< Ezekiyel 28 >
1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Beseda Gospodova je ponovno prišla k meni, rekoč:
2 “Ɗan mutum, ka faɗa wa mai mulkin Taya cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Cikin alfarmar zuciyarka ka ce, “Ni allah ne; ina zama a kan kursiyin allah a tsakiyar tekuna.” Amma kai mutum ne ba allah ba, ko da yake ka ɗauka kana da hikima kamar allah.
»Človeški sin, povej princu Tira: ›Tako govori Gospod Bog: ›Ker je tvoje srce povzdignjeno in si rekel: ›Jaz sem Bog, sedim na Božjem sedežu v sredi morij; ‹ vendar si človek in ne Bog, čeprav si svoje srce postavljal kakor srce Boga.
3 Ka fi Daniyel hikima ne? Ba asirin da yake ɓoye a gare ka?
Glej, modrejši si kakor Daniel; ni skrivnosti, ki jo lahko skrijejo pred teboj.
4 Ta wurin hikimarka da ganewarka ka sami dukiya wa kanka ka kuma tara zinariya da azurfa cikin wuraren ajiyarka.
S svojo modrostjo in s svojim razumevanjem si si pridobil bogastva in v svojih zakladnicah si si pridobil zlato in srebro.
5 Ta wurin dabararka mai girma cikin kasuwanci ka ƙara dukiyarka, kuma saboda dukiyarka zuciyarka ta cika da alfarma.
S svojo veliko modrostjo in s svojim preprodajanjem si povečal svoja bogastva in tvoje srce je povzdignjeno zaradi tvojih bogastev.‹
6 “‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Domin ka ɗauka kai mai hikima ne, mai hikima kamar allah,
Zato tako govori Gospod Bog: ›Ker si svoje srce postavil kakor srce Boga;
7 zan kawo baƙi a kanka, waɗanda suka fi mugunta cikin sauran al’ummai; za su zāre takubansu a kan kyakkyawar hikimarka su kuma ɓarke darajarka mai walƙiya.
glej, zato bom nadte privedel tujce, strašne izmed narodov. Svoje meče bodo izvlekli zoper lepoto tvoje modrosti in omadeževali bodo tvoj sijaj.
8 Za su jefar da kai cikin rami, za ka kuwa yi muguwar mutuwa a tsakiyar tekuna.
Privedli te bodo dol do jame in umrl boš [s] smrtmi tistih, ki so umorjeni v sredi morij.
9 Za ka iya ce yanzu, “Ni allah ne,” a gaban waɗanda suka kashe ka? Za ka zama mutum kurum, ba allah ba, a hannuwan waɗanda suka kashe ka.
Ali boš še govoril pred tistim, ki te ubija: ›Jaz sem Bog?‹ Toda ti boš mož in ne Bog, v roki tistega, ki te ubija.
10 Za ka yi mutuwar marar kaciya a hannuwan baƙi. Na faɗa, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”
Umrl boš s smrtmi neobrezancev, po roki tujcev, kajti jaz sem to govoril, ‹ govori Gospod Bog.«
11 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Poleg tega je prišla k meni Gospodova beseda, rekoč:
12 “Ɗan mutum, ka yi makoki domin sarkin Taya ka kuma ce masa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Ka kasance hatimin cikakke, cike da hikima da cikakke a kyau.
»Človeški sin, vzdigni žalostinko nad kraljem Tira in mu reci: ›Tako govori Gospod Bog: ›Ti pečatiš vsoto, poln si modrosti in popoln v lepoti.
13 Ka kasance a Eden, a lambun Allah; aka yi maka ado da kowane dutse mai daraja, yakutu, tofaz, da zumurrudu, kirisolit, onis da yasfa, saffaya, turkuwoyis da beril. Tsare-tsare da shirye-shiryenka an yi su da zinariya ne; a ranar da aka halicce ka an shirya su.
Bil si v Raju, Božjem vrtu; vsak dragocen kamen je bil tvoje pokrivalo: sardij, topaz in diamant, beril, oniks in jaspis, safir, smaragd, granat in zlato. Izdelava tvojih bobničev in tvojih piščali je bila pripravljena v tebi na dan, ko si bil ustvarjen.
14 An shafe ka kamar kerub mai tsaro, gama haka na naɗa ka. Kana a tsattsarkan dutsen Allah; ka yi tafiya a tsakiyar duwatsun wuta.
Ti si maziljen kerub, ki zaslanja; in jaz sem te tako postavil. Bil si na sveti gori Boga; hodil si gor in dol v sredi ognjenih kamnov.
15 Ka kasance marar laifi cikin dukan hanyoyinka daga ranar da aka halicce ka sai da aka sami mugunta a cikinka.
Bil si popoln na svojih poteh, od dneva, ko si bil ustvarjen, dokler ni bila v tebi najdena krivičnost.
16 Ta wurin yawan kasuwancinka ka cika da rikici, ka kuma yi zunubi. Saboda haka na kore ka da kunya daga dutsen Allah, na kore ka, ya kerub mai tsaro, daga cikin duwatsun wuta.
Z množico tvojih trgovanj so tvojo sredo napolnili z nasiljem in si grešil, zato te bom pahnil, kot oskrunjenega iz Božje gore in te bom uničil, oh zaslanjajoči kerub, iz srede ognjenih kamnov.
17 Zuciyarka ta cika da alfarma saboda kyanka, ka kuma lalace hikimarka saboda darajarka. Saboda haka na jefar da kai zuwa ƙasa; na sa ka zama abin kallo a gaban sarakuna.
Tvoje srce se je povzdignilo zaradi tvoje lepote, svojo modrost si izpridil zaradi svojega sijaja. Jaz te bom vrgel na tla, jaz te bom položil pred kralje, da te bodo lahko gledali.
18 Ta wurin yawan zunubanka da kasuwancinka na cuta ka ƙazantar da wuri mai tsarkinka. Saboda haka na sa wuta ta fito daga cikinka, ta cinye ka, na maishe ka toka a bisa ƙasa a kan idon dukan waɗanda suke kallonka.
Svoja svetišča si omadeževal z množico svojih krivičnosti, s krivičnostjo svojega preprodajanja; zato bom privedel ogenj iz tvoje srede; ta te bo požrl, jaz pa te bom spremenil v pepel na zemlji, pred očmi vseh tistih, ki te gledajo.
19 Dukan al’umman da suka san ka sun giggice saboda masifar da ta auko maka; ka zo ga mummunar ƙarshe ba za ka ƙara kasancewa ba har abada.’”
In tisti, ki te med ljudstvom poznajo, bodo osupli nad teboj. Strahota boš in nikoli te ne bo več.‹«
20 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Ponovno je prišla k meni Gospodova beseda, rekoč:
21 “Ɗan mutum, ka fuskanci Sidon; ka yi annabci a kanta
»Človeški sin, naravnaj svoj obraz proti Sidónu in prerokuj zoper njega
22 ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Ina gāba da ke, ya Sidon, zan sami ɗaukaka a cikinki. Za su san cewa ni ne Ubangiji, sa’ad da na zartar da hukunci a kanta na kuma nuna kaina mai tsarki a cikinta.
ter reci: ›Tako govori Gospod Bog: ›Glej, zoper tebe sem, oh Sidón; in proslavljen bom v tvoji sredi in vedeli bodo, da jaz sem Gospod, ko bom izvršil sodbe v njem in bom posvečen v njem.
23 Zan aika da annoba a kanta in kuma sa jini ya zuba a titunanta. Kisassu za su fāɗi a cikinta, da takobi yana gāba da ita a kowane gefe. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji.
Kajti vanj bom poslal kužno bolezen in kri na njegove ulice; in ranjeni bodo sojeni v njegovi sredi z mečem na njem, na vsaki strani; in spoznali bodo, da jaz sem Gospod.
24 “‘Mutanen Isra’ila ba za su ƙara kasance da mugayen maƙwabta waɗanda za su zama sarƙaƙƙiya masu zafi da ƙaya mai tsini ba. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji Mai Iko Duka.
In ne bo več bodečega osata nad Izraelovo hišo niti kakršnegakoli bolečega trna od vseh, ki so okoli njih, ki so jih prezirali; in spoznali bodo, da jaz sem Gospod Bog.‹
25 “‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa sa’ad da na tattara mutanen Isra’ila daga al’ummai inda suke a warwatse, zan nuna kaina mai tsarki a cikinsu a idon al’ummai. Sa’an nan za su zauna a ƙasarsu, wadda na ba wa bawana Yaƙub.
Tako govori Gospod Bog: ›Ko bom Izraelovo hišo zbral izmed ljudstev, med katere so razkropljeni in bom posvečen v njih v očeh poganov, potem bodo prebivali v svoji deželi, ki sem jo dal svojemu služabniku Jakobu.
26 Za su zauna a can lafiya su kuma gina gidaje su nome gonakin inabi; za su zauna lafiya sa’ad da zan zartar da hukunci a kan dukan maƙwabtansu da suka wulaƙanta su. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji Allahnsu.’”
In v njej bodo varno prebivali in gradili bodo hiše in sadili vinograde; da, prebivali bodo z zaupanjem, ko izvršim sodbe nad vsemi tistimi, ki jih prezirajo naokoli njih; in spoznali bodo, da jaz sem Gospod, njihov Bog.‹«