< Ezekiyel 28 >
1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
The word of Jehovah came again to me, saying:
2 “Ɗan mutum, ka faɗa wa mai mulkin Taya cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Cikin alfarmar zuciyarka ka ce, “Ni allah ne; ina zama a kan kursiyin allah a tsakiyar tekuna.” Amma kai mutum ne ba allah ba, ko da yake ka ɗauka kana da hikima kamar allah.
Son of man, say to the prince of Tyre, Thus saith the Lord Jehovah: Because thy heart is lifted up, and thou hast said, “I am a god, I sit in the seat of a god, in the midst of the seas”; and though thou art man, not God, yet settest thy heart as the heart of a god, —
3 Ka fi Daniyel hikima ne? Ba asirin da yake ɓoye a gare ka?
behold, thou art wiser than Daniel; there is no secret which can be hidden from thee;
4 Ta wurin hikimarka da ganewarka ka sami dukiya wa kanka ka kuma tara zinariya da azurfa cikin wuraren ajiyarka.
by thy wisdom and by thine understanding thou hast gotten thee riches, and hast gotten gold and silver in thy treasures;
5 Ta wurin dabararka mai girma cikin kasuwanci ka ƙara dukiyarka, kuma saboda dukiyarka zuciyarka ta cika da alfarma.
by thy great wisdom, by thy traffic, thou hast increased thy riches, and thy heart is lifted up because of thy wealth, —
6 “‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Domin ka ɗauka kai mai hikima ne, mai hikima kamar allah,
therefore thus saith the Lord Jehovah: Because thou settest thy heart as the heart of a god, therefore,
7 zan kawo baƙi a kanka, waɗanda suka fi mugunta cikin sauran al’ummai; za su zāre takubansu a kan kyakkyawar hikimarka su kuma ɓarke darajarka mai walƙiya.
behold, I will bring upon thee strangers, the terrible of the nations; and they shall draw their swords against the beauty of thy wisdom, and they shall defile thy brightness.
8 Za su jefar da kai cikin rami, za ka kuwa yi muguwar mutuwa a tsakiyar tekuna.
They shall bring thee down to the pit, and thou shalt die the death of the slain, in the midst of the seas.
9 Za ka iya ce yanzu, “Ni allah ne,” a gaban waɗanda suka kashe ka? Za ka zama mutum kurum, ba allah ba, a hannuwan waɗanda suka kashe ka.
Wilt thou yet say, “I am a god,” before him that slayeth thee? Thou shalt be man, and not God, in the hand of him that slayeth thee.
10 Za ka yi mutuwar marar kaciya a hannuwan baƙi. Na faɗa, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”
Thou shalt die the death of the uncircumcised, by the hand of strangers; for I have spoken it, saith the Lord Jehovah.
11 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Moreover, the word of Jehovah came to me, saying:
12 “Ɗan mutum, ka yi makoki domin sarkin Taya ka kuma ce masa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Ka kasance hatimin cikakke, cike da hikima da cikakke a kyau.
Son of man, take up a lamentation upon the king of Tyre, and say to him, Thus saith the Lord Jehovah: —Thou wast a finished signet, Full of wisdom and perfect in beauty;
13 Ka kasance a Eden, a lambun Allah; aka yi maka ado da kowane dutse mai daraja, yakutu, tofaz, da zumurrudu, kirisolit, onis da yasfa, saffaya, turkuwoyis da beril. Tsare-tsare da shirye-shiryenka an yi su da zinariya ne; a ranar da aka halicce ka an shirya su.
In Eden, the garden of God, thou didst dwell; Every precious stone was thy covering, The ruby, the topaz, and the diamond, The chrysolite, the onyx, and the jasper, The sapphire, the carbuncle, and the emerald, and gold. The workmanship of thy jewel-holes was within thee; On the day when thou wast born were they prepared.
14 An shafe ka kamar kerub mai tsaro, gama haka na naɗa ka. Kana a tsattsarkan dutsen Allah; ka yi tafiya a tsakiyar duwatsun wuta.
Thou wast an outspread, covering cherub; I set thee upon the holy mountain of God; Thou didst walk in the midst of the stones of fire.
15 Ka kasance marar laifi cikin dukan hanyoyinka daga ranar da aka halicce ka sai da aka sami mugunta a cikinka.
Thou wast prosperous in thy ways from the day that thou wast born Until iniquity was found in thee.
16 Ta wurin yawan kasuwancinka ka cika da rikici, ka kuma yi zunubi. Saboda haka na kore ka da kunya daga dutsen Allah, na kore ka, ya kerub mai tsaro, daga cikin duwatsun wuta.
Through the abundance of thy merchandise thou art full of injustice; And thou hast sinned; Therefore I will cast thee as profane out of the mountain of God, And I will destroy thee, O covering cherub, from the midst of the stones of fire.
17 Zuciyarka ta cika da alfarma saboda kyanka, ka kuma lalace hikimarka saboda darajarka. Saboda haka na jefar da kai zuwa ƙasa; na sa ka zama abin kallo a gaban sarakuna.
Thy heart was lifted up because of thy beauty; Thou hast corrupted thy wisdom by reason of thy splendor; I will cast thee to the ground; I will give thee up to kings to be their gazing-stock.
18 Ta wurin yawan zunubanka da kasuwancinka na cuta ka ƙazantar da wuri mai tsarkinka. Saboda haka na sa wuta ta fito daga cikinka, ta cinye ka, na maishe ka toka a bisa ƙasa a kan idon dukan waɗanda suke kallonka.
By the multitude of thine iniquities, by the unrighteousness of thy traffic, Thou hast defiled thy sanctuaries. Therefore will I bring forth a fire from the midst of thee, which shall devour thee, And I will bring thee to ashes upon the earth, In the sight of all them that behold thee.
19 Dukan al’umman da suka san ka sun giggice saboda masifar da ta auko maka; ka zo ga mummunar ƙarshe ba za ka ƙara kasancewa ba har abada.’”
All they that know thee among the nations shall be astonished at thee; Thou art become a desolation, and shalt exist no more forever.
20 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Again the word of Jehovah came to me, saying:
21 “Ɗan mutum, ka fuskanci Sidon; ka yi annabci a kanta
Son of man, set thy face against Sidon, and prophesy against her,
22 ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Ina gāba da ke, ya Sidon, zan sami ɗaukaka a cikinki. Za su san cewa ni ne Ubangiji, sa’ad da na zartar da hukunci a kanta na kuma nuna kaina mai tsarki a cikinta.
and say, Thus saith the Lord Jehovah: Behold, I am against thee, O Sidon, and I will be glorified in the midst of thee, and they shall know that I am Jehovah, when I execute judgments in her, and am sanctified in her.
23 Zan aika da annoba a kanta in kuma sa jini ya zuba a titunanta. Kisassu za su fāɗi a cikinta, da takobi yana gāba da ita a kowane gefe. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji.
I will send upon her pestilence, and blood into her streets, and the wounded shall fall in the midst of her by the sword which is against her on every side; and they shall know that I am Jehovah.
24 “‘Mutanen Isra’ila ba za su ƙara kasance da mugayen maƙwabta waɗanda za su zama sarƙaƙƙiya masu zafi da ƙaya mai tsini ba. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji Mai Iko Duka.
And there shall be no more to the house of Israel a pricking brier, or a grieving thorn of all that are round about them, that despised them; and they shall know that I am the Lord Jehovah.
25 “‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa sa’ad da na tattara mutanen Isra’ila daga al’ummai inda suke a warwatse, zan nuna kaina mai tsarki a cikinsu a idon al’ummai. Sa’an nan za su zauna a ƙasarsu, wadda na ba wa bawana Yaƙub.
Thus saith the Lord Jehovah: When I shall gather the house of Israel from the nations among which they are scattered, then shall I be sanctified through them in the sight of the nations, and they shall dwell in the land which I gave to my servant Jacob.
26 Za su zauna a can lafiya su kuma gina gidaje su nome gonakin inabi; za su zauna lafiya sa’ad da zan zartar da hukunci a kan dukan maƙwabtansu da suka wulaƙanta su. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji Allahnsu.’”
They shall dwell therein securely, and shall build houses, and plant vineyards, yea, they shall dwell securely when I have executed judgments on all that despised them round about; and they shall know that I am Jehovah, their God.