< Ezekiyel 3 >

1 Ya kuma ce mini, “Ɗan mutum, ka ci abin da yake a gabanka, ka ci wannan littafi; sa’an nan ka tafi ka yi magana wa gidan Isra’ila.”
Og han sagde til mig: Du Menneskesøn! æd det, som du her modtager; æd denne Rulle, og gak hen, tal til Israels Hus.
2 Saboda haka na buɗe bakina, ya kuma ba ni littafin in ci.
Og jeg oplod min Mund, og han gav mig denne Rulle at æde.
3 Sai ya ce mini, “Ɗan mutum, ka ci wannan littafin da nake ba ka, ka kuma cika cikinka da shi.” Sai na ci shi, ya kuma yi zaki kamar zuma a bakina.
Og han sagde til mig: Du Menneskesøn! Du skal bespise din Bug og fylde dine Indvolde med denne Rulle, som jeg giver dig; og jeg aad, og den var sød i min Mund som Honning.
4 Sa’an nan ya ce mini, “Ɗan mutum, yanzu ka tafi gidan Isra’ila ka faɗa kalmomina gare su.
Og han sagde til mig: Du Menneskesøn! gak hen, kom til Israels Hus, og tal mine Ord til dem!
5 Ba ina aikan ka wurin mutanen da suke da baƙon harshe da kuma yare mai wuya ba ne, amma zuwa ga gidan Isra’ila ne,
Thi du er ikke sendt til et Folk med et uforstaaeligt og vanskeligt Tungemaal, men til Israels Hus;
6 ba ga mutane da yawa na baƙon harshe da yare mai wuya, waɗanda ba ka san kalmominsu ba. Tabbatacce da na aike ka wurin irinsu, da sun saurare ka.
ikke til mange Folk med et uforstaaeligt og vanskeligt Tungemaal, hvis Ord du ikke kan forstaa; men jeg sender dig til dem, som kunne forstaa dig.
7 Amma gidan Isra’ila ba sa niyya su saurare ka domin ba sa niyya su saurare ni, gama dukan gidan Isra’ila sun taurare suna kuma kin ji.
Men Israels Hus skal ikke ville høre dig; thi de ville ikke høre mig; thi hele Israels Hus har haarde Pander og stive Hjerter.
8 Amma zan sa ka zama mai taurinkai da taurin zuciya kamar su.
Se, jeg gør dit Ansigt haardt imod deres Ansigt og din Pande haard imod deres Pande.
9 Zan sa goshinka ya zama da tauri kamar dutse, da tauri fiye da dutsen ƙanƙara ƙarfi. Kada ka ji tsoronsu ko ka firgita ta wurinsu, ko da yake su gidan’yan tawaye ne.”
Jeg gør din Pande som en Demant, haardere end en Klippe; du skal ikke frygte for dem og ej forfærdes for deres Ansigt; thi de ere et genstridigt Hus.
10 Ya kuma ce mini, “Ɗan mutum, ka ji da kyau ka kuma lura da dukan kalmomin da nake maka magana.
Og han sagde til mig: Du Menneskesøn! alle mine Ord, som jeg taler til dig, annam dem i dit Hjerte, og hør dem med dine Øren!
11 Ka tafi yanzu zuwa ga’yan’uwanka waɗanda suke zaman bauta ka yi musu magana. Ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa,’ ko ku ji, ko kada ku ji.”
Og gak hen, kom til de bortførte, til dit Folks Børn, og tal til dem, og sig til dem: Saa siger den Herre, Herre — hvad enten de lyde eller lade være.
12 Sa’an nan Ruhu ya ɗaga ni sama, a bayana na ji wata karar babban motsi na cewa, Bari a yabi ɗaukakar Ubangiji a wurin zamansa!
Da løftede Aanden mig op, og jeg hørte bag mig et stort Bulders Røst: „Lovet være Herrens Herlighed”, fra dens Sted;
13 Karar fikafikan rayayyun halittun nan ne suke goge junansu da kuma karar da’irorin nan da suke kusa da su, ƙarar babban motsi.
og Lyden af hine levende Væseners Vinger, som berørte den ene den anden, og Lyden af Hjulene ved Siden af dem og et stort Bulders Lyd.
14 Sa’an nan Ruhu ya ɗaga ni sama ya kuma tafi da ni, na kuwa tafi da ɓacin rai da kuma fushin ruhuna, tare da hannu mai ƙarfi na Ubangiji a bisa na.
Og en Aand opløftede mig og tog mig bort, og jeg for hen, bitter i min Aands Harme; men Herrens Haand var stærk over mig.
15 Na zo wurin masu zaman bautan da suke zama a Tel Abib kusa da Kogin Kebar, A can kuwa, inda suke zama, na zauna a cikinsu kwana bakwai, ina mamaki.
Og jeg kom til de bortførte til Tel-Abib, til dem, som boede ved Floden Kebar, og der, hvor de boede, blev jeg siddende i syv Dage, stum midt iblandt dem.
16 A ƙarshen kwana bakwai ɗin maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Og det skete, der syv Dage vare til Ende, da kom Herrens Ord til mig saaledes:
17 “Ɗan mutum, na mai da kai mai tsaro don gidan Isra’ila; saboda haka ka ji maganar da zan yi ka kuma yi musu kashedin nan da ya fito daga gare ni.
Du Menneskesøn! jeg har sat dig til en Vægter for Israels Hus, og du skal høre Ord af min Mund og advare dem paa mine Vegne.
18 In na ce wa mugu, ‘Lalle za ka mutu,’ ba ka kuwa yi masa kashedi ko ka tsawata masa a kan mugayen hanyoyinsa don yă ceci ransa ba, wannan mugun zai mutu saboda zunubinsa, zan kuwa nemi hakkin jininsa a hannunka.
Naar jeg siger til den ugudelige: Du skal visselig dø, og du ikke advarer ham og ikke taler for at advare den ugudelige for hans ugudelige Vej, for at frelse hans Liv: Da skal den ugudelige selv dø i sin Misgerning, og jeg vil kræve hans Blod af din Haand.
19 Amma in ka yi wa mugun kashedi bai kuwa juya daga mugayen hanyoyinsa ba, zai mutu saboda zunubinsa; amma kai kam za ka kuɓuta.
Men naar du har advaret den ugudelige, og han dog ikke omvender sig fra sin Ugudelighed og fra sin ugudelige Vej, da skal han dø i sin Misgerning, men du har din Sjæl frelst.
20 “Har yanzu, in mai adalci ya juya daga adalcinsa ya aikata mugunta, na kuma sa abin tuntuɓe a gabansa, zai mutu. Da yake ba ka yi masa kashedi ba, zai mutu saboda zunubinsa. Ba za a tuna da abin adalcin da ya yi ba, zan kuwa nemi hakkin jininsa a hannunka.
Og naar en retfærdig vender sig bort fra sin Retfærdighed og gør Uret, og jeg lægger Anstød for hans Ansigt, skal han dø; fordi du ikke har advaret ham, skal han dø i sin Synd, og hans retfærdige Gerninger, som han har gjort, skulle ikke ihukommes; og hans Blod vil jeg kræve af din Haand.
21 Amma in ka yi wa mai adalcin kashedi kada yă yi zunubi bai kuwa yi zunubi ba, tabbatacce zai rayu saboda ya ji kashedin, kuma kai kam za ka kuɓuta.”
Men naar du har advaret den retfærdige, at den retfærdige ikke maa synde, og han ikke synder, da skal han visselig leve; thi han lod sig advare, og du har din Sjæl frelst.
22 Hannun Ubangiji ya kasance a kaina a can, ya kuma ce mini, “Tashi ka fita zuwa fili, a can kuwa zan yi maka magana.”
Og Herrens Haand var over mig der, og han sagde til mig: Staa op, gak ud i Dalen, og der vil jeg tale med dig.
23 Saboda haka na tashi da tafi fili. Ɗaukakar Ubangiji kuwa ta tsaya a can, kamar ɗaukakar da na gani kusa da Kogin Kebar, sai na fāɗi rubda ciki.
Og jeg stod op og gik ud i Dalen, og se, der stod Herrens Herlighed ligesom den Herlighed, hvilken jeg havde set ved Floden Kebar; og jeg faldt paa mit Ansigt.
24 Sai Ruhu ya sauko a kaina ya kuma ɗaga ni na tsaya a ƙafafuna. Ya yi mini magana ya ce, “Ka fita, ka rufe kanka a cikin gida.
Og der kom Aand i mig og rejste mig op paa mine Fødder, og han talte med mig og sagde til mig: Gak hen, luk dig inde i dit Hus!
25 Kuma kai, ɗan mutum, za su ɗaura ka da igiyoyi; za a daure ka yadda ba za ka iya fita a cikin mutane ba.
Og du Menneskesøn! se, de skulle lægge Reb paa dig og binde dig med dem, at du ikke kan gaa ud midt iblandt dem.
26 Zan sa harshenka ya manne wa dasashinka don ka yi shiru ka kuma kāsa tsawata musu, ko da yake su gidan’yan tawaye ne.
Og jeg vil lade din Tunge hænge ved din Gane, at du skal være stum og ikke være dem en Mand, som straffer; thi de ere et genstridigt Hus.
27 Amma sa’ad da na yi maka magana, zan buɗe bakinka za ka kuwa faɗa musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya faɗa.’ Duk mai ji ya ji, kuma duk wanda ya ƙi ji, ya ƙi ji; gama su gida ne na’yan tawaye.
Men naar jeg taler til dig, vil jeg aabne din Mund, og du skal sige til dem: Saa siger den Herre, Herre: Hvo, der vil høre, han høre! og hvo, der vil lade være, han lade være! thi de ere et genstridigt Hus.

< Ezekiyel 3 >