< Ezekiyel 29 >

1 A shekara ta goma, a wata na goma, a rana ta goma sha biyu, maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Godine desete, desetoga mjeseca, dvanaestoga dana, dođe mi riječ Jahvina:
2 “Ɗan mutum, ka fuskanci Fir’auna sarkin Masar ka kuma yi annabci gāba da shi da dukan Masar.
“Sine čovječji, okreni lice faraonu, kralju egipatskom, i prorokuj protiv njega i protiv sveg Egipta.
3 Yi masa magana ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Ina gāba da kai, Fir’auna sarkin Masar, kai babban mugun dodon ruwa kwance cikin rafuffukanka. Ka ce, “Nilu nawa ne; na yi shi wa kaina.”
Govori i reci: 'Ovako govori Jahve Gospod: Evo me protiv tebe, faraone, kralju egipatski, golemi krokodile što ležiš usred rijeka svojih. Ti reče: 'Rijeke su moje, sebi sam ih načinio.'
4 Amma zan sa ƙugiyoyi a muƙamuƙanka in sa kifin rafuffukanka su manne wa kamɓorinka. Zan jawo ka daga cikin tsakiyar rafuffukanka, da dukan kifayen rafuffukanka, waɗanda suka manne a ƙamborinka,
I zato ću ti kuke zarit' u gubicu i sve ribe rijeka tvojih zalijepiti na krljušti tvoje. Izvući ću te isred rijeka tvojih sa svim ribama rijeka tvojih zalijepljenim na tvoje krljušti.
5 Zan bar ka a cikin hamada, kai da dukan kifin rafuffukanka. Za ka fāɗi a fili ba kuwa za a tattara ka ko a kwashe ba. Zan ba da kai kamar abinci ga namun jeji na duniya da tsuntsayen sararin sama.
Bacit ću u pustinju tebe i sve ribe iz rijeka tvojih. Na tlo ćeš poljsko pasti, nitko te neće podić' ni sahraniti, zvijerima zemaljskim i nebeskim pticama dat ću te za hranu!
6 Ta haka dukan waɗanda suke zama a Masar za su san cewa ni ne Ubangiji. “‘Ka zama sandan iwa domin gidan Isra’ila.
I znat će svi stanovnici Egipta da sam ja Jahve. Jer ti bješe trska za oslonac domu Izraelovu!
7 Sa’ad da suka kama ka da hannuwansu, ka tsattsage, ka kuma buɗu a kafaɗunsu; sa’ad da suka jingina a kanka, sai ka karye, bayansu kuwa ya firgita.
Kad te u ruku uhvatiše, ti se slomi i rane im otvori; a kad se na te osloniše, ti prepuče i bedra im sva izrani.'
8 “‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan kawo takobi a kanka in kashe mutane da dabbobi.
Stog ovako govori Jahve Gospod: 'Gle, dovest ću mač svoj na te, istrijebit ću iz tebe i ljude i stoku!
9 Masar za tă zama kufai. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji. “‘Domin ka ce, “Nilu nawa ne; ni na yi shi,”
Sva će zemlja egipatska pustoš biti i razvalina, i oni će znati da sam ja Jahve!' Jer ti reče: 'Rijeka je moja, sebi je načinih.'
10 saboda haka ina gāba da kai da rafuffukanka, zan kuma maishe ƙasar Masar ta lalace ta kuma zama kango daga Migdol zuwa Aswan, har iyakar Kush.
'Zato evo me na te i na rijeke tvoje da pretvorim zemlju egipatsku u pustinju i pustoš od Migdola do Sevana i do granice etiopske!
11 Ba ƙafar mutum ko ta dabbar da za tă ratsa ta; ba wanda zai zauna a can har shekaru arba’in.
Neće njome više prolaziti noga ljudska ni noga životinjska, ostat će nenaseljena četrdeset godina.
12 Zan mai da ƙasar Masar kufai a cikin ƙasashen da aka ragargaza, biranenta kuma za su zama kango har shekaru arba’in a cikin biranen da aka lalace. Zan watsar da Masarawa a cikin al’ummai in warwatsa su cikin ƙasashe.
Od zemlje ću egipatske načiniti pustoš sred zemalja opustošenih, a gradovi njezini bit će četrdeset godina ruševine među razvaljenim gradovima. I raspršit ću Egipćane među narode i rasijat ću ih po zemljama.'
13 “‘Duk da haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa a ƙarshen shekaru arba’in ɗin zan tattara Masarawa daga al’ummai inda aka warwatsa su.
Jer, ovako govori Jahve Gospod: 'Kad mine četrdeset godina, sakupit ću opet sve Egipćane između naroda kamo bijahu raspršeni.
14 Zan komo da su daga zaman bauta in mai da su zuwa Masar ta Bisa, ƙasarsu ta ainihi. A can za su zama masarauta marar ƙarfi.
Vratit ću izgnanike egipatske, vratit ću ih opet u zemlju Patros, domovinu njihovu, da osnuju ondje slabo kraljevstvo.
15 Za tă zama masarauta mafi rarrauna cikin masarautai, ba kuwa za tă ƙara ɗaga kanta a kan sauran al’ummai ba. Zan sa tă zama marar ƙarfi ƙwarai, har da ba za tă ƙara yin mulkin a kan al’ummai ba.
Ono će biti najmanje od svih kraljevstava, da se više nikad ne digne nad druge narode. Smanjit ću ga da više nikad ne podjarmi drugih naroda
16 Masar ba za tă ƙara zama abin dogara ga mutanen Isra’ila ba amma za tă zama abin tunin zunubinsu na juyawa gare ta don taimako. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji Mai Iko Duka.’”
i da više ne bude uzdanje domu Izraelovu. Nek' mu u pamet doziva grijehe koje bijaše počinio okrećući se za njima. I oni će spoznati da sam ja Jahve.'”
17 A shekara ta ashirin da bakwai, a wata na fari a rana ta farko, maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Godine dvadeset i sedme, prvoga dana prvoga mjeseca, dođe mi riječ Jahvina:
18 “Ɗan mutum, Nebukadnezzar sarkin Babilon ya sa sojojinsa su matsa wa Taya; kowane kai ya koɗe, kowace kafaɗa kuma ta goge. Duk da haka shi da sojojinsa ba su sami wani lada daga matsin da suka yi a kan Taya ba.
“Sine čovječji, kralj babilonski Nabukodonozor krenu s vojskom na velik pohod protiv grada Tira. I svaka glava ogolje i svako se rame odadrije. Ali ni on ni vojska mu ne imahu nikakve dobiti od toga što krenuše na Tir.
19 Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan ba da Masar ga Nebukadnezzar sarkin Babilon, zai washe dukiyarta. Zai kwashe ya washe ƙasar ganima a matsayin abin biyan sojojinsa.
Stoga ovako govori Jahve Gospod: 'Gle, predat ću Nabukodonozoru, kralju babilonskome, zemlju egipatsku. Odnijet će joj blago, nagrabiti plijena i opljačkati je. To će biti plaća vojsci njegovoj.
20 Saboda haka na ba shi Masar a matsayin lada don ƙoƙarinsa domin shi da sojojinsa sun yi wannan domina ne, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
Za trud što na Tir krenu dat ću mu svu zemlju egipatsku, jer za me bijaše radio' - riječ je Jahve Gospoda.
21 “A wannan rana zan sa ƙaho ya tsiro wa gidan Isra’ila, zan kuma buɗe bakinka a cikinsu. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji.”
'U onaj ću dan učiniti da izraste rog domu Izraelovu, a tebi ću usta otvoriti među njima. I znat će da sam ja Jahve.'”

< Ezekiyel 29 >