< Ezekiyel 28 >

1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
RAB bana şöyle seslendi:
2 “Ɗan mutum, ka faɗa wa mai mulkin Taya cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Cikin alfarmar zuciyarka ka ce, “Ni allah ne; ina zama a kan kursiyin allah a tsakiyar tekuna.” Amma kai mutum ne ba allah ba, ko da yake ka ɗauka kana da hikima kamar allah.
“İnsanoğlu, Sur önderine de ki, ‘Egemen RAB şöyle diyor: “‘Gurura kapılıp Ben tanrıyım, Denizlerin bağrında, Tanrı'nın tahtında oturuyorum dedin. Kendini Tanrı sandın, Oysa sen Tanrı değil, insansın.
3 Ka fi Daniyel hikima ne? Ba asirin da yake ɓoye a gare ka?
İşte, Daniel'den daha bilgesin, Kimse senden bir giz saklayamaz.
4 Ta wurin hikimarka da ganewarka ka sami dukiya wa kanka ka kuma tara zinariya da azurfa cikin wuraren ajiyarka.
Bilgeliğin, anlayışın sayesinde, Kendine servet biriktirdin, Hazinelerine altın, gümüş yığdın.
5 Ta wurin dabararka mai girma cikin kasuwanci ka ƙara dukiyarka, kuma saboda dukiyarka zuciyarka ta cika da alfarma.
Ticaretteki üstün becerilerin sayesinde Servetini çoğalttın, Zenginliğin seni gurura sürükledi.
6 “‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Domin ka ɗauka kai mai hikima ne, mai hikima kamar allah,
Bu yüzden Egemen RAB şöyle diyor: Madem kendini Tanrı gibi bilge sandın,
7 zan kawo baƙi a kanka, waɗanda suka fi mugunta cikin sauran al’ummai; za su zāre takubansu a kan kyakkyawar hikimarka su kuma ɓarke darajarka mai walƙiya.
Ben de yabancıları, en acımasız ulusları Üzerine göndereceğim. Bilgeliğinin güzelliğine kılıç çekecek, Görkemini kirletecekler.
8 Za su jefar da kai cikin rami, za ka kuwa yi muguwar mutuwa a tsakiyar tekuna.
Seni ölüm çukuruna indirecekler, Denizlerin bağrında korkunç bir ölümle öleceksin.
9 Za ka iya ce yanzu, “Ni allah ne,” a gaban waɗanda suka kashe ka? Za ka zama mutum kurum, ba allah ba, a hannuwan waɗanda suka kashe ka.
O zaman seni öldürenlerin önünde Ben Tanrı'yım diyecek misin? Seni öldürenlerin elinde Sen Tanrı değil, insansın.
10 Za ka yi mutuwar marar kaciya a hannuwan baƙi. Na faɗa, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”
Yabancıların elinde, Sünnetsizin ölümüyle öleceksin. Egemen RAB böyle diyor.’”
11 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
RAB bana şöyle seslendi:
12 “Ɗan mutum, ka yi makoki domin sarkin Taya ka kuma ce masa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Ka kasance hatimin cikakke, cike da hikima da cikakke a kyau.
“İnsanoğlu, Sur Kralı için bir ağıt yak. Ona diyeceksin ki, ‘Egemen RAB şöyle diyor: “‘Kusursuzlukta örnek biriydin, Bilgeliğin ve güzelliğin eksiksizdi.
13 Ka kasance a Eden, a lambun Allah; aka yi maka ado da kowane dutse mai daraja, yakutu, tofaz, da zumurrudu, kirisolit, onis da yasfa, saffaya, turkuwoyis da beril. Tsare-tsare da shirye-shiryenka an yi su da zinariya ne; a ranar da aka halicce ka an shirya su.
Sen Tanrı'nın bahçesi Aden'deydin. Yakut, topaz, aytaşı, Sarı yakut, oniks, yeşim, Laciverttaşı, firuze, zümrütle, çeşit çeşit değerli taşla bezenmiştin. Kakma ve oyma işlerin hep altındandı. Bunlar yaratıldığın gün hazırlanmışlardı.
14 An shafe ka kamar kerub mai tsaro, gama haka na naɗa ka. Kana a tsattsarkan dutsen Allah; ka yi tafiya a tsakiyar duwatsun wuta.
Meshedilmiş, koruyucu bir Keruv olarak Seni oraya yerleştirdim. Tanrı'nın kutsal dağındaydın, Yanan taşlar arasında dolaştın.
15 Ka kasance marar laifi cikin dukan hanyoyinka daga ranar da aka halicce ka sai da aka sami mugunta a cikinka.
Yaratıldığın günden Sende kötülük bulunana dek Yollarında kusursuzdun.
16 Ta wurin yawan kasuwancinka ka cika da rikici, ka kuma yi zunubi. Saboda haka na kore ka da kunya daga dutsen Allah, na kore ka, ya kerub mai tsaro, daga cikin duwatsun wuta.
Ticaretinin bolluğundan Zorbalıkla doldun Ve günah işledin. Bu yüzden kirli bir şey gibi Seni Tanrı'nın dağından attım, Yanan taşların arasından kovdum, Ey koruyucu Keruv.
17 Zuciyarka ta cika da alfarma saboda kyanka, ka kuma lalace hikimarka saboda darajarka. Saboda haka na jefar da kai zuwa ƙasa; na sa ka zama abin kallo a gaban sarakuna.
Güzelliğinden ötürü Gurura kapıldın, Görkeminden ötürü Bilgeliğini bozdun. Böylece seni yere attım, Kralların önünde seni yüzkarası yaptım.
18 Ta wurin yawan zunubanka da kasuwancinka na cuta ka ƙazantar da wuri mai tsarkinka. Saboda haka na sa wuta ta fito daga cikinka, ta cinye ka, na maishe ka toka a bisa ƙasa a kan idon dukan waɗanda suke kallonka.
İşlediğin pek çok günah Ve ticaretteki hileciliğin yüzünden Kutsal yerlerini kirlettin. Seni yakıp yok edecek Bir ateş çıkardım içinden, Bütün seyredenlerin gözü önünde Seni yeryüzünde küle çevirdim.
19 Dukan al’umman da suka san ka sun giggice saboda masifar da ta auko maka; ka zo ga mummunar ƙarshe ba za ka ƙara kasancewa ba har abada.’”
Seni tanıyan bütün uluslar sana şaştı, Sonun korkunç oldu. Bir daha var olmayacaksın.’”
20 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
RAB bana şöyle seslendi:
21 “Ɗan mutum, ka fuskanci Sidon; ka yi annabci a kanta
“İnsanoğlu, yüzünü Sayda'ya çevir, ona karşı peygamberlik et.
22 ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Ina gāba da ke, ya Sidon, zan sami ɗaukaka a cikinki. Za su san cewa ni ne Ubangiji, sa’ad da na zartar da hukunci a kanta na kuma nuna kaina mai tsarki a cikinta.
Diyeceksin ki, ‘Egemen RAB şöyle diyor: “‘İşte sana karşıyım, ey Sayda, Senin içinde yüceleceğim. Onları cezalandırınca, Kutsallığımı onlara gösterince, Benim RAB olduğumu anlayacaklar.
23 Zan aika da annoba a kanta in kuma sa jini ya zuba a titunanta. Kisassu za su fāɗi a cikinta, da takobi yana gāba da ita a kowane gefe. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji.
Üzerine salgın hastalık gönderecek, Sokaklarında kan akıtacağım. Kentin içinde, her yanında Kılıçla yaralananlar düşüp ölecekler. O zaman benim RAB olduğumu anlayacaklar.’”
24 “‘Mutanen Isra’ila ba za su ƙara kasance da mugayen maƙwabta waɗanda za su zama sarƙaƙƙiya masu zafi da ƙaya mai tsini ba. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji Mai Iko Duka.
“‘İsrail halkını küçümseyen Çevre uluslardan hiçbiri Bir daha İsrail için batan bir çalı, Acıtan bir diken olmayacak. O zaman benim RAB olduğumu anlayacaklar.
25 “‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa sa’ad da na tattara mutanen Isra’ila daga al’ummai inda suke a warwatse, zan nuna kaina mai tsarki a cikinsu a idon al’ummai. Sa’an nan za su zauna a ƙasarsu, wadda na ba wa bawana Yaƙub.
“‘Egemen RAB şöyle diyor: İsrail halkını aralarına dağılmış oldukları uluslardan topladığım, ulusların gözü önünde kutsallığımı gösterdiğim zaman kulum Yakup'a verdiğim kendi ülkelerine yerleşecekler.
26 Za su zauna a can lafiya su kuma gina gidaje su nome gonakin inabi; za su zauna lafiya sa’ad da zan zartar da hukunci a kan dukan maƙwabtansu da suka wulaƙanta su. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji Allahnsu.’”
Orada güvenlik içinde yaşayacak, evler yapacak, bağlar dikecekler. Onları küçümseyen bütün çevre ulusları cezalandırdığımda güvenlik içinde yaşayacaklar. O zaman benim Tanrıları RAB olduğumu anlayacaklar.’”

< Ezekiyel 28 >