< Ezekiyel 28 >
1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
And it came [the] word of Yahweh to me saying.
2 “Ɗan mutum, ka faɗa wa mai mulkin Taya cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Cikin alfarmar zuciyarka ka ce, “Ni allah ne; ina zama a kan kursiyin allah a tsakiyar tekuna.” Amma kai mutum ne ba allah ba, ko da yake ka ɗauka kana da hikima kamar allah.
O son of humankind say to [the] ruler of Tyre thus he says - [the] Lord Yahweh because it has been haughty heart your and you have said [am] a god I [the] seat of gods I sit in [the] heart of [the] seas and you [are] a human being and not a god and you have made heart your like [the] heart of a god.
3 Ka fi Daniyel hikima ne? Ba asirin da yake ɓoye a gare ka?
There! [are] wise you (more than Daniel *Q(K)*) any secret [thing] not people hold dark from you.
4 Ta wurin hikimarka da ganewarka ka sami dukiya wa kanka ka kuma tara zinariya da azurfa cikin wuraren ajiyarka.
By wisdom your and by understanding your you have acquired for yourself wealth and you have acquired gold and silver in treasuries your.
5 Ta wurin dabararka mai girma cikin kasuwanci ka ƙara dukiyarka, kuma saboda dukiyarka zuciyarka ta cika da alfarma.
By [the] greatness of skill your by trading your you have increased wealth your and it has been haughty heart your in wealth your.
6 “‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Domin ka ɗauka kai mai hikima ne, mai hikima kamar allah,
Therefore thus he says [the] Lord Yahweh because making you heart your like [the] heart of a god.
7 zan kawo baƙi a kanka, waɗanda suka fi mugunta cikin sauran al’ummai; za su zāre takubansu a kan kyakkyawar hikimarka su kuma ɓarke darajarka mai walƙiya.
Therefore here I [am] about to bring on you strangers ruthless [ones] of nations and they will draw swords their on [the] beauty of wisdom your and they will profane splendor your.
8 Za su jefar da kai cikin rami, za ka kuwa yi muguwar mutuwa a tsakiyar tekuna.
To the pit they will bring down you and you will die [the] death of [the] slain in [the] heart of [the] seas.
9 Za ka iya ce yanzu, “Ni allah ne,” a gaban waɗanda suka kashe ka? Za ka zama mutum kurum, ba allah ba, a hannuwan waɗanda suka kashe ka.
¿ Really will you say [am] a god I before killer your and you [are] a human being and not a god in [the] hand of [those who] pierce you.
10 Za ka yi mutuwar marar kaciya a hannuwan baƙi. Na faɗa, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”
[the] deaths of Uncircumcised [men] you will die by [the] hand of strangers for I I have spoken [the] utterance of [the] Lord Yahweh.
11 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
And it came [the] word of Yahweh to me saying.
12 “Ɗan mutum, ka yi makoki domin sarkin Taya ka kuma ce masa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Ka kasance hatimin cikakke, cike da hikima da cikakke a kyau.
O son of humankind take up a lamentation on [the] king of Tyre and you will say to him thus he says [the] Lord Yahweh you [were one who] seals an example full of wisdom and perfect of beauty.
13 Ka kasance a Eden, a lambun Allah; aka yi maka ado da kowane dutse mai daraja, yakutu, tofaz, da zumurrudu, kirisolit, onis da yasfa, saffaya, turkuwoyis da beril. Tsare-tsare da shirye-shiryenka an yi su da zinariya ne; a ranar da aka halicce ka an shirya su.
In Eden [the] garden of God you were [was] every stone precious covering your ruby topaz and emerald chrysolite onyx and jasper sapphire turquoise and beryl and gold [the] workmanship of tambourines your and settings your on you on [the] day are created you they were prepared.
14 An shafe ka kamar kerub mai tsaro, gama haka na naɗa ka. Kana a tsattsarkan dutsen Allah; ka yi tafiya a tsakiyar duwatsun wuta.
You [were] a cherub of expansion [one which] covers and I appointed you on [the] mountain of [the] holiness of God you were in [the] middle of stones of fire you walked about.
15 Ka kasance marar laifi cikin dukan hanyoyinka daga ranar da aka halicce ka sai da aka sami mugunta a cikinka.
[were] blameless You in ways your from [the] day are created you until it was found unrighteousness in you.
16 Ta wurin yawan kasuwancinka ka cika da rikici, ka kuma yi zunubi. Saboda haka na kore ka da kunya daga dutsen Allah, na kore ka, ya kerub mai tsaro, daga cikin duwatsun wuta.
In [the] abundance of trading your people filled [the] middle of you violence and you sinned and I profaned you from [the] mountain of God and I destroyed you O cherub [one which] covers from [the] middle of [the] stones of fire.
17 Zuciyarka ta cika da alfarma saboda kyanka, ka kuma lalace hikimarka saboda darajarka. Saboda haka na jefar da kai zuwa ƙasa; na sa ka zama abin kallo a gaban sarakuna.
It was haughty heart your in beauty your you perverted wisdom your on splendor your on [the] ground I threw you before kings I put you to look on you.
18 Ta wurin yawan zunubanka da kasuwancinka na cuta ka ƙazantar da wuri mai tsarkinka. Saboda haka na sa wuta ta fito daga cikinka, ta cinye ka, na maishe ka toka a bisa ƙasa a kan idon dukan waɗanda suke kallonka.
From [the] greatness of iniquities your by [the] unrighteousness of trading your you profaned sanctuaries your and I brought out fire from [the] midst of you it it consumed you and I made you into ash[es] on the ground to [the] eyes of all [those who] saw you.
19 Dukan al’umman da suka san ka sun giggice saboda masifar da ta auko maka; ka zo ga mummunar ƙarshe ba za ka ƙara kasancewa ba har abada.’”
All [those who] knew you among the peoples they were appalled on you terrors you became and there not [will be] you until perpetuity.
20 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
And it came [the] word of Yahweh to me saying.
21 “Ɗan mutum, ka fuskanci Sidon; ka yi annabci a kanta
O son of humankind set face your to Sidon and prophesy on it.
22 ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Ina gāba da ke, ya Sidon, zan sami ɗaukaka a cikinki. Za su san cewa ni ne Ubangiji, sa’ad da na zartar da hukunci a kanta na kuma nuna kaina mai tsarki a cikinta.
And you will say thus he says [the] Lord Yahweh here I [am] on you O Sidon and I will gain glory in [the] midst of you and people will know that I [am] Yahweh when bring about I on it judgments and I will show myself holy in it.
23 Zan aika da annoba a kanta in kuma sa jini ya zuba a titunanta. Kisassu za su fāɗi a cikinta, da takobi yana gāba da ita a kowane gefe. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji.
And I will send on it a pestilence and blood in streets its and it will fall [the] slain in [the] midst of it by [the] sword on it from round about and they will know that I [am] Yahweh.
24 “‘Mutanen Isra’ila ba za su ƙara kasance da mugayen maƙwabta waɗanda za su zama sarƙaƙƙiya masu zafi da ƙaya mai tsini ba. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji Mai Iko Duka.
And not it will belong again to [the] house of Israel a brier [which] pricks and a thorn [which] causes pain from all around them who despise them and they will know that I [am the] Lord Yahweh.
25 “‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa sa’ad da na tattara mutanen Isra’ila daga al’ummai inda suke a warwatse, zan nuna kaina mai tsarki a cikinsu a idon al’ummai. Sa’an nan za su zauna a ƙasarsu, wadda na ba wa bawana Yaƙub.
Thus he says [the] Lord Yahweh when gather I - [the] house of Israel from the peoples which they have been scattered among them and I will show myself holy among them to [the] eyes of the nations and they will dwell on own land their which I gave to servant my to Jacob.
26 Za su zauna a can lafiya su kuma gina gidaje su nome gonakin inabi; za su zauna lafiya sa’ad da zan zartar da hukunci a kan dukan maƙwabtansu da suka wulaƙanta su. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji Allahnsu.’”
And they will dwell on it to security and they will build houses and they will plant vineyards and they will dwell to security when bring about I judgments on all those [who] despise them from around them and they will know that I [am] Yahweh God their.