< Ezekiyel 3 >

1 Ya kuma ce mini, “Ɗan mutum, ka ci abin da yake a gabanka, ka ci wannan littafi; sa’an nan ka tafi ka yi magana wa gidan Isra’ila.”
Puis il me dit: fils d'homme, mange ce que tu trouveras, mange ce rouleau, et t'en va, [et] parle à la maison d'Israël.
2 Saboda haka na buɗe bakina, ya kuma ba ni littafin in ci.
J'ouvris donc ma bouche, et il me fit manger ce rouleau.
3 Sai ya ce mini, “Ɗan mutum, ka ci wannan littafin da nake ba ka, ka kuma cika cikinka da shi.” Sai na ci shi, ya kuma yi zaki kamar zuma a bakina.
Et il me dit: fils d'homme, repais ton ventre, et remplis tes entrailles de ce rouleau que je te donne; et je le mangeai, et il fut doux dans ma bouche comme du miel.
4 Sa’an nan ya ce mini, “Ɗan mutum, yanzu ka tafi gidan Isra’ila ka faɗa kalmomina gare su.
Puis il me dit: fils d'homme, lève-toi et va vers la maison d'Israël, et leur prononce mes paroles.
5 Ba ina aikan ka wurin mutanen da suke da baƙon harshe da kuma yare mai wuya ba ne, amma zuwa ga gidan Isra’ila ne,
[Car] tu n'es point envoyé vers un peuple de langage inconnu, ou de langue barbare; c'est vers la maison d'Israël;
6 ba ga mutane da yawa na baƙon harshe da yare mai wuya, waɗanda ba ka san kalmominsu ba. Tabbatacce da na aike ka wurin irinsu, da sun saurare ka.
Ni vers plusieurs peuples de langage inconnu, ou de langue barbare, dont tu ne puisses pas entendre les paroles; si je t'eusse envoyé vers eux, ne t'écouteraient-ils pas?
7 Amma gidan Isra’ila ba sa niyya su saurare ka domin ba sa niyya su saurare ni, gama dukan gidan Isra’ila sun taurare suna kuma kin ji.
Mais la maison d'Israël ne te voudra pas écouter, parce qu'ils ne me veulent point écouter; car toute la maison d'Israël est effrontée, et d'un cœur obstiné.
8 Amma zan sa ka zama mai taurinkai da taurin zuciya kamar su.
Voici, j'ai renforcé ta face contre leurs faces, et j'ai renforcé ton front contre leurs fronts.
9 Zan sa goshinka ya zama da tauri kamar dutse, da tauri fiye da dutsen ƙanƙara ƙarfi. Kada ka ji tsoronsu ko ka firgita ta wurinsu, ko da yake su gidan’yan tawaye ne.”
Et j'ai rendu ton front semblable à un diamant, [et] plus fort qu'un caillou; ne les crains donc point, et ne t'effraie point à cause d'eux, quoiqu'ils soient une maison rebelle.
10 Ya kuma ce mini, “Ɗan mutum, ka ji da kyau ka kuma lura da dukan kalmomin da nake maka magana.
Puis il me dit: fils d'homme, reçois dans ton cœur, et écoute de tes oreilles toutes les paroles que je te dirai.
11 Ka tafi yanzu zuwa ga’yan’uwanka waɗanda suke zaman bauta ka yi musu magana. Ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa,’ ko ku ji, ko kada ku ji.”
Lève-toi donc, va vers ceux qui ont été emmenés captifs, va vers les enfants de ton peuple, parle-leur, et leur dis que le Seigneur l'Eternel a ainsi parlé, soit qu'ils écoutent, ou qu'ils n'en fassent rien.
12 Sa’an nan Ruhu ya ɗaga ni sama, a bayana na ji wata karar babban motsi na cewa, Bari a yabi ɗaukakar Ubangiji a wurin zamansa!
Puis l'Esprit m'éleva, et j'ouïs après moi une voix [qui me causa] une grande émotion, [disant]: Bénie soit de son lieu la gloire de l'Eternel.
13 Karar fikafikan rayayyun halittun nan ne suke goge junansu da kuma karar da’irorin nan da suke kusa da su, ƙarar babban motsi.
Et j'ouïs le bruit des ailes des animaux, qui s'entre-touchaient les unes les autres, et le bruit des roues vis-à-vis d'eux, [j'ouïs], dis-je, une voix qui me causa une grande émotion.
14 Sa’an nan Ruhu ya ɗaga ni sama ya kuma tafi da ni, na kuwa tafi da ɓacin rai da kuma fushin ruhuna, tare da hannu mai ƙarfi na Ubangiji a bisa na.
L'Esprit donc m'éleva, et me ravit, et je m'en allai l'esprit rempli d'amertume et de colère mais la main de l'Eternel me fortifia.
15 Na zo wurin masu zaman bautan da suke zama a Tel Abib kusa da Kogin Kebar, A can kuwa, inda suke zama, na zauna a cikinsu kwana bakwai, ina mamaki.
Je vins donc vers ceux qui avaient été transportés à Télabib, vers ceux qui demeuraient auprès du fleuve de Kébar; et je me tins là où ils se tenaient, même je me tins là parmi eux sept jours, tout étonné.
16 A ƙarshen kwana bakwai ɗin maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Et au bout de sept jours, la parole de l'Eternel me fut [adressée], en disant:
17 “Ɗan mutum, na mai da kai mai tsaro don gidan Isra’ila; saboda haka ka ji maganar da zan yi ka kuma yi musu kashedin nan da ya fito daga gare ni.
Fils d'homme, je t'ai établi pour surveillant à la maison d'Israël; tu écouteras donc la parole de ma bouche, et tu les avertiras de ma part.
18 In na ce wa mugu, ‘Lalle za ka mutu,’ ba ka kuwa yi masa kashedi ko ka tsawata masa a kan mugayen hanyoyinsa don yă ceci ransa ba, wannan mugun zai mutu saboda zunubinsa, zan kuwa nemi hakkin jininsa a hannunka.
Quand j'aurai dit au méchant: tu mourras de mort, et que tu ne l'auras point averti, et que tu ne lui auras point parlé pour l'avertir de se garder de son méchant train, afin de lui sauver la vie; ce méchant-là mourra dans son iniquité, mais je redemanderai son sang de ta main.
19 Amma in ka yi wa mugun kashedi bai kuwa juya daga mugayen hanyoyinsa ba, zai mutu saboda zunubinsa; amma kai kam za ka kuɓuta.
Que si tu as averti le méchant, et qu'il ne se soit point détourné de sa méchanceté, ni de son méchant train; il mourra dans son iniquité, mais tu auras délivré ton âme.
20 “Har yanzu, in mai adalci ya juya daga adalcinsa ya aikata mugunta, na kuma sa abin tuntuɓe a gabansa, zai mutu. Da yake ba ka yi masa kashedi ba, zai mutu saboda zunubinsa. Ba za a tuna da abin adalcin da ya yi ba, zan kuwa nemi hakkin jininsa a hannunka.
Pareillement si le juste se détourne de sa justice, et commet l'iniquité, lorsque j'aurai mis quelque obstacle devant lui, il mourra, parce que tu ne l'auras point averti; il mourra dans son péché, et il ne sera point fait mention de ses justices qu'il aura faites; mais je redemanderai son sang de ta main.
21 Amma in ka yi wa mai adalcin kashedi kada yă yi zunubi bai kuwa yi zunubi ba, tabbatacce zai rayu saboda ya ji kashedin, kuma kai kam za ka kuɓuta.”
Que si tu avertis le juste de ne pécher point, et que lui aussi ne pèche point, il vivra certainement, parce qu'il aura été averti, et toi pareillement tu auras délivré ton âme.
22 Hannun Ubangiji ya kasance a kaina a can, ya kuma ce mini, “Tashi ka fita zuwa fili, a can kuwa zan yi maka magana.”
Et la main de l'Eternel fut là sur moi, et il me dit: lève-toi, et sors vers la campagne, et là je te parlerai.
23 Saboda haka na tashi da tafi fili. Ɗaukakar Ubangiji kuwa ta tsaya a can, kamar ɗaukakar da na gani kusa da Kogin Kebar, sai na fāɗi rubda ciki.
Je me levai donc, et sortis vers la campagne; et voici, la gloire de l'Eternel se tenait là, telle que la gloire que j'avais vue auprès du fleuve de Kébar, et je tombai sur ma face.
24 Sai Ruhu ya sauko a kaina ya kuma ɗaga ni na tsaya a ƙafafuna. Ya yi mini magana ya ce, “Ka fita, ka rufe kanka a cikin gida.
Alors l'Esprit entra dans moi, et me releva sur mes pieds, et il me parla, et [me] dit: entre, et t'enferme dans ta maison.
25 Kuma kai, ɗan mutum, za su ɗaura ka da igiyoyi; za a daure ka yadda ba za ka iya fita a cikin mutane ba.
Car quant à toi, fils d'homme, voici, on mettra des cordes sur toi, et on t'en liera, et tu ne sortiras point pour aller parmi eux.
26 Zan sa harshenka ya manne wa dasashinka don ka yi shiru ka kuma kāsa tsawata musu, ko da yake su gidan’yan tawaye ne.
Et je ferai tenir ta langue à ton palais, tu seras muet, et tu ne les reprendras point; parce qu'ils sont une maison rebelle.
27 Amma sa’ad da na yi maka magana, zan buɗe bakinka za ka kuwa faɗa musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya faɗa.’ Duk mai ji ya ji, kuma duk wanda ya ƙi ji, ya ƙi ji; gama su gida ne na’yan tawaye.
Mais quand je te parlerai, j'ouvrirai ta bouche, et tu leur diras: ainsi a dit le Seigneur l'Eternel: que celui qui écoute, écoute; et que celui qui n'écoute pas, n'écoute pas; car ils [sont] une maison rebelle.

< Ezekiyel 3 >