< Ezekiyel 3 >

1 Ya kuma ce mini, “Ɗan mutum, ka ci abin da yake a gabanka, ka ci wannan littafi; sa’an nan ka tafi ka yi magana wa gidan Isra’ila.”
And he said to me, Son of man, eat that which thou findest; eat this roll, and go, speak to the house of Israel!
2 Saboda haka na buɗe bakina, ya kuma ba ni littafin in ci.
So I opened my mouth, and he gave me the roll to eat.
3 Sai ya ce mini, “Ɗan mutum, ka ci wannan littafin da nake ba ka, ka kuma cika cikinka da shi.” Sai na ci shi, ya kuma yi zaki kamar zuma a bakina.
And he said to me, Son of man, let thy stomach eat, and fill thy body with this roll which I give thee! Then I ate it, and it was in my mouth as honey for sweetness.
4 Sa’an nan ya ce mini, “Ɗan mutum, yanzu ka tafi gidan Isra’ila ka faɗa kalmomina gare su.
And he said to me: Son of man, go, get thee to the house of Israel, and speak my words to them!
5 Ba ina aikan ka wurin mutanen da suke da baƙon harshe da kuma yare mai wuya ba ne, amma zuwa ga gidan Isra’ila ne,
For not to a people of a dark speech and a hard language art thou sent, but to the house of Israel;
6 ba ga mutane da yawa na baƙon harshe da yare mai wuya, waɗanda ba ka san kalmominsu ba. Tabbatacce da na aike ka wurin irinsu, da sun saurare ka.
not to many nations of a dark speech and a hard language, whose words thou canst not understand. Truly, had I sent thee to them, they would have hearkened to thee.
7 Amma gidan Isra’ila ba sa niyya su saurare ka domin ba sa niyya su saurare ni, gama dukan gidan Isra’ila sun taurare suna kuma kin ji.
But the house of Israel will not hearken to thee, for they will not hearken to me. For the whole house of Israel is brazen-faced and stiff-hearted.
8 Amma zan sa ka zama mai taurinkai da taurin zuciya kamar su.
Behold, I have made thy face strong against their faces, and thy forehead strong against their foreheads.
9 Zan sa goshinka ya zama da tauri kamar dutse, da tauri fiye da dutsen ƙanƙara ƙarfi. Kada ka ji tsoronsu ko ka firgita ta wurinsu, ko da yake su gidan’yan tawaye ne.”
As an adamant, harder than flint, have I made thy forehead; fear them not, nor be dismayed at their looks; for they are a rebellious house.
10 Ya kuma ce mini, “Ɗan mutum, ka ji da kyau ka kuma lura da dukan kalmomin da nake maka magana.
Moreover, he said to me: Son of man, all my words, which I shall speak to thee, receive in thy heart, and hear with thine ears!
11 Ka tafi yanzu zuwa ga’yan’uwanka waɗanda suke zaman bauta ka yi musu magana. Ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa,’ ko ku ji, ko kada ku ji.”
And go, get thee to them of the captivity, to the children of thy people, and speak to them, and say to them, Thus saith the Lord Jehovah; whether they will hear, or whether they will forbear.
12 Sa’an nan Ruhu ya ɗaga ni sama, a bayana na ji wata karar babban motsi na cewa, Bari a yabi ɗaukakar Ubangiji a wurin zamansa!
Then the spirit lifted me up, and I heard behind me the sound, as of a great rushing, saying, “Praised be the majesty of Jehovah from his place!”
13 Karar fikafikan rayayyun halittun nan ne suke goge junansu da kuma karar da’irorin nan da suke kusa da su, ƙarar babban motsi.
I heard also the noise of the wings of the living creatures, that touched one another, and the noise of the wheels beside them, even a noise of a great rushing.
14 Sa’an nan Ruhu ya ɗaga ni sama ya kuma tafi da ni, na kuwa tafi da ɓacin rai da kuma fushin ruhuna, tare da hannu mai ƙarfi na Ubangiji a bisa na.
So the spirit lifted me up, and took me away, and I went in bitterness, in the heat of my spirit; but the hand of Jehovah was strong upon me.
15 Na zo wurin masu zaman bautan da suke zama a Tel Abib kusa da Kogin Kebar, A can kuwa, inda suke zama, na zauna a cikinsu kwana bakwai, ina mamaki.
Then I came to them of the captivity at Tel-abib, that dwelt by the river Chebar; and I dwelt where they dwelt; I even dwelt astonished among them seven days.
16 A ƙarshen kwana bakwai ɗin maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
And at the end of seven days, the word of Jehovah came to me, and said:
17 “Ɗan mutum, na mai da kai mai tsaro don gidan Isra’ila; saboda haka ka ji maganar da zan yi ka kuma yi musu kashedin nan da ya fito daga gare ni.
Son of man, I have set thee as a watchman to the house of Israel; therefore hear the word from my mouth, and warn them from me!
18 In na ce wa mugu, ‘Lalle za ka mutu,’ ba ka kuwa yi masa kashedi ko ka tsawata masa a kan mugayen hanyoyinsa don yă ceci ransa ba, wannan mugun zai mutu saboda zunubinsa, zan kuwa nemi hakkin jininsa a hannunka.
When I say to the wicked, Thou shalt surely die! and thou givest him not warning, nor speakest to warn the wicked from his wicked way, so that he may live, that wicked man shall die for his iniquity; but his blood will I require at thy hand.
19 Amma in ka yi wa mugun kashedi bai kuwa juya daga mugayen hanyoyinsa ba, zai mutu saboda zunubinsa; amma kai kam za ka kuɓuta.
Yet if thou warn the wicked, and he turn not from his wickedness, and from his wicked way, he shall die for his iniquity, but thou hast delivered thy soul.
20 “Har yanzu, in mai adalci ya juya daga adalcinsa ya aikata mugunta, na kuma sa abin tuntuɓe a gabansa, zai mutu. Da yake ba ka yi masa kashedi ba, zai mutu saboda zunubinsa. Ba za a tuna da abin adalcin da ya yi ba, zan kuwa nemi hakkin jininsa a hannunka.
Again, when a righteous man turneth from his righteousness, and committeth iniquity, and I lay a stumbling-block before him, and he shall die because thou hast not given him warning, he will die for his sin; and his righteousness which he hath done will not be remembered; but his blood will I require at thy hand.
21 Amma in ka yi wa mai adalcin kashedi kada yă yi zunubi bai kuwa yi zunubi ba, tabbatacce zai rayu saboda ya ji kashedin, kuma kai kam za ka kuɓuta.”
Yet if thou warn the righteous man, that he sin not, and the righteous man doth not sin, he shall surely live, because he hath received warning; and thou hast delivered thy soul.
22 Hannun Ubangiji ya kasance a kaina a can, ya kuma ce mini, “Tashi ka fita zuwa fili, a can kuwa zan yi maka magana.”
And the hand of Jehovah was there upon me, and he said to me, Arise, go forth into the plain, and there will I speak with thee.
23 Saboda haka na tashi da tafi fili. Ɗaukakar Ubangiji kuwa ta tsaya a can, kamar ɗaukakar da na gani kusa da Kogin Kebar, sai na fāɗi rubda ciki.
Then I arose, and went forth into the plain, and lo, the glory of Jehovah stood there, as the glory which I saw by the river Chebar; and I fell upon my face.
24 Sai Ruhu ya sauko a kaina ya kuma ɗaga ni na tsaya a ƙafafuna. Ya yi mini magana ya ce, “Ka fita, ka rufe kanka a cikin gida.
Then the spirit entered into me, and set me upon my feet. And he spake with me, and said to me: Go, shut thyself within thy house.
25 Kuma kai, ɗan mutum, za su ɗaura ka da igiyoyi; za a daure ka yadda ba za ka iya fita a cikin mutane ba.
And behold, O son of man, bands shall be put upon thee, and thou shalt be bound therewith; and thou shalt not go out among them.
26 Zan sa harshenka ya manne wa dasashinka don ka yi shiru ka kuma kāsa tsawata musu, ko da yake su gidan’yan tawaye ne.
And I will make thy tongue cleave to the roof of thy mouth, that thou shalt be dumb, and shalt not be to them a reprover; for they are a rebellious house.
27 Amma sa’ad da na yi maka magana, zan buɗe bakinka za ka kuwa faɗa musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya faɗa.’ Duk mai ji ya ji, kuma duk wanda ya ƙi ji, ya ƙi ji; gama su gida ne na’yan tawaye.
But when I speak with thee, I will open thy mouth, and thou shalt say to them, Thus saith the Lord Jehovah: He that will hear, let him hear, and he that will forbear, let him forbear; for they are a rebellious house.

< Ezekiyel 3 >