< Ezekiyel 28 >
1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
And the word of the Lord came to me, saying,
2 “Ɗan mutum, ka faɗa wa mai mulkin Taya cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Cikin alfarmar zuciyarka ka ce, “Ni allah ne; ina zama a kan kursiyin allah a tsakiyar tekuna.” Amma kai mutum ne ba allah ba, ko da yake ka ɗauka kana da hikima kamar allah.
And you, son of man, say to the prince of Tyrus, Thus says the Lord; Because your heart has been exalted, and you have said, I am God, I have inhabited the dwelling of God in the heart of the sea; yet you are man and not God, though you have set your heart as the heart of God:
3 Ka fi Daniyel hikima ne? Ba asirin da yake ɓoye a gare ka?
are you wiser than Daniel? or have not the wise instructed you with their knowledge?
4 Ta wurin hikimarka da ganewarka ka sami dukiya wa kanka ka kuma tara zinariya da azurfa cikin wuraren ajiyarka.
Hast you gained power for yourself by your [own] knowledge or your [own] prudence, and [gotten] gold and silver in your treasures?
5 Ta wurin dabararka mai girma cikin kasuwanci ka ƙara dukiyarka, kuma saboda dukiyarka zuciyarka ta cika da alfarma.
By your abundant knowledge and your traffic you have multiplied your power; your heart has been lifted up by your power.
6 “‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Domin ka ɗauka kai mai hikima ne, mai hikima kamar allah,
Therefore thus says the Lord; Since you have set your heart as the hart of God;
7 zan kawo baƙi a kanka, waɗanda suka fi mugunta cikin sauran al’ummai; za su zāre takubansu a kan kyakkyawar hikimarka su kuma ɓarke darajarka mai walƙiya.
because of this, behold, I [will] bring on you strange plagues from the nations; and they shall draw their swords against you, and against the beauty of your knowledge,
8 Za su jefar da kai cikin rami, za ka kuwa yi muguwar mutuwa a tsakiyar tekuna.
and they shall bring down your beauty to destruction. And they shall bring you down; and you shall die the death of the slain in the heart of the sea.
9 Za ka iya ce yanzu, “Ni allah ne,” a gaban waɗanda suka kashe ka? Za ka zama mutum kurum, ba allah ba, a hannuwan waɗanda suka kashe ka.
Will you indeed say, I am God, before them that kill you? whereas you are man, and not God.
10 Za ka yi mutuwar marar kaciya a hannuwan baƙi. Na faɗa, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”
You shall perish by the hands of strangers among the multitude of the uncircumcised: for I have spoken it, says the Lord.
11 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
And the word of the Lord came to me, saying,
12 “Ɗan mutum, ka yi makoki domin sarkin Taya ka kuma ce masa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Ka kasance hatimin cikakke, cike da hikima da cikakke a kyau.
Son of man, take up a lamentation for the prince of Tyre, and say to him, Thus says the Lord God; You are a seal of resemblance, and crown of beauty.
13 Ka kasance a Eden, a lambun Allah; aka yi maka ado da kowane dutse mai daraja, yakutu, tofaz, da zumurrudu, kirisolit, onis da yasfa, saffaya, turkuwoyis da beril. Tsare-tsare da shirye-shiryenka an yi su da zinariya ne; a ranar da aka halicce ka an shirya su.
You were in the delight of the paradise of God; you have bound upon you every precious stone, the sardius, and topaz, and emerald, and carbuncle, and sapphire, and jasper, and silver, and gold, and ligure, and agate, and amethyst, and chrysolite, and beryl, and onyx: and you have filled your treasures and your stores in you with gold.
14 An shafe ka kamar kerub mai tsaro, gama haka na naɗa ka. Kana a tsattsarkan dutsen Allah; ka yi tafiya a tsakiyar duwatsun wuta.
From the day that you were created you [was] with the cherub: I set you on the holy mount of God; you were in the midst of the stones of fire.
15 Ka kasance marar laifi cikin dukan hanyoyinka daga ranar da aka halicce ka sai da aka sami mugunta a cikinka.
You were faultless in your days, from the day that you were created, until iniquity was found in you.
16 Ta wurin yawan kasuwancinka ka cika da rikici, ka kuma yi zunubi. Saboda haka na kore ka da kunya daga dutsen Allah, na kore ka, ya kerub mai tsaro, daga cikin duwatsun wuta.
Of the abundance of your merchandise you have filled your storehouses with iniquity, and have sinned: therefore you have been cast down wounded from the mount of God, and the cherub has brought you out of the midst of the stones of fire.
17 Zuciyarka ta cika da alfarma saboda kyanka, ka kuma lalace hikimarka saboda darajarka. Saboda haka na jefar da kai zuwa ƙasa; na sa ka zama abin kallo a gaban sarakuna.
Your heart has been lifted up because of your beauty; your knowledge has been corrupted with your beauty: because of the multitude of your sins I have cast you to the ground, I have caused you to be put to open shame before kings.
18 Ta wurin yawan zunubanka da kasuwancinka na cuta ka ƙazantar da wuri mai tsarkinka. Saboda haka na sa wuta ta fito daga cikinka, ta cinye ka, na maishe ka toka a bisa ƙasa a kan idon dukan waɗanda suke kallonka.
Because of the multitude of your sins and the iniquities of your merchandise, I have profaned your sacred things; and I will bring fire out of the midst of you, this shall devour you; and I will make you [to be] ashes upon your land before all that see you.
19 Dukan al’umman da suka san ka sun giggice saboda masifar da ta auko maka; ka zo ga mummunar ƙarshe ba za ka ƙara kasancewa ba har abada.’”
And all that know you among the nations shall groan over you: you are gone to destruction, and you shall not exist any more.
20 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
And the word of the Lord came to me, saying,
21 “Ɗan mutum, ka fuskanci Sidon; ka yi annabci a kanta
Son of man, set your face against Sidon, and prophesy against it,
22 ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Ina gāba da ke, ya Sidon, zan sami ɗaukaka a cikinki. Za su san cewa ni ne Ubangiji, sa’ad da na zartar da hukunci a kanta na kuma nuna kaina mai tsarki a cikinta.
and say, Thus says the Lord; Behold, I am against you, O Sidon; and I will be glorified in you; and you shall know that I am the Lord, when I have wrought judgments in you, and I will be sanctified in you.
23 Zan aika da annoba a kanta in kuma sa jini ya zuba a titunanta. Kisassu za su fāɗi a cikinta, da takobi yana gāba da ita a kowane gefe. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji.
Blood and death [shall be] in your streets; and [men] wounded with swords shall fall in you and on every side of you; and they shall know that I am the Lord.
24 “‘Mutanen Isra’ila ba za su ƙara kasance da mugayen maƙwabta waɗanda za su zama sarƙaƙƙiya masu zafi da ƙaya mai tsini ba. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji Mai Iko Duka.
And there shall no more be in the house of Israel a thorn of bitterness and a pricking briar proceeding from them that are round about them, who dishonored them; and they shall know that I am the Lord.
25 “‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa sa’ad da na tattara mutanen Isra’ila daga al’ummai inda suke a warwatse, zan nuna kaina mai tsarki a cikinsu a idon al’ummai. Sa’an nan za su zauna a ƙasarsu, wadda na ba wa bawana Yaƙub.
Thus says the Lord God; I will also gather Israel from the nations, among whom they have been scattered, and I will be sanctified among them, and before the peoples and nations: and they shall dwell upon their land, which I gave to my servant Jacob.
26 Za su zauna a can lafiya su kuma gina gidaje su nome gonakin inabi; za su zauna lafiya sa’ad da zan zartar da hukunci a kan dukan maƙwabtansu da suka wulaƙanta su. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji Allahnsu.’”
Yes, they shall dwell upon it safely, and they shall build houses, and plant vineyards, and dwell securely, when I shall execute judgment on all that have dishonored them, [even] on those [that are] round about them; and they shall know that I am the Lord their God, and the God of their fathers.