< Ezekiyel 28 >

1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Et la parole du Seigneur me fut adressée, disant:
2 “Ɗan mutum, ka faɗa wa mai mulkin Taya cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Cikin alfarmar zuciyarka ka ce, “Ni allah ne; ina zama a kan kursiyin allah a tsakiyar tekuna.” Amma kai mutum ne ba allah ba, ko da yake ka ɗauka kana da hikima kamar allah.
Fils d’un homme, dis au prince de Tyr: Voici ce que dit le Seigneur Dieu: À cause que ton cœur s’est élevé, et que tu as dit: Moi je suis un Dieu, je suis assis sur le trône d’un Dieu au milieu de la mer, lorsque tu n’es qu’un homme et non un Dieu; parce que tu as posé ton cœur comme le cœur d’un Dieu;
3 Ka fi Daniyel hikima ne? Ba asirin da yake ɓoye a gare ka?
Voilà que tu es plus sage que Daniel; aucun secret n’est caché pour toi.
4 Ta wurin hikimarka da ganewarka ka sami dukiya wa kanka ka kuma tara zinariya da azurfa cikin wuraren ajiyarka.
Par la sagesse et ta prudence tu t’es créé de la puissance, et tu as amassé de l’or et de l’argent dans tes trésors.
5 Ta wurin dabararka mai girma cikin kasuwanci ka ƙara dukiyarka, kuma saboda dukiyarka zuciyarka ta cika da alfarma.
Par la grandeur de ta sagesse, et par ton commerce tu as multiplié ta puissance, et ton cœur s’est élevé dans ta force.
6 “‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Domin ka ɗauka kai mai hikima ne, mai hikima kamar allah,
À cause de cela, voici ce que dit le Seigneur Dieu: Parce que ton cœur s’est élevé comme le cœur d’un Dieu,
7 zan kawo baƙi a kanka, waɗanda suka fi mugunta cikin sauran al’ummai; za su zāre takubansu a kan kyakkyawar hikimarka su kuma ɓarke darajarka mai walƙiya.
À cause de cela, voici que moi j’amènerai sur toi des étrangers, les plus forts d’entre les nations, et ils tireront leurs glaives sur la beauté de ta sagesse, et ils souilleront ta splendeur.
8 Za su jefar da kai cikin rami, za ka kuwa yi muguwar mutuwa a tsakiyar tekuna.
Ils te tueront et te précipiteront dans la fosse, et tu mourras dans la destruction des tués au milieu de la mer.
9 Za ka iya ce yanzu, “Ni allah ne,” a gaban waɗanda suka kashe ka? Za ka zama mutum kurum, ba allah ba, a hannuwan waɗanda suka kashe ka.
Est-ce que tu parleras, disant: Je suis un Dieu, devant ceux qui te tueront; lorsque tu n’es qu’un homme et non un Dieu, dans la main de ceux qui te feront mourir?
10 Za ka yi mutuwar marar kaciya a hannuwan baƙi. Na faɗa, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”
Tu mourras de la mort des incirconcis par la main des étrangers, parce que c’est moi qui ai parlé, dit le Seigneur Dieu.
11 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Et la parole du Seigneur me fut adressée, disant: Fils d’un homme, fais entendre un chant de deuil sur le roi de Tyr,
12 “Ɗan mutum, ka yi makoki domin sarkin Taya ka kuma ce masa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Ka kasance hatimin cikakke, cike da hikima da cikakke a kyau.
Et tu lui diras: Voici ce que dit le Seigneur Dieu: Toi le sceau de la ressemblance de Dieu, toi plein de sagesse et parfait en beauté,
13 Ka kasance a Eden, a lambun Allah; aka yi maka ado da kowane dutse mai daraja, yakutu, tofaz, da zumurrudu, kirisolit, onis da yasfa, saffaya, turkuwoyis da beril. Tsare-tsare da shirye-shiryenka an yi su da zinariya ne; a ranar da aka halicce ka an shirya su.
Tu as été dans les délices du paradis de Dieu; toute pierre précieuse était ta couverture: la sardoine, la topaze, le jaspe, la chrysolithe, l’onyx, le béryl, le saphir, l’escarboucle, l’émeraude; l’or servait à relever ta beauté; et tes bijoux percés ont été préparés pour le jour auquel tu as été créé.
14 An shafe ka kamar kerub mai tsaro, gama haka na naɗa ka. Kana a tsattsarkan dutsen Allah; ka yi tafiya a tsakiyar duwatsun wuta.
Tu étais un chérubin aux ailes étendues et protecteur; et je t’ai établi sur la montagne sainte de Dieu; et tu as marché au milieu de pierres étincelantes comme le feu.
15 Ka kasance marar laifi cikin dukan hanyoyinka daga ranar da aka halicce ka sai da aka sami mugunta a cikinka.
Tu as été parfait dans tes voies depuis le jour de ta création jusqu’à ce que l’iniquité a été trouvée en toi.
16 Ta wurin yawan kasuwancinka ka cika da rikici, ka kuma yi zunubi. Saboda haka na kore ka da kunya daga dutsen Allah, na kore ka, ya kerub mai tsaro, daga cikin duwatsun wuta.
Dans la multiplication de ton commerce ton intérieur a été rempli d’iniquité, et tu as péché; et je t’ai chassé de la montagne de Dieu, et je t’ai exterminé, ô chérubin, couvrant le propitiatoire du milieu des pierres étincelantes comme le feu.
17 Zuciyarka ta cika da alfarma saboda kyanka, ka kuma lalace hikimarka saboda darajarka. Saboda haka na jefar da kai zuwa ƙasa; na sa ka zama abin kallo a gaban sarakuna.
Et ton cœur s’est élevé dans ta beauté: tu as perdu ta sagesse dans ta beauté; je t’ai jeté sur la terre, et je t’ai exposé devant la face des rois, afin qu’ils t’aperçussent.
18 Ta wurin yawan zunubanka da kasuwancinka na cuta ka ƙazantar da wuri mai tsarkinka. Saboda haka na sa wuta ta fito daga cikinka, ta cinye ka, na maishe ka toka a bisa ƙasa a kan idon dukan waɗanda suke kallonka.
Dans la multitude de tes iniquités, et dans l’iniquité de ton commerce tu as souillé ton sanctuaire: je ferai donc sortir du milieu de toi un feu qui te dévorera, et je te réduirai en cendre sur la terre en présence de tous ceux qui te verront.
19 Dukan al’umman da suka san ka sun giggice saboda masifar da ta auko maka; ka zo ga mummunar ƙarshe ba za ka ƙara kasancewa ba har abada.’”
Tous ceux qui te verront parmi les nations seront frappés de stupeur sur toi; tu es devenu comme un néant, et tu ne seras plus à jamais.
20 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Et la parole du Seigneur me fut adressée, disant:
21 “Ɗan mutum, ka fuskanci Sidon; ka yi annabci a kanta
Fils d’un homme, tourne ton visage contre Sidon; et tu prophétiseras sur elle,
22 ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Ina gāba da ke, ya Sidon, zan sami ɗaukaka a cikinki. Za su san cewa ni ne Ubangiji, sa’ad da na zartar da hukunci a kanta na kuma nuna kaina mai tsarki a cikinta.
Et tu diras: Voici ce que dit le Seigneur Dieu: Voilà que je viens vers toi, Sidon, et je serai glorifié au milieu de toi; et ils sauront que je suis le Seigneur, lorsque j’aurai exercé sur elle des jugements, et que j’aurai été sanctifié en elle.
23 Zan aika da annoba a kanta in kuma sa jini ya zuba a titunanta. Kisassu za su fāɗi a cikinta, da takobi yana gāba da ita a kowane gefe. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji.
Et je lui enverrai la peste et le sang sur ses places publiques; et les tués tomberont au milieu d’elles par le glaive qui frappera tout autour; et ils sauront que je suis le Seigneur.
24 “‘Mutanen Isra’ila ba za su ƙara kasance da mugayen maƙwabta waɗanda za su zama sarƙaƙƙiya masu zafi da ƙaya mai tsini ba. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji Mai Iko Duka.
Et elle ne sera plus pour la maison d’Israël une pierre d’achoppement, et un sujet d’amertume, et une épine causant de la douleur de tous côtés à ceux qui l’environnent et qui la combattent; et ils sauront que je suis le Seigneur Dieu.
25 “‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa sa’ad da na tattara mutanen Isra’ila daga al’ummai inda suke a warwatse, zan nuna kaina mai tsarki a cikinsu a idon al’ummai. Sa’an nan za su zauna a ƙasarsu, wadda na ba wa bawana Yaƙub.
Voici ce que dit le Seigneur Dieu: Lorsque j’aurai rassemblé la maison d’Israël du milieu des peuples parmi lesquels ils ont été dispersés, je serai sanctifié parmi eux devant les nations; et ils habiteront dans leur terre, que j’ai donnée à mon serviteur Jacob.
26 Za su zauna a can lafiya su kuma gina gidaje su nome gonakin inabi; za su zauna lafiya sa’ad da zan zartar da hukunci a kan dukan maƙwabtansu da suka wulaƙanta su. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji Allahnsu.’”
Et ils y habiteront avec sécurité, et ils bâtiront des maisons, et ils planteront des vignes, et ils habiteront avec confiance, lorsque j’aurai exercé des jugements sur tous ceux qui les environnent et qui les combattent, et ils sauront que je suis le Seigneur leur Dieu.

< Ezekiyel 28 >