< Ezekiyel 30 >

1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
And the word of the LORD came unto me, saying:
2 “Ɗan mutum, ka yi annabci ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Yi kuka kana cewa, “Kaito saboda wannan rana!”
'Son of man, prophesy, and say: Thus saith the Lord GOD: Wail ye: Woe worth the day!
3 Gama ranar ta yi kusa, ranar Ubangiji ta gabato, ranar gizagizai, lokacin hallaka wa al’ummai.
For the day is near, even the day of the LORD is near, a day of clouds, it shall be the time of the nations.
4 Takobi zai zo a kan Masar, azaba za tă zo a kan Kush. Sa’ad da kisassu za su fāɗi a Masar, za a kwashe dukiyarta a tafi a rushe harsashinta.
And a sword shall come upon Egypt, and convulsion shall be in Ethiopia, when the slain shall fall in Egypt; and they shall take away her abundance, and her foundation shall be broken down.
5 Kush da Fut, Lidiya da dukan Arabiya, Libiya da kuma mutanen ƙasar alkawari za su mutu ta wurin takobi tare da Masar.
Ethiopia, and Put, and Lud, and all the mingled people, and Cub, and the children of the land that is in league, shall fall with them by the sword.
6 “‘Ga abin da Ubangiji ya faɗa, “‘Waɗanda suke goyon bayan Masar za su fāɗi ƙarfinta da take fariya da shi zai ƙare. Daga Migdol zuwa Aswan za su mutu ta wurin takobi a cikinta, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
Thus saith the LORD: They also that uphold Egypt shall fall, and the pride of her power shall come down; from Migdol to Syene shall they fall in it by the sword, saith the Lord GOD.
7 Za su zama kango a cikin ƙasashen da suke kango, biranensu kuwa za su zama kufai a cikin biranen da suka lalace.
And they shall be desolate in the midst of the countries that are desolate, and her cities shall be in the midst of the cities that are wasted.
8 Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji, sa’ad da suka ga na sa wuta wa Masar aka kuma ragargaza masu taimakonta.
And they shall know that I am the LORD, when I have set a fire in Egypt, and all her helpers are destroyed.
9 “‘A wannan rana manzanni za su fito daga wurina a jiragen ruwa don su tsorata Kush daga sake jikinta. Azaba za tă kama su a ranar hallakar Masar, gama tabbatacce za tă zo.
In that day shall messengers go forth from before Me in ships to make the confident Ethiopians afraid; and there shall come convulsion upon them in the day of Egypt; for, lo, it cometh.
10 “‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Zan kawo ƙarshen mutanen Masar ta hannun Nebukadnezzar sarkin Babilon.
Thus saith the Lord GOD: I will also make the multitude of Egypt to cease, by the hand of Nebuchadrezzar king of Babylon.
11 Shi da sojojinsa, mafi bantsoro cikin al’ummai, za a kawo don su hallaka ƙasar. Za su zāre takuba a kan Masar su kuma cika ƙasar da kisassu.
He and his people with him, the terrible of the nations, shall be brought in to destroy the land; and they shall draw their swords against Egypt, and fill the land with the slain.
12 Zan kafe rafuffukan Nilu in sayar da ƙasar ga mugayen mutane; ta hannun baƙi zan sa ƙasar ta lalace da kome da yake cikinta. Ni Ubangiji na faɗa.
And I will make the rivers dry, and will give the land over into the hand of evil men; and I will make the land desolate, and all that is therein, by the hand of strangers; I the LORD have spoken it.
13 “‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Zan hallaka gumaka in kuma kawo ƙarshen siffofi a Memfis. Ba za a ƙara samun yerima a ƙasar Masar ba, zan kuma baza tsoro a duk fāɗin ƙasar.
Thus saith the Lord GOD: I will also destroy the idols, and I will cause the things of nought to cease from Noph; and there shall be no more a prince out of the land of Egypt; and I will put a fear in the land of Egypt.
14 Zan lalace Masar ta Bisa in ƙuna wuta wa Zowan in zartar da hukunci a kan Tebes.
And I will make Pathros desolate, and will set a fire in Zoan, and will execute judgments in No.
15 Zan kwarara hasalata a kan Felusiyum, kagarar Masar, in kuma datse mutanen Tebes.
And I will pour My fury upon Sin, the stronghold of Egypt; and I will cut off the multitude of No.
16 Zan ƙuna wuta wa Masar; Felusiyum za tă sha azaba mai zafi. Za a tayar wa Tebes da hankali; Memfis za tă riƙa kasance cikin ɓacin rai.
And I will set a fire in Egypt; Sin shall be in great convulsion, and No shall be rent asunder; and in Noph shall come adversaries in the day-time.
17 Samarin Heliyofolis da Bubastis za su mutu ta wurin takobi, biranen kansu za su tafi bauta.
The young men of Aven and of Pi-beseth shall fall by the sword; and these cities shall go into captivity.
18 Duhu ne zai zama rana a Tafanes sa’ad da na karye ikon Masar; a can ƙarfin da take fariya zai ƙare. Za a rufe ta da gizagizai ƙauyukanta kuma za su tafi bauta.
At Tehaphnehes also the day shall withdraw itself, when I shall break there the yokes of Egypt, and the pride of her power shall cease in her; as for her, a cloud shall cover her, and her daughters shall go into captivity.
19 Ta haka zan zartar da hukunci a kan Masar, za su kuwa san cewa ni ne Ubangiji.’”
Thus will I execute judgments in Egypt; and they shall know that I am the LORD.'
20 A shekara ta goma sha ɗaya, a wata na fari a rana ta goma sha bakwai, maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
And it came to pass in the eleventh year, in the first month, in the seventh day of the month, that the word of the LORD came unto me, saying:
21 “Ɗan mutum, na karye hannun Fir’auna sarkin Masar. Ba a daure shi don warkarwa ba ko a sa tsinke saboda kada yă zama da ƙarfi har ya riƙe takobi.
'Son of man, I have broken the arm of Pharaoh king of Egypt; and, lo, it hath not been bound up to be healed, to put a roller, that it be bound up and wax strong, that it hold the sword.
22 Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gāba da Fir’auna sarkin Masar. Zan karye hannuwansa biyu, hannun da yake da kyau da kuma wanda an riga an karya, in kuma sa takobi ya fāɗi daga hannunsa.
Therefore thus saith the Lord GOD: Behold, I am against Pharaoh king of Egypt, and will break his arms, the strong, and that which was broken; and I will cause the sword to fall out of his hand.
23 Zan watsar da Masarawa a cikin al’ummai in warwatsa su cikin ƙasashe.
And I will scatter the Egyptians among the nations, and will disperse them through the countries.
24 Zan ƙarfafa hannuwan sarkin Babilon in kuma sa takobina a hannunsa, amma zan karya hannuwan Fir’auna, zai kuwa yi nishi a gabansa kamar mutumin da aka yi wa raunin mutuwa.
And I will strengthen the arms of the king of Babylon, and put My sword in his hand; but I will break the arms of Pharaoh, and he shall groan before him with the groanings of a deadly wounded man.
25 Zan ƙarfafa hannuwan sarkin Babilon, amma hannuwan Fir’auna za su shanye. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji, sa’ad da na sa takobi a hannun sarkin Babilon na kuma miƙa shi a kan Masar.
And I will hold up the arms of the king of Babylon, and the arms of Pharaoh shall fall down; and they shall know that I am the LORD, when I shall put My sword into the hand of the king of Babylon, and he shall stretch it out upon the land of Egypt.
26 Zan watsar da Masarawa a cikin al’ummai in warwatsa su cikin ƙasashe. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji.”
And I will scatter the Egyptians among the nations, and disperse them through the countries; and they shall know that I am the LORD.'

< Ezekiyel 30 >