< Ezekiyel 29 >

1 A shekara ta goma, a wata na goma, a rana ta goma sha biyu, maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
No décimo ano, no décimo mês, no décimo segundo dia do mês, a palavra de Javé veio a mim, dizendo:
2 “Ɗan mutum, ka fuskanci Fir’auna sarkin Masar ka kuma yi annabci gāba da shi da dukan Masar.
“Filho do homem, põe teu rosto contra o Faraó, rei do Egito, e profetiza contra ele e contra todo o Egito”.
3 Yi masa magana ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Ina gāba da kai, Fir’auna sarkin Masar, kai babban mugun dodon ruwa kwance cikin rafuffukanka. Ka ce, “Nilu nawa ne; na yi shi wa kaina.”
Fala e diz: “O Senhor Javé diz: “Eis que estou contra ti, faraó rei do Egito”, o grande monstro que está no meio de seus rios, que disse: 'Meu rio é meu', e eu o fiz por mim mesmo”.
4 Amma zan sa ƙugiyoyi a muƙamuƙanka in sa kifin rafuffukanka su manne wa kamɓorinka. Zan jawo ka daga cikin tsakiyar rafuffukanka, da dukan kifayen rafuffukanka, waɗanda suka manne a ƙamborinka,
Vou colocar ganchos em suas mandíbulas, e farei com que os peixes de seus rios fiquem grudados em suas escamas. Eu o tirarei do meio de seus rios, com todos os peixes de seus rios que se agarram a suas escamas.
5 Zan bar ka a cikin hamada, kai da dukan kifin rafuffukanka. Za ka fāɗi a fili ba kuwa za a tattara ka ko a kwashe ba. Zan ba da kai kamar abinci ga namun jeji na duniya da tsuntsayen sararin sama.
I vai expulsá-lo para o deserto, você e todos os peixes de seus rios. Você vai cair em campo aberto. Você não será reunido ou reunido. Eu vos dei de comer aos animais da terra e para as aves do céu.
6 Ta haka dukan waɗanda suke zama a Masar za su san cewa ni ne Ubangiji. “‘Ka zama sandan iwa domin gidan Isra’ila.
“““Todos os habitantes do Egito saberão que eu sou Yahweh, porque eles têm sido um pessoal de cana para a casa de Israel.
7 Sa’ad da suka kama ka da hannuwansu, ka tsattsage, ka kuma buɗu a kafaɗunsu; sa’ad da suka jingina a kanka, sai ka karye, bayansu kuwa ya firgita.
Quando eles se apoderaram de você pela mão, você quebrou e rasgou todos os seus ombros. Quando eles se apoiaram em você, você quebrou e paralisou todas as coxas deles”.
8 “‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan kawo takobi a kanka in kashe mutane da dabbobi.
“'Portanto, o Senhor Javé diz: “Eis que trarei uma espada sobre vós e vos cortarei o homem e o animal.
9 Masar za tă zama kufai. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji. “‘Domin ka ce, “Nilu nawa ne; ni na yi shi,”
A terra do Egito será uma desolação e um desperdício. Então eles saberão que eu sou Yahweh. Porque ele disse: “O rio é meu, e eu consegui”,
10 saboda haka ina gāba da kai da rafuffukanka, zan kuma maishe ƙasar Masar ta lalace ta kuma zama kango daga Migdol zuwa Aswan, har iyakar Kush.
portanto, eis que estou contra você e contra seus rios. Farei da terra do Egito um total desperdício e desolação, desde a torre de Seveneh até a fronteira da Etiópia.
11 Ba ƙafar mutum ko ta dabbar da za tă ratsa ta; ba wanda zai zauna a can har shekaru arba’in.
Nenhum pé do homem passará por ela, nem nenhum pé de animal passará por ela. Não será habitada por quarenta anos.
12 Zan mai da ƙasar Masar kufai a cikin ƙasashen da aka ragargaza, biranenta kuma za su zama kango har shekaru arba’in a cikin biranen da aka lalace. Zan watsar da Masarawa a cikin al’ummai in warwatsa su cikin ƙasashe.
Farei da terra do Egito uma desolação no meio dos países que estão desolados. Suas cidades entre as cidades assoladas serão uma desolação por quarenta anos. Espalharei os egípcios entre as nações, e os dispersarei pelos países”.
13 “‘Duk da haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa a ƙarshen shekaru arba’in ɗin zan tattara Masarawa daga al’ummai inda aka warwatsa su.
“'For the Lord Yahweh says: “No final de quarenta anos eu reunirei os egípcios dos povos onde eles estavam espalhados.
14 Zan komo da su daga zaman bauta in mai da su zuwa Masar ta Bisa, ƙasarsu ta ainihi. A can za su zama masarauta marar ƙarfi.
Vou reverter o cativeiro do Egito, e os farei voltar à terra de Pathros, à terra de seu nascimento”. Lá eles serão um reino humilde.
15 Za tă zama masarauta mafi rarrauna cikin masarautai, ba kuwa za tă ƙara ɗaga kanta a kan sauran al’ummai ba. Zan sa tă zama marar ƙarfi ƙwarai, har da ba za tă ƙara yin mulkin a kan al’ummai ba.
Será o mais humilde dos reinos. Não se erguerá mais acima das nações. Diminui-los-ei para que não governem mais sobre as nações.
16 Masar ba za tă ƙara zama abin dogara ga mutanen Isra’ila ba amma za tă zama abin tunin zunubinsu na juyawa gare ta don taimako. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji Mai Iko Duka.’”
Não será mais a confiança da casa de Israel, trazendo a iniqüidade à memória, quando se voltarem para cuidar deles. Então saberão que eu sou o Senhor Yahweh””.
17 A shekara ta ashirin da bakwai, a wata na fari a rana ta farko, maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
No vigésimo sétimo ano, no primeiro mês, no primeiro dia do mês, a palavra de Javé veio a mim, dizendo:
18 “Ɗan mutum, Nebukadnezzar sarkin Babilon ya sa sojojinsa su matsa wa Taya; kowane kai ya koɗe, kowace kafaɗa kuma ta goge. Duk da haka shi da sojojinsa ba su sami wani lada daga matsin da suka yi a kan Taya ba.
“Filho do homem, Nabucodonosor rei da Babilônia fez com que seu exército prestasse um grande serviço contra Tiro. Cada cabeça era careca, e cada ombro era usado; contudo, ele não tinha salário, nem seu exército, de Tiro, pelo serviço que havia prestado contra ele.
19 Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan ba da Masar ga Nebukadnezzar sarkin Babilon, zai washe dukiyarta. Zai kwashe ya washe ƙasar ganima a matsayin abin biyan sojojinsa.
Portanto, o Senhor Javé diz: “Eis que eu darei a terra do Egito a Nabucodonosor, rei da Babilônia”. Ele carregará a multidão dela, a saqueará e a tomará presa”. Esse será o salário de seu exército”.
20 Saboda haka na ba shi Masar a matsayin lada don ƙoƙarinsa domin shi da sojojinsa sun yi wannan domina ne, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
Eu lhe dei a terra do Egito como seu pagamento pelo qual ele serviu, porque eles trabalharam para mim”, diz o Senhor Yahweh.
21 “A wannan rana zan sa ƙaho ya tsiro wa gidan Isra’ila, zan kuma buɗe bakinka a cikinsu. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji.”
“Naquele dia farei brotar uma buzina para a casa de Israel, e abrirei sua boca entre eles. Então eles saberão que eu sou Yahweh”.

< Ezekiyel 29 >