< Ezekiyel 28 >

1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
I stalo se slovo Hospodinovo ke mně, řkoucí:
2 “Ɗan mutum, ka faɗa wa mai mulkin Taya cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Cikin alfarmar zuciyarka ka ce, “Ni allah ne; ina zama a kan kursiyin allah a tsakiyar tekuna.” Amma kai mutum ne ba allah ba, ko da yake ka ɗauka kana da hikima kamar allah.
Synu člověčí, rci vývodovi Tyrskému: Takto praví Panovník Hospodin: Proto že se vyvyšuje srdce tvé, a říkáš: Bůh silný jsem, na stolici Boží sedím u prostřed moře, ješto jsi člověk a ne Bůh silný, ačkoli sobě přivlastňuješ srdce podobné srdci Božímu,
3 Ka fi Daniyel hikima ne? Ba asirin da yake ɓoye a gare ka?
Aj hle, moudřejší jsi nad Daniele, žádná věc tajná není před tebou ukrytá;
4 Ta wurin hikimarka da ganewarka ka sami dukiya wa kanka ka kuma tara zinariya da azurfa cikin wuraren ajiyarka.
Moudrosti svou a rozumností svou nashromáždils sobě zboží, a nahrnuls zlata a stříbra do pokladů svých;
5 Ta wurin dabararka mai girma cikin kasuwanci ka ƙara dukiyarka, kuma saboda dukiyarka zuciyarka ta cika da alfarma.
Velikou moudrostí svou v kupectví svém rozmnožil jsi zboží svá, a tak pozdvihlo se srdce tvé zbožím tvým;
6 “‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Domin ka ɗauka kai mai hikima ne, mai hikima kamar allah,
Z té příčiny takto praví Panovník Hospodin: Proto že sobě přivlastňuješ srdce podobné srdci Božímu,
7 zan kawo baƙi a kanka, waɗanda suka fi mugunta cikin sauran al’ummai; za su zāre takubansu a kan kyakkyawar hikimarka su kuma ɓarke darajarka mai walƙiya.
Protož aj, já přivedu na tě cizozemce, nejukrutnější národy, kteříž vytrhnouce meče své na krásu moudrosti tvé, zabijí jasnost tvou.
8 Za su jefar da kai cikin rami, za ka kuwa yi muguwar mutuwa a tsakiyar tekuna.
Do jámy spustí tě, a umřeš smrtí hroznou u prostřed moře.
9 Za ka iya ce yanzu, “Ni allah ne,” a gaban waɗanda suka kashe ka? Za ka zama mutum kurum, ba allah ba, a hannuwan waɗanda suka kashe ka.
Budeš-liž tu ještě říkati před oblíčejem mordéře svého: Bohem jsem, poněvadž jsi člověk a ne Bůh silný, jsa v ruce toho, jenž tě mordovati bude?
10 Za ka yi mutuwar marar kaciya a hannuwan baƙi. Na faɗa, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”
Smrtí neobřezanců umřeš od ruky cizozemců; nebo já mluvil jsem, praví Panovník Hospodin.
11 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
I stalo se slovo Hospodinovo ke mně, řkoucí:
12 “Ɗan mutum, ka yi makoki domin sarkin Taya ka kuma ce masa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Ka kasance hatimin cikakke, cike da hikima da cikakke a kyau.
Synu člověčí, vydej se v naříkání nad králem Tyrským, a rci jemu: Takto praví Panovník Hospodin: Ty, jenž zapečeťuješ summy, plný moudrosti a nejkrásnější,
13 Ka kasance a Eden, a lambun Allah; aka yi maka ado da kowane dutse mai daraja, yakutu, tofaz, da zumurrudu, kirisolit, onis da yasfa, saffaya, turkuwoyis da beril. Tsare-tsare da shirye-shiryenka an yi su da zinariya ne; a ranar da aka halicce ka an shirya su.
V Eden, zahradě Boží, byl jsi, všelijaké drahé kamení přikrývalo tě, sardius, topazius, jaspis, tarsis, onychin, beryl, zafir, karbunkulus a smaragd i zlato; nástrojové bubnů tvých a píšťal tvých v tobě, hned jakžs se narodil, připraveni jsou.
14 An shafe ka kamar kerub mai tsaro, gama haka na naɗa ka. Kana a tsattsarkan dutsen Allah; ka yi tafiya a tsakiyar duwatsun wuta.
Ty jsi cherubem od pomazání. Jakž jsem tě za ochránce představil, na hoře svaté Boží jsi byl, u prostřed kamení ohnivého ustavičně jsi chodil.
15 Ka kasance marar laifi cikin dukan hanyoyinka daga ranar da aka halicce ka sai da aka sami mugunta a cikinka.
Byl jsi dokonalý na cestách svých, hned jakžs se narodil, až se našla nepravost při tobě.
16 Ta wurin yawan kasuwancinka ka cika da rikici, ka kuma yi zunubi. Saboda haka na kore ka da kunya daga dutsen Allah, na kore ka, ya kerub mai tsaro, daga cikin duwatsun wuta.
Pro množství kupectví tvého u prostřed tebe plno jest bezpráví, a velmi jsi prohřešil. Pročež zahubím tě, a vyhladím z hory Boží, ó cherube ochránce, z prostřed kamenů ohnivých.
17 Zuciyarka ta cika da alfarma saboda kyanka, ka kuma lalace hikimarka saboda darajarka. Saboda haka na jefar da kai zuwa ƙasa; na sa ka zama abin kallo a gaban sarakuna.
Pozdvihlo se srdce tvé slávou tvou, k zlému jsi užíval moudrosti své příčinou jasnosti své. Porazím tě na zemi, před oblíčej králů povrhu tě, aby se dívali na tebe.
18 Ta wurin yawan zunubanka da kasuwancinka na cuta ka ƙazantar da wuri mai tsarkinka. Saboda haka na sa wuta ta fito daga cikinka, ta cinye ka, na maishe ka toka a bisa ƙasa a kan idon dukan waɗanda suke kallonka.
Pro množství nepravostí tvých, a pro nespravedlnosti kupectví tvého poškvrnil jsi svatyně své. Protož vyvedu oheň z prostřed tebe, kterýž tě sžíře, a obrátí tě v popel na zemi před očima všech na tě hledících.
19 Dukan al’umman da suka san ka sun giggice saboda masifar da ta auko maka; ka zo ga mummunar ƙarshe ba za ka ƙara kasancewa ba har abada.’”
Všickni, kdož tě znali mezi národy, ztrnou nad tebou; k hrůze veliké budeš, a nebude tě na věky.
20 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
I stalo se slovo Hospodinovo ke mně, řkoucí:
21 “Ɗan mutum, ka fuskanci Sidon; ka yi annabci a kanta
Synu člověčí, obrať tvář svou proti Sidonu, a prorokuj proti němu,
22 ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Ina gāba da ke, ya Sidon, zan sami ɗaukaka a cikinki. Za su san cewa ni ne Ubangiji, sa’ad da na zartar da hukunci a kanta na kuma nuna kaina mai tsarki a cikinta.
A rci: Takto praví Panovník Hospodin: Aj, já proti tobě jsem, ó Sidone, a budu oslaven u prostřed tebe. I zvědí, že já jsem Hospodin, když vykonám při něm soudy, a posvěcen budu v něm.
23 Zan aika da annoba a kanta in kuma sa jini ya zuba a titunanta. Kisassu za su fāɗi a cikinta, da takobi yana gāba da ita a kowane gefe. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji.
Pošli zajisté na něj mor, a krev na ulice jeho, a padati budou zranění u prostřed něho od meče na všecky strany, i zvědí, že já jsem Hospodin.
24 “‘Mutanen Isra’ila ba za su ƙara kasance da mugayen maƙwabta waɗanda za su zama sarƙaƙƙiya masu zafi da ƙaya mai tsini ba. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji Mai Iko Duka.
A tak nebude více míti dům Izraelský trnu urážejícího a bodláku bodoucího ze všech okolních pohrdajících jimi, a zvědí, že já jsem Panovník Hospodin.
25 “‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa sa’ad da na tattara mutanen Isra’ila daga al’ummai inda suke a warwatse, zan nuna kaina mai tsarki a cikinsu a idon al’ummai. Sa’an nan za su zauna a ƙasarsu, wadda na ba wa bawana Yaƙub.
Takto praví Panovník Hospodin: Když shromáždím dům Izraelský z národů, mezi něž rozptýleni jsou, a posvěcen budu v nich před očima pohanů, a bydliti budou v zemi své, kterouž jsem byl dal služebníku svému Jákobovi:
26 Za su zauna a can lafiya su kuma gina gidaje su nome gonakin inabi; za su zauna lafiya sa’ad da zan zartar da hukunci a kan dukan maƙwabtansu da suka wulaƙanta su. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji Allahnsu.’”
Tehdy bydliti budou v ní bezpečně, a nastavějí domů, a štípí vinice. Bydliti, pravím, budou bezpečně, když vykonám soudy, při všech zhoubcích jejich vůkol nich, i zvědí, že já jsem Hospodin Bůh jejich.

< Ezekiyel 28 >