< Ezekiyel 29 >

1 A shekara ta goma, a wata na goma, a rana ta goma sha biyu, maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
در سال دهم تبعیدمان، در روز دوازدهم ماه دهم، این پیغام از جانب خداوند بر من نازل شد:
2 “Ɗan mutum, ka fuskanci Fir’auna sarkin Masar ka kuma yi annabci gāba da shi da dukan Masar.
«ای پسر انسان، رو به سوی مصر نموده، بر ضد پادشاه و تمام مردم آن پیشگویی کن.
3 Yi masa magana ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Ina gāba da kai, Fir’auna sarkin Masar, kai babban mugun dodon ruwa kwance cikin rafuffukanka. Ka ce, “Nilu nawa ne; na yi shi wa kaina.”
به ایشان بگو که خداوند یهوه می‌فرماید: ای پادشاه مصر، ای اژدهای بزرگ که در وسط رودخانه‌ات خوابیده‌ای، من دشمن تو هستم. چون گفته‌ای:”رود نیل مال من است! من آن را برای خود درست کرده‌ام!“
4 Amma zan sa ƙugiyoyi a muƙamuƙanka in sa kifin rafuffukanka su manne wa kamɓorinka. Zan jawo ka daga cikin tsakiyar rafuffukanka, da dukan kifayen rafuffukanka, waɗanda suka manne a ƙamborinka,
پس، من قلابها را در چانه‌ات می‌گذارم و تو را با ماهی‌هایی که به پوست بدنت چسبیده‌اند به خشکی می‌کشانم.
5 Zan bar ka a cikin hamada, kai da dukan kifin rafuffukanka. Za ka fāɗi a fili ba kuwa za a tattara ka ko a kwashe ba. Zan ba da kai kamar abinci ga namun jeji na duniya da tsuntsayen sararin sama.
تو را با تمام ماهی‌ها در خشکی رها می‌کنم تا بمیرید. لاشه‌های شما در صحرا پراکنده خواهد شد و کسی آنها را جمع نخواهد کرد. من شما را خوراک پرندگان و جانوران وحشی می‌کنم.
6 Ta haka dukan waɗanda suke zama a Masar za su san cewa ni ne Ubangiji. “‘Ka zama sandan iwa domin gidan Isra’ila.
آنگاه تمام مردم مصر خواهند دانست که من یهوه هستم.» خداوند می‌فرماید: «ای مصر، تو برای قوم اسرائیل عصای ترک خورده‌ای بیش نبودی.
7 Sa’ad da suka kama ka da hannuwansu, ka tsattsage, ka kuma buɗu a kafaɗunsu; sa’ad da suka jingina a kanka, sai ka karye, bayansu kuwa ya firgita.
وقتی اسرائیل به تو تکیه کرد، تو خرد شدی و شانه‌اش را شکستی و او را به درد و عذاب گرفتار کردی.
8 “‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan kawo takobi a kanka in kashe mutane da dabbobi.
بنابراین، من که خداوند یهوه هستم به تو می‌گویم که لشکری به جنگ تو می‌آورم و تمام انسانها و حیواناتت را از بین می‌برم.
9 Masar za tă zama kufai. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji. “‘Domin ka ce, “Nilu nawa ne; ni na yi shi,”
سرزمین مصر به ویرانه‌ای تبدیل خواهد شد و مصری‌ها خواهند دانست من یهوه هستم. «چون گفتی:”رود نیل مال من است! من آن را درست کرده‌ام!“
10 saboda haka ina gāba da kai da rafuffukanka, zan kuma maishe ƙasar Masar ta lalace ta kuma zama kango daga Migdol zuwa Aswan, har iyakar Kush.
پس، من بر ضد تو و بر ضد رودخانه‌ات هستم و سرزمین مصر را از مِجدُل تا اَسوان و تا مرز حبشه به کلی ویران می‌کنم.
11 Ba ƙafar mutum ko ta dabbar da za tă ratsa ta; ba wanda zai zauna a can har shekaru arba’in.
تا مدت چهل سال هیچ انسان یا حیوانی از آن عبور نخواهد کرد و آن کاملاً ویران و غیر مسکون خواهد بود.
12 Zan mai da ƙasar Masar kufai a cikin ƙasashen da aka ragargaza, biranenta kuma za su zama kango har shekaru arba’in a cikin biranen da aka lalace. Zan watsar da Masarawa a cikin al’ummai in warwatsa su cikin ƙasashe.
مصر را از سرزمینهای ویران شدهٔ همسایه‌اش ویران‌تر می‌سازم و شهرهایش مدت چهل سال خراب می‌مانند و مصری‌ها را به سرزمینهای دیگر تبعید می‌کنم.»
13 “‘Duk da haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa a ƙarshen shekaru arba’in ɗin zan tattara Masarawa daga al’ummai inda aka warwatsa su.
خداوند یهوه می‌فرماید: «بعد از چهل سال، دوباره مصری‌ها را از ممالکی که به آنجا تبعید شده بودند، به مصر باز می‌آورم
14 Zan komo da su daga zaman bauta in mai da su zuwa Masar ta Bisa, ƙasarsu ta ainihi. A can za su zama masarauta marar ƙarfi.
تا در زمین فَتروس که در جنوب مصر قرار دارد و زادگاه خودشان است، زندگی کنند. ولی آنها قومی کم‌اهمیت و کوچک خواهند بود.
15 Za tă zama masarauta mafi rarrauna cikin masarautai, ba kuwa za tă ƙara ɗaga kanta a kan sauran al’ummai ba. Zan sa tă zama marar ƙarfi ƙwarai, har da ba za tă ƙara yin mulkin a kan al’ummai ba.
آنها از همهٔ قومها پست‌تر خواهند بود و دیگر خود را برتر از سایرین نخواهند دانست. من مصر را آنقدر کوچک می‌کنم که دیگر نتواند بر قومهای دیگر حکمرانی کند.
16 Masar ba za tă ƙara zama abin dogara ga mutanen Isra’ila ba amma za tă zama abin tunin zunubinsu na juyawa gare ta don taimako. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji Mai Iko Duka.’”
قوم اسرائیل نیز دیگر از مصر انتظار هیچ کمکی نخواهند داشت. هر وقت به فکر کمک گرفتن از مصر بیفتند، گناهی را که قبلاً از این لحاظ مرتکب شده بودند، به یاد خواهند آورد. پس خواهند دانست که من خداوند یهوه هستم.»
17 A shekara ta ashirin da bakwai, a wata na fari a rana ta farko, maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
در سال بیست و هفتم تبعیدمان، در روز اول ماه اول، از طرف خداوند این پیغام به من رسید:
18 “Ɗan mutum, Nebukadnezzar sarkin Babilon ya sa sojojinsa su matsa wa Taya; kowane kai ya koɗe, kowace kafaɗa kuma ta goge. Duk da haka shi da sojojinsa ba su sami wani lada daga matsin da suka yi a kan Taya ba.
«ای پسر انسان، وقتی نِبوکَدنِصَّر، پادشاه بابِل، با مملکت صور می‌جنگید، سربازانش آنقدر بارهای سنگین حمل کردند که موهای سرشان ریخت و پوست شانه‌هایشان ساییده شد. اما از آن همه زحمتی که در این جنگ کشیدند چیزی نصیب نِبوکَدنِصَّر و سربازانش نشد.
19 Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan ba da Masar ga Nebukadnezzar sarkin Babilon, zai washe dukiyarta. Zai kwashe ya washe ƙasar ganima a matsayin abin biyan sojojinsa.
پس، من که خداوند یهوه هستم سرزمین مصر را به نِبوکَدنِصَّر، پادشاه بابِل، می‌دهم تا ثروت آن را به یغما ببرد و هر چه دارد غارت کند و اجرت سربازانش را بدهد.
20 Saboda haka na ba shi Masar a matsayin lada don ƙoƙarinsa domin shi da sojojinsa sun yi wannan domina ne, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
بله، به جای اجرتش سرزمین مصر را به او می‌دهم، چون در طول آن سیزده سال در صور او برای من کار می‌کرد. من که خداوند یهوه هستم این را گفته‌ام.
21 “A wannan rana zan sa ƙaho ya tsiro wa gidan Isra’ila, zan kuma buɗe bakinka a cikinsu. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji.”
«سرانجام روزی می‌رسد که من قدرت گذشتهٔ اسرائیل را به او باز می‌گردانم، و دهان تو را ای حِزِقیال خواهم گشود تا سخن بگویی؛ آنگاه مصر خواهد دانست که من یهوه هستم.»

< Ezekiyel 29 >