: ainsi a dit le Seigneur l'Eternel: hurlez, [et dites]: ah quelle journée!
3 Gama ranar ta yi kusa, ranar Ubangiji ta gabato, ranar gizagizai, lokacin hallaka wa al’ummai.
Car la journée [est] proche, oui la journée de l'Eternel est proche, c'est une journée de nuage; ce sera le temps des nations.
4 Takobi zai zo a kan Masar, azaba za tă zo a kan Kush. Sa’ad da kisassu za su fāɗi a Masar, za a kwashe dukiyarta a tafi a rushe harsashinta.
L'épée viendra sur l'Egypte, et il y aura de l'effroi en Cus, quand ceux qui seront blessés à mort tomberont dans l'Egypte, et quand on enlèvera la multitude de son peuple, et que ses fondements seront ruinés.
5 Kush da Fut, Lidiya da dukan Arabiya, Libiya da kuma mutanen ƙasar alkawari za su mutu ta wurin takobi tare da Masar.
Cus, et Put, et Lud, et tout le mélange [d'Arabie], et Cub, et les enfants du pays allié tomberont par l'épée avec eux.
6 “‘Ga abin da Ubangiji ya faɗa, “‘Waɗanda suke goyon bayan Masar za su fāɗi ƙarfinta da take fariya da shi zai ƙare. Daga Migdol zuwa Aswan za su mutu ta wurin takobi a cikinta, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
Ainsi a dit l'Eternel: ceux qui soutiendront l'Egypte, tomberont; et l'orgueil de sa force sera renversé; ils tomberont en elle par l'épée depuis la tour de Syène, dit le Seigneur l'Eternel.
7 Za su zama kango a cikin ƙasashen da suke kango, biranensu kuwa za su zama kufai a cikin biranen da suka lalace.
Et ils seront désolés au milieu des pays désolés, et ses villes seront au milieu des villes rendues désertes.
8 Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji, sa’ad da suka ga na sa wuta wa Masar aka kuma ragargaza masu taimakonta.
Et ils sauront que je suis l'Eternel, quand j'aurai mis le feu en Egypte; et tous ceux qui lui donneront du secours, seront brisés.
9 “‘A wannan rana manzanni za su fito daga wurina a jiragen ruwa don su tsorata Kush daga sake jikinta. Azaba za tă kama su a ranar hallakar Masar, gama tabbatacce za tă zo.
En ce jour-là des messagers sortiront de ma part dans des navires pour effrayer Cus l'assurée, et il y aura entre eux un tourment tel qu'à la journée d'Egypte; car voici, il vient.
10 “‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Zan kawo ƙarshen mutanen Masar ta hannun Nebukadnezzar sarkin Babilon.
Ainsi a dit le Seigneur l'Eternel: je ferai périr la multitude d'Egypte par la puissance de Nébucadnetsar, Roi de Babylone.
11 Shi da sojojinsa, mafi bantsoro cikin al’ummai, za a kawo don su hallaka ƙasar. Za su zāre takuba a kan Masar su kuma cika ƙasar da kisassu.
Lui et son peuple avec lui, les plus terribles d'entre les nations, seront amenés pour ruiner le pays, et ils tireront leurs épées contre les Egyptiens, et rempliront la terre de morts.
12 Zan kafe rafuffukan Nilu in sayar da ƙasar ga mugayen mutane; ta hannun baƙi zan sa ƙasar ta lalace da kome da yake cikinta. Ni Ubangiji na faɗa.
Et je mettrai à sec les bras [d'eau], et je livrerai le pays entre les mains de gens méchants, je désolerai le pays, et tout ce qui y est, par la puissance des étrangers; moi l'Eternel j'ai parlé.
13 “‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Zan hallaka gumaka in kuma kawo ƙarshen siffofi a Memfis. Ba za a ƙara samun yerima a ƙasar Masar ba, zan kuma baza tsoro a duk fāɗin ƙasar.
Ainsi a dit le Seigneur l'Eternel: je détruirai aussi les idoles, j'anéantirai les faux dieux de Noph, et il n'y aura point de Prince qui soit du pays d'Egypte; et je mettrai la frayeur dans le pays d'Egypte.
14 Zan lalace Masar ta Bisa in ƙuna wuta wa Zowan in zartar da hukunci a kan Tebes.
Je désolerai Pathros, je mettrai le feu à Tsohan, et j'exercerai des jugements dans No.
15 Zan kwarara hasalata a kan Felusiyum, kagarar Masar, in kuma datse mutanen Tebes.
Et je répandrai ma fureur sur Sin, qui est la force d'Egypte, et j'exterminerai la multitude qui est à No.
16 Zan ƙuna wuta wa Masar; Felusiyum za tă sha azaba mai zafi. Za a tayar wa Tebes da hankali; Memfis za tă riƙa kasance cikin ɓacin rai.
Quand je mettrai le feu en Egypte, Sin sera grièvement tourmentée, et No sera rompue par diverses brèches, et il n'y aura à Noph que détresses en plein jour.
17 Samarin Heliyofolis da Bubastis za su mutu ta wurin takobi, biranen kansu za su tafi bauta.
Les jeunes gens d'élite d'Aven et de Pibeseth tomberont par l'épée, et elles iront en captivité.
18 Duhu ne zai zama rana a Tafanes sa’ad da na karye ikon Masar; a can ƙarfin da take fariya zai ƙare. Za a rufe ta da gizagizai ƙauyukanta kuma za su tafi bauta.
Et le jour défaudra dans Taphnès, lorsque j'y romprai les barres d'Egypte, et que l'orgueil de sa force aura cessé; une nuée la couvrira, et les villes de son ressort iront en captivité.
19 Ta haka zan zartar da hukunci a kan Masar, za su kuwa san cewa ni ne Ubangiji.’”
Et j'exercerai des jugements en Egypte; et ils sauront que je suis l'Eternel.
20 A shekara ta goma sha ɗaya, a wata na fari a rana ta goma sha bakwai, maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Or il était arrivé en la onzième année, au septième jour du premier mois, que la parole de l'Eternel m'avait été adressée, en disant:
21 “Ɗan mutum, na karye hannun Fir’auna sarkin Masar. Ba a daure shi don warkarwa ba ko a sa tsinke saboda kada yă zama da ƙarfi har ya riƙe takobi.
Fils d'homme, j'ai rompu le bras de Pharaon Roi d'Egypte; et voici on ne l'a point bandé pour le guérir, en sorte qu'on lui ait mis des linges pour le bander, [et] pour le fortifier, afin qu'il pût empoigner l'épée.
22 Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gāba da Fir’auna sarkin Masar. Zan karye hannuwansa biyu, hannun da yake da kyau da kuma wanda an riga an karya, in kuma sa takobi ya fāɗi daga hannunsa.
C'est pourquoi ainsi a dit le Seigneur l'Eternel: voici, j'en veux à Pharaon Roi d'Egypte, et je romprai ses bras, tant celui qui est fort, que celui qui est rompu, et je ferai tomber l'épée de sa main.
23 Zan watsar da Masarawa a cikin al’ummai in warwatsa su cikin ƙasashe.
Et je disperserai les Egyptiens parmi les nations, et les répandrai parmi les pays.
24 Zan ƙarfafa hannuwan sarkin Babilon in kuma sa takobina a hannunsa, amma zan karya hannuwan Fir’auna, zai kuwa yi nishi a gabansa kamar mutumin da aka yi wa raunin mutuwa.
Et je fortifierai les bras du Roi de Babylone, et je lui mettrai mon épée en la main; mais je romprai les bras de Pharaon, et [Pharaon] jettera des sanglots devant lui, comme des gens blessés à mort.
25 Zan ƙarfafa hannuwan sarkin Babilon, amma hannuwan Fir’auna za su shanye. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji, sa’ad da na sa takobi a hannun sarkin Babilon na kuma miƙa shi a kan Masar.
Je fortifierai donc les bras du Roi de Babylone, mais les bras de Pharaon tomberont; et on saura que je suis l'Eternel, quand j'aurai mis mon épée en la main du Roi de Babylone, et qu'il l'aura étendue sur le pays d'Egypte.
26 Zan watsar da Masarawa a cikin al’ummai in warwatsa su cikin ƙasashe. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji.”
Et je disperserai les Egyptiens parmi les nations, et les répandrai parmi les pays; et ils sauront que je suis l'Eternel.

< Ezekiyel 30 >