< Ezekiyel 29 >

1 A shekara ta goma, a wata na goma, a rana ta goma sha biyu, maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
En la dixième année, au dixième mois, au onzième jour du mois, la parole du Seigneur me fut adressée, disant:
2 “Ɗan mutum, ka fuskanci Fir’auna sarkin Masar ka kuma yi annabci gāba da shi da dukan Masar.
Fils d’un homme, tourne ta face contre Pharaon, roi d’Egypte, et tu prophétiseras sur lui et sur toute l’Egypte.
3 Yi masa magana ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Ina gāba da kai, Fir’auna sarkin Masar, kai babban mugun dodon ruwa kwance cikin rafuffukanka. Ka ce, “Nilu nawa ne; na yi shi wa kaina.”
Parle, et tu diras: Voici ce que dit le Seigneur Dieu: Voilà que moi je viens vers toi, Pharaon, roi d’Egypte, grand dragon, qui te couches au milieu de tes fleuves, et dis: Le fleuve est à moi, et je me suis fait moi-même.
4 Amma zan sa ƙugiyoyi a muƙamuƙanka in sa kifin rafuffukanka su manne wa kamɓorinka. Zan jawo ka daga cikin tsakiyar rafuffukanka, da dukan kifayen rafuffukanka, waɗanda suka manne a ƙamborinka,
Et je mettrai un frein à tes mâchoires, et j’attacherai les poissons de tes fleuves à tes écailles; et je te tirerai du milieu de tes fleuves, et tous les poissons s’attacheront à tes écailles,
5 Zan bar ka a cikin hamada, kai da dukan kifin rafuffukanka. Za ka fāɗi a fili ba kuwa za a tattara ka ko a kwashe ba. Zan ba da kai kamar abinci ga namun jeji na duniya da tsuntsayen sararin sama.
Et je te jetterai dans le désert, toi et tous les poissons de ton fleuve; tu tomberas sur la face de la terre; tu ne seras ni recueilli ni ramassé; aux bêtes de la terre et aux volatiles du ciel, je t’ai donné pour être dévoré.
6 Ta haka dukan waɗanda suke zama a Masar za su san cewa ni ne Ubangiji. “‘Ka zama sandan iwa domin gidan Isra’ila.
Et tous les habitants de l’Egypte sauront que je suis le Seigneur, parce que tu as été un bâton de roseau pour la maison d’Israël.
7 Sa’ad da suka kama ka da hannuwansu, ka tsattsage, ka kuma buɗu a kafaɗunsu; sa’ad da suka jingina a kanka, sai ka karye, bayansu kuwa ya firgita.
Quand ils t’ont pris avec la main, tu t’es rompu, et tu leur as déchiré toute l’épaule; et lorsqu’ils se sont appuyés sur toi, tu as été mis en pièces, et tu as brisé tous leurs reins.
8 “‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan kawo takobi a kanka in kashe mutane da dabbobi.
À cause de cela, voici ce que dit le Seigneur Dieu: Voilà que moi j’amènerai sur toi le glaive, et je tuerai de toi les hommes et les bêtes.
9 Masar za tă zama kufai. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji. “‘Domin ka ce, “Nilu nawa ne; ni na yi shi,”
Et la terre de l’Egypte sera convertie en désert et en solitude; et ils sauront que je suis le Seigneur, parce que tu as dit: Le fleuve est à moi, et c’est moi qui l’ai fait.
10 saboda haka ina gāba da kai da rafuffukanka, zan kuma maishe ƙasar Masar ta lalace ta kuma zama kango daga Migdol zuwa Aswan, har iyakar Kush.
C’est pourquoi voici que moi je viens vers toi et vers tes fleuves: et je ferai de la terre d’Egypte des solitudes, après qu’elle aura été ravagée par le glaive, depuis la tour de Syène jusqu’aux frontières de l’Ethiopie.
11 Ba ƙafar mutum ko ta dabbar da za tă ratsa ta; ba wanda zai zauna a can har shekaru arba’in.
Le pied d’un homme ne la traversera pas, et le pied d’une bête n’y marchera pas; et elle ne sera pas habitée pendant quarante ans.
12 Zan mai da ƙasar Masar kufai a cikin ƙasashen da aka ragargaza, biranenta kuma za su zama kango har shekaru arba’in a cikin biranen da aka lalace. Zan watsar da Masarawa a cikin al’ummai in warwatsa su cikin ƙasashe.
Et je rendrai la terre d’Egypte déserte parmi des terres désertes, et ses cités ruinées parmi des villes ruinées, et elles seront désolées pendant quarante ans; et je disperserai les Egyptiens parmi les nations, et je les jetterai au vent dans les divers pays.
13 “‘Duk da haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa a ƙarshen shekaru arba’in ɗin zan tattara Masarawa daga al’ummai inda aka warwatsa su.
Parce que voici ce que dit le Seigneur Dieu: Après la fin de quarante années, je rassemblerai les Egyptiens du milieu des peuples, parmi lesquels ils avaient été dispersés.
14 Zan komo da su daga zaman bauta in mai da su zuwa Masar ta Bisa, ƙasarsu ta ainihi. A can za su zama masarauta marar ƙarfi.
Et je ramènerai les captifs de l’Egypte, et je les établirai dans la terre de Phathurès, dans la terre de leur naissance, et là ils formeront un humble royaume;
15 Za tă zama masarauta mafi rarrauna cikin masarautai, ba kuwa za tă ƙara ɗaga kanta a kan sauran al’ummai ba. Zan sa tă zama marar ƙarfi ƙwarai, har da ba za tă ƙara yin mulkin a kan al’ummai ba.
Entre tous les royaumes, elle sera le plus humble, et elle ne s’élèvera plus au-dessus des nations; et je les affaiblirai, pour qu’ils ne commandent pas aux nations.
16 Masar ba za tă ƙara zama abin dogara ga mutanen Isra’ila ba amma za tă zama abin tunin zunubinsu na juyawa gare ta don taimako. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji Mai Iko Duka.’”
Et ils ne seront plus la confiance de la maison d’Israël, lui enseignant l’iniquité, afin qu’ils me fuient et qu’ils les suivent; et ils sauront que je suis le Seigneur Dieu.
17 A shekara ta ashirin da bakwai, a wata na fari a rana ta farko, maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Et il arriva en la vingt-septième année, au premier mois, au premier jour du mois, que la parole du Seigneur me fut adressée, disant:
18 “Ɗan mutum, Nebukadnezzar sarkin Babilon ya sa sojojinsa su matsa wa Taya; kowane kai ya koɗe, kowace kafaɗa kuma ta goge. Duk da haka shi da sojojinsa ba su sami wani lada daga matsin da suka yi a kan Taya ba.
Fils d’un homme, Nabuchodonosor, roi de Babylone, a fait faire un grand travail à son armée contre Tyr; toute tête est devenue chauve, toute épaule s’est dépilée: et il ne lui a pas été donné de récompense, ni à son armée, au sujet de Tyr, pour le travail qu’il a fait pour moi contre elle.
19 Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan ba da Masar ga Nebukadnezzar sarkin Babilon, zai washe dukiyarta. Zai kwashe ya washe ƙasar ganima a matsayin abin biyan sojojinsa.
À cause de cela, voici ce que dit le Seigneur Dieu: Voilà que moi j’établirai Nabuchodonosor, roi de Babylone, dans la terre d’Egypte; et il en prendra la multitude, et il en fera son butin, et il enlèvera ses dépouilles; et ce sera une récompense pour son armée,
20 Saboda haka na ba shi Masar a matsayin lada don ƙoƙarinsa domin shi da sojojinsa sun yi wannan domina ne, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
Et pour le service qu’il m’a rendu contre Tyr; je lui ai donné la terre d’Egypte, parce qu’il a travaillé pour moi, dit le Seigneur Dieu.
21 “A wannan rana zan sa ƙaho ya tsiro wa gidan Isra’ila, zan kuma buɗe bakinka a cikinsu. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji.”
.En ce jour-là, une corne poussera à la maison d’Israël; pour toi, je t’ouvrirai la bouche au milieu d’eux; et ils sauront que je suis le Seigneur.

< Ezekiyel 29 >