< Ezekiyel 30 >

1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
The word of Jehovah came again to me, saying:
2 “Ɗan mutum, ka yi annabci ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Yi kuka kana cewa, “Kaito saboda wannan rana!”
Son of man, prophesy, and say, Thus saith the Lord Jehovah: Howl ye, Alas! alas for the day!
3 Gama ranar ta yi kusa, ranar Ubangiji ta gabato, ranar gizagizai, lokacin hallaka wa al’ummai.
For the day is near, the day of Jehovah is near! A day of clouds, the time of the nations is come.
4 Takobi zai zo a kan Masar, azaba za tă zo a kan Kush. Sa’ad da kisassu za su fāɗi a Masar, za a kwashe dukiyarta a tafi a rushe harsashinta.
The sword shall come upon Egypt, and anguish shall be in Ethiopia, when the slain shall fall in Egypt, and they shall take away her multitude, and her foundations shall be destroyed.
5 Kush da Fut, Lidiya da dukan Arabiya, Libiya da kuma mutanen ƙasar alkawari za su mutu ta wurin takobi tare da Masar.
Ethiopia, and Lybia, and Lydia, and all her auxiliaries, and Chub, and the men of every country that is in league, shall fall with them by the sword.
6 “‘Ga abin da Ubangiji ya faɗa, “‘Waɗanda suke goyon bayan Masar za su fāɗi ƙarfinta da take fariya da shi zai ƙare. Daga Migdol zuwa Aswan za su mutu ta wurin takobi a cikinta, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
Thus saith Jehovah: They that uphold Egypt shall fall, and the pride of her power shall come down; from Migdol to Syene shall they fall in her by the sword, saith the Lord Jehovah.
7 Za su zama kango a cikin ƙasashen da suke kango, biranensu kuwa za su zama kufai a cikin biranen da suka lalace.
And they shall be laid waste in the midst of the lands that are laid waste, and her cities shall be amongst the cities that are desolate.
8 Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji, sa’ad da suka ga na sa wuta wa Masar aka kuma ragargaza masu taimakonta.
And they shall know that I am Jehovah, when I have brought a fire into Egypt, and all her helpers shall be destroyed.
9 “‘A wannan rana manzanni za su fito daga wurina a jiragen ruwa don su tsorata Kush daga sake jikinta. Azaba za tă kama su a ranar hallakar Masar, gama tabbatacce za tă zo.
In that day shall messengers go forth from me in ships, to make the confident Ethiopians afraid; and anguish shall come upon them, as in the day of Egypt; for behold, it cometh!
10 “‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Zan kawo ƙarshen mutanen Masar ta hannun Nebukadnezzar sarkin Babilon.
Thus saith the Lord Jehovah: I will make the multitude of Egypt to cease by the hand of Nebuchadnezzar, the king of Babylon.
11 Shi da sojojinsa, mafi bantsoro cikin al’ummai, za a kawo don su hallaka ƙasar. Za su zāre takuba a kan Masar su kuma cika ƙasar da kisassu.
He and his people with him, the terrible of the nations, shall be brought to make the land desolate; and they shall draw their swords against Egypt, and fill the land with the slain.
12 Zan kafe rafuffukan Nilu in sayar da ƙasar ga mugayen mutane; ta hannun baƙi zan sa ƙasar ta lalace da kome da yake cikinta. Ni Ubangiji na faɗa.
And I will make the rivers dry, and I will sell the land into the hand of evil men; and I will lay waste the land and all that is therein, by the hand of strangers; I, Jehovah, have spoken it.
13 “‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Zan hallaka gumaka in kuma kawo ƙarshen siffofi a Memfis. Ba za a ƙara samun yerima a ƙasar Masar ba, zan kuma baza tsoro a duk fāɗin ƙasar.
Thus saith the Lord Jehovah: I will destroy the idols, and cause the images to cease out of Noph; and there shall be no more a prince of the land of Egypt; and I will bring fear upon the land of Egypt:
14 Zan lalace Masar ta Bisa in ƙuna wuta wa Zowan in zartar da hukunci a kan Tebes.
And I will lay waste Pathros, and bring a fire upon Zoan, and execute judgments upon No.
15 Zan kwarara hasalata a kan Felusiyum, kagarar Masar, in kuma datse mutanen Tebes.
And I will pour out my fury upon Sin, the strength of Egypt, and I will cut off the multitude of No.
16 Zan ƙuna wuta wa Masar; Felusiyum za tă sha azaba mai zafi. Za a tayar wa Tebes da hankali; Memfis za tă riƙa kasance cikin ɓacin rai.
And I will bring a fire upon Egypt; Sin shall tremble, and No shall be broken through, and Noph shall be plundered by day.
17 Samarin Heliyofolis da Bubastis za su mutu ta wurin takobi, biranen kansu za su tafi bauta.
The young men of On and of Pibeseth shall fall by the sword, and the women shall go into captivity.
18 Duhu ne zai zama rana a Tafanes sa’ad da na karye ikon Masar; a can ƙarfin da take fariya zai ƙare. Za a rufe ta da gizagizai ƙauyukanta kuma za su tafi bauta.
At Tahpanhes also the day shall be darkened, when I shall break there the yoke of Egypt, and the pride of her strength shall cease within her. A cloud shall cover her, and her daughters shall go into captivity.
19 Ta haka zan zartar da hukunci a kan Masar, za su kuwa san cewa ni ne Ubangiji.’”
Thus will I execute judgments upon Egypt; and they shall know that I am Jehovah.
20 A shekara ta goma sha ɗaya, a wata na fari a rana ta goma sha bakwai, maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Now it came to pass in the eleventh year, in the first month, on the seventh day of the month, that the word of Jehovah came to me, saying:
21 “Ɗan mutum, na karye hannun Fir’auna sarkin Masar. Ba a daure shi don warkarwa ba ko a sa tsinke saboda kada yă zama da ƙarfi har ya riƙe takobi.
Son of man, I have broken the arm of Pharaoh, king of Egypt, and lo, it is not bound up, so as to have medicines applied to it; a bandage is not applied to it, to make it strong to hold the sword.
22 Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gāba da Fir’auna sarkin Masar. Zan karye hannuwansa biyu, hannun da yake da kyau da kuma wanda an riga an karya, in kuma sa takobi ya fāɗi daga hannunsa.
Therefore thus saith the Lord Jehovah: Behold, I am against Pharaoh, the king of Egypt; and I will break his arms, both the strong one, and that which was broken, and I will cause the sword to fall out of his hand.
23 Zan watsar da Masarawa a cikin al’ummai in warwatsa su cikin ƙasashe.
And I will scatter the Egyptians among the nations, and disperse them through the countries.
24 Zan ƙarfafa hannuwan sarkin Babilon in kuma sa takobina a hannunsa, amma zan karya hannuwan Fir’auna, zai kuwa yi nishi a gabansa kamar mutumin da aka yi wa raunin mutuwa.
But I will strengthen the arms of the king of Babylon, and will put my sword into his hand, and break the arms of Pharaoh, so that he shall groan before him with the groanings of a deadly wounded man.
25 Zan ƙarfafa hannuwan sarkin Babilon, amma hannuwan Fir’auna za su shanye. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji, sa’ad da na sa takobi a hannun sarkin Babilon na kuma miƙa shi a kan Masar.
Yea, I will strengthen the arms of the king of Babylon, and the arms of Pharaoh shall fall down; and they shall know that I am Jehovah, when I shall put my sword into the hand of the king of Babylon, and he shall stretch it out upon the land of Egypt.
26 Zan watsar da Masarawa a cikin al’ummai in warwatsa su cikin ƙasashe. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji.”
And I will scatter the Egyptians among the nations, and disperse them among the countries, and they shall know that I am Jehovah.

< Ezekiyel 30 >