< Ezekiyel 29 >

1 A shekara ta goma, a wata na goma, a rana ta goma sha biyu, maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Léta desátého, desátého měsíce, dvanáctého dne téhož měsíce, stalo se slovo Hospodinovo ke mně, řkoucí:
2 “Ɗan mutum, ka fuskanci Fir’auna sarkin Masar ka kuma yi annabci gāba da shi da dukan Masar.
Synu člověčí, obrať tvář svou proti Faraonovi králi Egyptskému, a prorokuj proti němu i proti všemu Egyptu.
3 Yi masa magana ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Ina gāba da kai, Fir’auna sarkin Masar, kai babban mugun dodon ruwa kwance cikin rafuffukanka. Ka ce, “Nilu nawa ne; na yi shi wa kaina.”
Mluv a rci: Takto praví Panovník Hospodin: Aj, já proti tobě jsem, ó Faraone králi Egyptský, draku veliký, kterýž ležíš u prostřed řek svých, ješto říkáš: Já mám řeku svou, já zajisté jsem ji přivedl sobě.
4 Amma zan sa ƙugiyoyi a muƙamuƙanka in sa kifin rafuffukanka su manne wa kamɓorinka. Zan jawo ka daga cikin tsakiyar rafuffukanka, da dukan kifayen rafuffukanka, waɗanda suka manne a ƙamborinka,
Protož dám udici do čelistí tvých, a učiním, že zváznou ryby řek tvých na tvých šupinách; i vyvleku tě z prostředku řek tvých, i všecky ryby řek tvých na šupinách tvých zvázlé.
5 Zan bar ka a cikin hamada, kai da dukan kifin rafuffukanka. Za ka fāɗi a fili ba kuwa za a tattara ka ko a kwashe ba. Zan ba da kai kamar abinci ga namun jeji na duniya da tsuntsayen sararin sama.
A nechám tě na poušti, tebe i všech ryb řek tvých. Na svrchku pole padneš, nebudeš sebrán ani shromážděn; šelmám zemským i ptactvu nebeskému dám tě k sežrání.
6 Ta haka dukan waɗanda suke zama a Masar za su san cewa ni ne Ubangiji. “‘Ka zama sandan iwa domin gidan Isra’ila.
I zvědí všickni obyvatelé Egyptští, že já jsem Hospodin, proto že jste holí třtinovou domu Izraelskému.
7 Sa’ad da suka kama ka da hannuwansu, ka tsattsage, ka kuma buɗu a kafaɗunsu; sa’ad da suka jingina a kanka, sai ka karye, bayansu kuwa ya firgita.
Když se chytají tebe rukou, lámeš se, a roztínáš jim všecko rameno; a když se na tě zpodpírají, ztroskotána býváš, ačkoli nastavuješ jim všech bedr.
8 “‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan kawo takobi a kanka in kashe mutane da dabbobi.
Protož takto praví Panovník Hospodin: Aj, já přivedu na tě meč, a vypléním z tebe lidi i hovada.
9 Masar za tă zama kufai. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji. “‘Domin ka ce, “Nilu nawa ne; ni na yi shi,”
I bude země Egyptská pustinou a pouští, i zvědí, že já jsem Hospodin, proto že říkal: Řeka má jest, já zajisté jsem ji přivedl.
10 saboda haka ina gāba da kai da rafuffukanka, zan kuma maishe ƙasar Masar ta lalace ta kuma zama kango daga Migdol zuwa Aswan, har iyakar Kush.
Protož aj, já budu proti tobě i proti řece tvé, a obrátím zemi Egyptskou v pustiny, v poušť přehroznou od věže Sevéne až do pomezí Mouřenínského.
11 Ba ƙafar mutum ko ta dabbar da za tă ratsa ta; ba wanda zai zauna a can har shekaru arba’in.
Nepůjdeť přes ni noha člověka, ani noha dobytčete půjde přes ni, a nebude v ní bydleno za čtyřidceti let.
12 Zan mai da ƙasar Masar kufai a cikin ƙasashen da aka ragargaza, biranenta kuma za su zama kango har shekaru arba’in a cikin biranen da aka lalace. Zan watsar da Masarawa a cikin al’ummai in warwatsa su cikin ƙasashe.
A tak uvedu zemi Egyptskou v pustinu nad jiné země pusté, a města její nad jiná města zpuštěná pustá budou za čtyřidceti let, když rozptýlím Egyptské mezi národy, a rozženu je do rozličných zemí.
13 “‘Duk da haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa a ƙarshen shekaru arba’in ɗin zan tattara Masarawa daga al’ummai inda aka warwatsa su.
A však takto praví Panovník Hospodin: Po skonání čtyřidceti let shromáždím Egyptské z národů, kamž rozptýleni budou.
14 Zan komo da su daga zaman bauta in mai da su zuwa Masar ta Bisa, ƙasarsu ta ainihi. A can za su zama masarauta marar ƙarfi.
A přivedu zase zajaté Egyptské, a uvedu je zase do země Patros, do země přebývání jejich, i budou tam královstvím sníženým.
15 Za tă zama masarauta mafi rarrauna cikin masarautai, ba kuwa za tă ƙara ɗaga kanta a kan sauran al’ummai ba. Zan sa tă zama marar ƙarfi ƙwarai, har da ba za tă ƙara yin mulkin a kan al’ummai ba.
Mimo jiná království bude sníženější, aniž se bude vynášeti více nad jiné národy; zmenším je zajisté, aby nepanovali nad národy.
16 Masar ba za tă ƙara zama abin dogara ga mutanen Isra’ila ba amma za tă zama abin tunin zunubinsu na juyawa gare ta don taimako. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji Mai Iko Duka.’”
I nebude více domu Izraelskému doufáním, kteréž by na pamět přivodilo nepravost, když by se obraceli za nimi; nebo zvědí, že já jsem Panovník Hospodin.
17 A shekara ta ashirin da bakwai, a wata na fari a rana ta farko, maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Potom bylo dvadcátého sedmého léta, prvního měsíce, prvního dne, že se stalo slovo Hospodinovo ke mně, řkoucí:
18 “Ɗan mutum, Nebukadnezzar sarkin Babilon ya sa sojojinsa su matsa wa Taya; kowane kai ya koɗe, kowace kafaɗa kuma ta goge. Duk da haka shi da sojojinsa ba su sami wani lada daga matsin da suka yi a kan Taya ba.
Synu člověčí, Nabuchodonozor král Babylonský podrobil vojsko své v službu velikou proti Týru. Každá hlava oblezla, a každé rameno odříno jest, mzdy pak nemá, on ani vojsko jeho, z Týru za tu službu, kterouž sloužili proti němu.
19 Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan ba da Masar ga Nebukadnezzar sarkin Babilon, zai washe dukiyarta. Zai kwashe ya washe ƙasar ganima a matsayin abin biyan sojojinsa.
Z té příčiny takto praví Panovník Hospodin: Aj, já dávám Nabuchodonozorovi králi Babylonskému zemi Egyptskou, aby pobral zboží její, a rozebral loupeže její, i rozchvátal kořisti její, aby mělo mzdu vojsko jeho.
20 Saboda haka na ba shi Masar a matsayin lada don ƙoƙarinsa domin shi da sojojinsa sun yi wannan domina ne, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
Za práci jejich, kterouž mi sloužili, dám jim zemi Egyptskou, proto že mně pracovali, praví Panovník Hospodin.
21 “A wannan rana zan sa ƙaho ya tsiro wa gidan Isra’ila, zan kuma buɗe bakinka a cikinsu. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji.”
V ten den rozkáži vypučiti se rohu domu Izraelského. Tobě též způsobím, že otevřeš ústa u prostřed nich, i zvědí, že já jsem Hospodin.

< Ezekiyel 29 >