< Ezekiyel 29 >

1 A shekara ta goma, a wata na goma, a rana ta goma sha biyu, maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
In the tenth year, in the tenth month, in the twelfth day of the month, the word of Jehovah came to me, saying:
2 “Ɗan mutum, ka fuskanci Fir’auna sarkin Masar ka kuma yi annabci gāba da shi da dukan Masar.
Son of man, set thy face against Pharaoh, the king of Egypt, and prophesy against him, and against all Egypt;
3 Yi masa magana ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Ina gāba da kai, Fir’auna sarkin Masar, kai babban mugun dodon ruwa kwance cikin rafuffukanka. Ka ce, “Nilu nawa ne; na yi shi wa kaina.”
Speak, and say, Thus saith the Lord Jehovah: Behold, I am against thee, Pharaoh, king of Egypt, thou great dragon, that liest in the midst of thy rivers, and sayest, “My river is my own, and I have made it for myself.”
4 Amma zan sa ƙugiyoyi a muƙamuƙanka in sa kifin rafuffukanka su manne wa kamɓorinka. Zan jawo ka daga cikin tsakiyar rafuffukanka, da dukan kifayen rafuffukanka, waɗanda suka manne a ƙamborinka,
And I will put hooks in thy jaws, and I will cause the fish of thy rivers to cleave to thy scales, and I will draw thee forth from the midst of thy rivers, and all the fish of thy rivers which cleave to thy scales.
5 Zan bar ka a cikin hamada, kai da dukan kifin rafuffukanka. Za ka fāɗi a fili ba kuwa za a tattara ka ko a kwashe ba. Zan ba da kai kamar abinci ga namun jeji na duniya da tsuntsayen sararin sama.
And I will cast thee into the desert, thee and all the fish of thy rivers; thou shalt fall upon the open fields; thou shalt not be brought together, nor gathered; to the beasts of the field and the birds of heaven I have given thee for food.
6 Ta haka dukan waɗanda suke zama a Masar za su san cewa ni ne Ubangiji. “‘Ka zama sandan iwa domin gidan Isra’ila.
And all the inhabitants of Egypt shall know that I am Jehovah; because they have been a staff of reed to the house of Israel.
7 Sa’ad da suka kama ka da hannuwansu, ka tsattsage, ka kuma buɗu a kafaɗunsu; sa’ad da suka jingina a kanka, sai ka karye, bayansu kuwa ya firgita.
When they took hold of thee by thy handle, thou didst break and pierce their whole shoulder; and when they leaned upon thee, thou didst go to pieces, and madest all their loins to shake.
8 “‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan kawo takobi a kanka in kashe mutane da dabbobi.
Therefore thus saith the Lord Jehovah: Behold, I will bring a sword upon thee, and cut off man and beast out of thee;
9 Masar za tă zama kufai. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji. “‘Domin ka ce, “Nilu nawa ne; ni na yi shi,”
and the land of Egypt shall be desolate and waste; and they shall know that I am Jehovah, because he hath said, “The river is mine, and I have made it.”
10 saboda haka ina gāba da kai da rafuffukanka, zan kuma maishe ƙasar Masar ta lalace ta kuma zama kango daga Migdol zuwa Aswan, har iyakar Kush.
Therefore, behold, I am against thee, and against thy rivers; and I will make the land of Egypt utterly waste and desolate, from Migdol even to Syene, and to the borders of Ethiopia.
11 Ba ƙafar mutum ko ta dabbar da za tă ratsa ta; ba wanda zai zauna a can har shekaru arba’in.
There shall not pass through it the foot of man, and the foot of beast shall not pass through it, neither shall it be inhabited forty years.
12 Zan mai da ƙasar Masar kufai a cikin ƙasashen da aka ragargaza, biranenta kuma za su zama kango har shekaru arba’in a cikin biranen da aka lalace. Zan watsar da Masarawa a cikin al’ummai in warwatsa su cikin ƙasashe.
I will make the land of Egypt desolate amidst the lands that are desolate, and her cities, among the cities that are laid waste, shall be desolate forty years; and I will scatter the Egyptians among the nations, and will disperse them through the countries.
13 “‘Duk da haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa a ƙarshen shekaru arba’in ɗin zan tattara Masarawa daga al’ummai inda aka warwatsa su.
Yet thus saith the Lord Jehovah: At the end of forty years will I gather the Egyptians from the nations whither they are scattered;
14 Zan komo da su daga zaman bauta in mai da su zuwa Masar ta Bisa, ƙasarsu ta ainihi. A can za su zama masarauta marar ƙarfi.
and I will bring back the captives of Egypt, and will cause them to return into the land of Pathros, into the land of their origin; and they shall be there a mean kingdom;
15 Za tă zama masarauta mafi rarrauna cikin masarautai, ba kuwa za tă ƙara ɗaga kanta a kan sauran al’ummai ba. Zan sa tă zama marar ƙarfi ƙwarai, har da ba za tă ƙara yin mulkin a kan al’ummai ba.
it shall be the meanest of all kingdoms; it shall no more exalt itself above the nations; for I will diminish them, that they shall no more rule over the nations.
16 Masar ba za tă ƙara zama abin dogara ga mutanen Isra’ila ba amma za tă zama abin tunin zunubinsu na juyawa gare ta don taimako. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji Mai Iko Duka.’”
And it shall be no more the confidence of the house of Israel, bringing to my remembrance their iniquity in looking to them for help; and they shall know that I am the Lord Jehovah.
17 A shekara ta ashirin da bakwai, a wata na fari a rana ta farko, maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
And it came to pass in the twenty-seventh year, in the first month, on the first day of the month, that the word of Jehovah came to me, saying:
18 “Ɗan mutum, Nebukadnezzar sarkin Babilon ya sa sojojinsa su matsa wa Taya; kowane kai ya koɗe, kowace kafaɗa kuma ta goge. Duk da haka shi da sojojinsa ba su sami wani lada daga matsin da suka yi a kan Taya ba.
Son of man, Nebuchadnezzar, the king of Babylon, caused his army to serve a great service against Tyre; every head was made bald, and every shoulder was peeled; yet neither he nor his army had wages from Tyre for the service which he served against it.
19 Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan ba da Masar ga Nebukadnezzar sarkin Babilon, zai washe dukiyarta. Zai kwashe ya washe ƙasar ganima a matsayin abin biyan sojojinsa.
Therefore thus saith the Lord Jehovah: Behold, I will give the land of Egypt to Nebuchadnezzar, the king of Babylon, and he shall take her multitude, and take her spoil, and take her plunder; and it shall be wages for his army.
20 Saboda haka na ba shi Masar a matsayin lada don ƙoƙarinsa domin shi da sojojinsa sun yi wannan domina ne, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
For his wages for his service I will give him the land of Egypt; for they wrought for me, saith the Lord Jehovah.
21 “A wannan rana zan sa ƙaho ya tsiro wa gidan Isra’ila, zan kuma buɗe bakinka a cikinsu. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji.”
In that day will I cause a horn to grow forth to the house of Israel, and I will give thee to open the mouth in the midst of them; and they shall know that I am Jehovah.

< Ezekiyel 29 >