< Ezekiyel 30 >
1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
And the word of the Lord was maad to me,
2 “Ɗan mutum, ka yi annabci ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Yi kuka kana cewa, “Kaito saboda wannan rana!”
and he seide, Sone of man, profesie thou, and seie, The Lord God seith these thingis, Yelle ye, Wo!
3 Gama ranar ta yi kusa, ranar Ubangiji ta gabato, ranar gizagizai, lokacin hallaka wa al’ummai.
wo! to the dai, for the dai is niy; and the dai of the Lord neiyith, the dai of a cloude. The tyme of hethene men schal be;
4 Takobi zai zo a kan Masar, azaba za tă zo a kan Kush. Sa’ad da kisassu za su fāɗi a Masar, za a kwashe dukiyarta a tafi a rushe harsashinta.
and a swerd schal come in to Egipt, and drede schal be in Ethiopie, whanne woundid men schulen falle doun in Egipt, and the multitude therof schal be takun awei, and the foundementis therof schulen be distried.
5 Kush da Fut, Lidiya da dukan Arabiya, Libiya da kuma mutanen ƙasar alkawari za su mutu ta wurin takobi tare da Masar.
Ethiopie, and Libie, and Lidiens, and al the residue comyn puple, and Chub, and the sones of the lond of boond of pees schulen falle doun bi swerd with hem.
6 “‘Ga abin da Ubangiji ya faɗa, “‘Waɗanda suke goyon bayan Masar za su fāɗi ƙarfinta da take fariya da shi zai ƙare. Daga Migdol zuwa Aswan za su mutu ta wurin takobi a cikinta, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
The Lord God seith these thingis, And thei that vndursetten Egipt schulen falle doun, and the pride of the lordschipe therof schal be destried; fro the tour of Sienes thei schulen falle bi swerd ther ynne, seith the Lord of oostis.
7 Za su zama kango a cikin ƙasashen da suke kango, biranensu kuwa za su zama kufai a cikin biranen da suka lalace.
And thei schulen be distried in the myddis of londis maad desolat, and the citees therof schulen be in the myddis of citees forsakun.
8 Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji, sa’ad da suka ga na sa wuta wa Masar aka kuma ragargaza masu taimakonta.
And thei schulen wite, that Y am the Lord God, whanne Y schal yyue fier in Egipt, and alle the helperis therof schulen be al to-brokun.
9 “‘A wannan rana manzanni za su fito daga wurina a jiragen ruwa don su tsorata Kush daga sake jikinta. Azaba za tă kama su a ranar hallakar Masar, gama tabbatacce za tă zo.
In that dai messangeris schulen go out fro my face in schippis with thre ordris of ooris, to al to-breke the trist of Ethiopie; and drede schal be in hem in the dai of Egipt, for with out doute it schal come.
10 “‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Zan kawo ƙarshen mutanen Masar ta hannun Nebukadnezzar sarkin Babilon.
The Lord God seith these thingis, And I schal make to ceesse the multitude of Egipt in the hond of Nabugodonosor, king of Babiloyne.
11 Shi da sojojinsa, mafi bantsoro cikin al’ummai, za a kawo don su hallaka ƙasar. Za su zāre takuba a kan Masar su kuma cika ƙasar da kisassu.
He and his puple with hym, the strongeste men of hethene men, schulen be brouyt, to leese the lond; and thei schulen drawe out her swerdis on Egipt, and thei schulen fille the lond with slayn men.
12 Zan kafe rafuffukan Nilu in sayar da ƙasar ga mugayen mutane; ta hannun baƙi zan sa ƙasar ta lalace da kome da yake cikinta. Ni Ubangiji na faɗa.
And Y schal make drie the botmes of floodis, and Y schal yyue the lond in the hond of the worste men; and I schal distrie the lond, and the fulnesse therof in the hond of aliens; Y the Lord spak.
13 “‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Zan hallaka gumaka in kuma kawo ƙarshen siffofi a Memfis. Ba za a ƙara samun yerima a ƙasar Masar ba, zan kuma baza tsoro a duk fāɗin ƙasar.
The Lord God seith these thingis, And Y schal leese simylacris, and Y schal make idols to ceesse fro Memphis, and a duyk of the lond of Egipt schal no more be. And Y schal yyue drede in the lond of Egipt,
14 Zan lalace Masar ta Bisa in ƙuna wuta wa Zowan in zartar da hukunci a kan Tebes.
and Y schal leese the lond of Phatures. And Y schal yyue fier in Tafnys, and Y schal make my domes in Alisaundre.
15 Zan kwarara hasalata a kan Felusiyum, kagarar Masar, in kuma datse mutanen Tebes.
And Y schal schede out myn indignacioun on Pelusyum, the strengthe of Egipt; and Y schal sle the multitude of Alisaundre,
16 Zan ƙuna wuta wa Masar; Felusiyum za tă sha azaba mai zafi. Za a tayar wa Tebes da hankali; Memfis za tă riƙa kasance cikin ɓacin rai.
and Y schal yyue fier in Egipt. Pelusyum, as a womman trauelynge of child, schal haue sorewe, and Alisaundre schal be destried, and in Memphis schulen be ech daies angwischis.
17 Samarin Heliyofolis da Bubastis za su mutu ta wurin takobi, biranen kansu za su tafi bauta.
The yonge men of Heliopoleos and of Bubasti schulen falle doun bi swerd, and tho citees schulen be led caitifs.
18 Duhu ne zai zama rana a Tafanes sa’ad da na karye ikon Masar; a can ƙarfin da take fariya zai ƙare. Za a rufe ta da gizagizai ƙauyukanta kuma za su tafi bauta.
And in Thafnys the dai schal wexe blak, whanne Y schal al to-breke there the ceptris of Egipt, and the pride of the power therof schal faile there ynne. A cloude schal hile it; forsothe the douytris therof schulen be led in to caitifte, and Y schal make domes in Egipt;
19 Ta haka zan zartar da hukunci a kan Masar, za su kuwa san cewa ni ne Ubangiji.’”
and thei schulen wite, that Y am the Lord.
20 A shekara ta goma sha ɗaya, a wata na fari a rana ta goma sha bakwai, maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
And it was doon in the enleuenthe yeer, in the firste monethe, in the seuenthe dai of the moneth, the word of the Lord was maad to me,
21 “Ɗan mutum, na karye hannun Fir’auna sarkin Masar. Ba a daure shi don warkarwa ba ko a sa tsinke saboda kada yă zama da ƙarfi har ya riƙe takobi.
and he seide, Thou sone of man, Y haue broke the arm of Farao, kyng of Egipt; and lo! it is not wlappid, that helthe schulde be restorid therto, that it schulde be boundun with clothis, and woundun with lynnun clothis, and that he myyte holde swerd, whanne he hadde resseyued strengthe.
22 Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gāba da Fir’auna sarkin Masar. Zan karye hannuwansa biyu, hannun da yake da kyau da kuma wanda an riga an karya, in kuma sa takobi ya fāɗi daga hannunsa.
Therfor the Lord God seith these thingis, Lo! Y to Farao, king of Egipt; and Y schal make lesse his strong arm but brokun, and Y schal caste doun the swerd fro his hond.
23 Zan watsar da Masarawa a cikin al’ummai in warwatsa su cikin ƙasashe.
And Y schal scatere Egipt among hethene men, and Y schal wyndewe hem in londis.
24 Zan ƙarfafa hannuwan sarkin Babilon in kuma sa takobina a hannunsa, amma zan karya hannuwan Fir’auna, zai kuwa yi nishi a gabansa kamar mutumin da aka yi wa raunin mutuwa.
And Y schal coumforte the armes of the kyng of Babiloyne, and Y schal yyue my swerd in the hond of hym; and Y schal breke the armes of Farao, and men slayn bifore his face schulen weile bi weilyngis.
25 Zan ƙarfafa hannuwan sarkin Babilon, amma hannuwan Fir’auna za su shanye. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji, sa’ad da na sa takobi a hannun sarkin Babilon na kuma miƙa shi a kan Masar.
And Y schal coumforte the armes of the kyng of Babiloyne, and the armes of Farao schulen falle doun. And thei schulen wite, that Y am the Lord, whanne Y schal yyue my swerd in the hond of the kyng of Babiloyne; and he schal stretche forth it on the lond of Egipt.
26 Zan watsar da Masarawa a cikin al’ummai in warwatsa su cikin ƙasashe. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji.”
And Y schal scatere Egipt in to naciouns, and Y schal wyndewe hem in to londis; and thei schulen wite, that Y am the Lord.