< Ezekiyel 27 >

1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
HIKI hou mai ka olelo a Iehova ia'u, i mai la,
2 “Ɗan mutum, ka yi makoki domin Taya.
Ano, o ke keiki a ke kanaka e hoomaka oe i ke kanikau no Turo.
3 Ka ce wa Taya, wadda take zaune a hanyar shiga zuwa teku, kasuwar masu yawa mutane a bakin teku, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Kin ce, ya Taya, “Ni kyakkyawa ce cikakkiya.”
A e olelo aku ia Turo, E ka mea e noho ana ma ke komo ana o ke kai, ka mea kalepa a kanaka o na mokupuni he nui, ke i mai nei Iehova ka Haku, E Turo, ua olelo oe, He nani loa au.
4 Manyan tekuna ne wurin zamanki; maginanki sun sa kyanki ya zama cikakke.
Aia kou mau palena mawaena konu o ke kai, o kou mau mea kukulu, ua hoohemolele lakou i kou nani.
5 Sun yi dukan katakanki daga itatuwan fir daga Senir; sun kwaso itatuwan al’ul daga Lebanon don su yi miki jigon jirgin ruwa.
Ua hana lakou i kou mau papa moku no na laau kaa o Senira; a mai Lebanona mai i lawe mai ai lakou i na kedera e hana i mau kia nou.
6 Da oak daga Bashan suka yi sandunan tuƙan jirgin ruwa da itatuwan kasharina daga bakin tekun Saifurus suka yi daɓe jirgin ruwanki, suka kuma manne masa hauren giwa.
No na oka o Basana i hana'i lakou i kou mau hoe; ua hana no hoi ka poe mamo a Asura i kou mau papa noho he niho elepani i laweia mai mai na moku mai o Kitima.
7 Lilin mai kyau mai ado daga Masar ne filafilan jirgin ruwanki suka kuma zama tutarki; an yi tutarki da shuɗi da shunayya daga bakin tekun Elisha.
O ke olona makalii i hoonionioia mai Aigupita mai, oia kau mea i kau ai i pea nou; o ka poni uliuli a me ka makue mai na moku o Elisa, oia ka mea i uhi mai ia oe.
8 Mutanen Sidon da Arfad su ne matuƙan jirgin ruwanki; gwanayenki, ya Taya, suna ciki a matsayi matuƙan jiragen ruwa.
O ko Zidona a me ko Arevada, oia kou poe holomoku: o kou poe kanaka akamai, na mea iloko ou, oia kou mau pailota.
9 Masu hikima na Gebal suna ciki a matsayin masu tattoshe mahaɗan katakon jirginki. Dukan jiragen ruwa da matuƙansu sukan zo wurinki don kasuwanci.
O na mea kahiko o Gehala, a me kona poe akamai, oia kou poe kapilimoku iwaena ou. Pau na mokuholo o ke kai a me ko lakou poe holomoku, ka iloko ou i ka lawelawe i kou waiwai kalepa.
10 “‘Mutanen Farisa, Lidiya da Fut su ne suka zama sojoji a cikin mayaƙanki. Sun rataye garkuwoyinsu da hulunan kwano a katangarki, suna kawo miki daraja.
O ko Peresia, a me ko Luda, a me ko Puta, kou poe kanaka kaua iloko o kou poe koa; ua kau lakou i ka palekaua a me ka mahiole iloko ou; ua hoike lakou i kou nani.
11 Mutanen Arfad da Helek sun yi tsaron katangar a kowace gefe; mutanen Gammad su ne a hasumiyoyinki. Sun rataye garkuwoyinsu kewaye da katangarki; sun sa kyanki ya zama cikakke.
O kanaka o Arevada, me kou poe koa, ka iluna o kou mau pa a puni, a me ko Gamada ka iloko o kou raau halekiai; ua Kau ae lakou i ko lakou mau palekaua ma kou mau paia a puni; a ua hoolilo lakou i kou nani i hemolele.
12 “‘Tarshish ta yi ciniki da ke saboda yawan wadatar kayayyakinki; sun sayi kayan cinikinki da azurfa, ƙarfe, kuza da dalma.
A lilo o Taresisa i mea kalepa no ka nui loa o kela waiwai keia waiwai; me ke kala, ka hao, ke tina, ke kepaupoka, i kuai ai lakou ma kou mau wahi kuai.
13 “‘Girka, Tubal da Meshek sun yi kasuwanci da ke; sun sayi kayanki suka biya da bayi da kuma abubuwan da aka yi da tagulla.
Iavana, Tubala, a me Mesaka, o lakou na hoa kalepa ou; ua kalepa lakou i kanaka, a me na ipu keleawe, ma kou mau wahi i kalepa ai.
14 “‘Mutanen Bet Togarma sun sayi kayan cinikinki da dawakai, dawakan yaƙi da alfadarai.
O ko ka ohana a Togarema ua kalepa mai, ma kou mau wahi i kalepa ai, me na lio, na hololio, a me na hoki.
15 “‘Mutanen Dedan sun yi kasuwanci da ke, bakin teku masu yawa abokan cinikinki ne; sun biya ki da hauren giwa da katakon kanya.
A o kanaka o Dedana, o lakou na hoa kalepa ou; he nui na mokupuni ka waiwai kalepa iloko o kou lima; lawe mai lakou i na pepeiaohao elepani a me ka eboni i makana nou.
16 “‘Mutanen Aram sun yi ciniki da ke saboda yawan kayanki; suka sayi kayan cinikinki da zumurrudu, da shunayya, da kayan ado, da lilin mai taushi, da murjani, da yakutu.
O Suria hoi kou hoa kalepa no ka nui o kau mau waiwai i hana'i; ua lawelawe lakou ma kou mau wahi i kalepa ai i na emerala, i ka makue, a me ka lole hoonionioia, a me ka lole olona, a me ke akoakoa, a me ka agate.
17 “‘Yahuda da Isra’ila sun yi kasuwanci da ke; sun sayi kayanki da alkama da Minnit da alawa, da zuma, da mai, da ganyaye masu ƙanshi.
O Iuda a me ka aina o ka Iseraela, o laua na hoa kalepa ou; ua kalepa lakou ma kou mau wahi kuai i ka palaoa o Minita, a o Panaga, a me ka meli, a me ka aila, a me ka balesama.
18 “‘Mutanen Damaskus sun ga abin da za ki iya bayarwa sai suka yi ciniki da ke, ta sayi kayanki da ruwan inabi daga Helbon, da ulu daga Zahar.
O Damaseko kou hoa kalepa ma na mea nui au i hana'i, no ka nui loa o kela waiwai keia waiwai, me ka waina o Helebona a me ka huluhulu keokeo.
19 Wedan da Yaban kusa da Uzal, suka sayi kayanki; wato gyararren ƙarfe da kayan yaji.
O Dana a me Iavana mai Uzala mai kekahi kalepa ma kou mau wahi i kalepa ai; o ka hao huali, a me ke kasia, a me ke kalamo ka iloko o kou mau wahi i kalepa ai.
20 “‘Mutanen Dedan sun sayi kayanki da sirdin zama a kan dawakai.
O Dedana kou mea kalepa ma na lole makamae no na kaa.
21 “‘Mutanen Arabiya da dukan sarakunan Kedar abokan cinikinki ne; sun yi ciniki da ke suka sayi kayanki da’yan raguna, da raguna, da awaki.
O Arabia a me na'lii a pau o Kedara, o ka poe kalepa lakou o kou lima, ma na keikihipa, a me na hipa kane a me na kao; ma ia mau mea he poe kalepa lakou nou.
22 “‘’Yan kasuwan Sheba da Ra’ama sun yi ciniki da ke; suka sayi kayanki da kayan yaji mafi kyau iri-iri, da duwatsu masu daraja iri-iri, da zinariya.
O na mea kalepa o Seba a me Raba, oia ka poe Kalepa ou; na kalepa lakou i ka maikai loa o na mea ala a pau, a me na pohaku maemae, a me ke gula.
23 “‘Haran, Kanne da Eden da kuma’yan kasuwan Sheba, Assuriya da Kilmad sun yi ciniki da ke.
O Harana, o Kane, a me Edena, na mea kalepa o Seba, Asura a me Kilemada, he mau mea kalepa nou.
24 A kasuwarki sun yi ciniki da ke suka sayar miki tufafi masu tsada, da na shuɗi, da masu ado, da dardumai masu ƙyalƙyali da kirtani, da igiyoyi waɗanda aka tuƙa da kyau.
O lakou kou mau hoa kalepa ma na mea maikai, na kapa uliuli, a me ka mea hoonionioia, a me na kapa komo anoninoni i paa i na kaula, a me ka laau kedera iwaena o kau waiwai kalepa.
25 “‘Jiragen ruwan Tarshish sun zama masu jigilar kayanki. Kin cika da kaya masu nauyi a tsakiyar teku.
O na moku holo o Taresisa kou mau huakai kalepa, a ua hoolakoia ae, a ua hooliloia i nani loa maloko io o ke kai.
26 Matuƙan jiragenki sun kai ki can cikin manyan tekuna. Amma iskar gabas za tă farfasa ki kucu-kucu a tsakiyar teku.
Ua lawe kou mau mea hoe ia oe iloko o na wai nui; ua wawahi ka makani hikina ia oe maloko o ke kai.
27 Dukiyarki, cinikinki da kayan kasuwarki, ma’aikatanki na jirgi, matuƙan jiragenki da masu tattoshe mahaɗan katakan jiragenki,’yan kasuwarki da dukan sojojinki, da kuma kowa da yake cikin jirgi zai nutsa a tsakiyar teku a ranar da jirginki zai nutse.
O kou waiwai nui, a me kou mau wahi i kalepa ai, o kou waiwai kalepa, a kou poe holo moku, a me kou mau pailota, o kou mau mea kapili moku, a me kou mau mea malama waiwai, a me kou poe kanaka kaua a pau iwaena ou, a o kou lehulehu hoi a pau iloko ou, e haule lakou iloko o ke kai, i ka la e pau ai oe.
28 Ƙasashen bakin teku za su girgiza sa’ad da matuƙan jirginki suka yi kuka.
E naueue na wahi e hoopuni ana no ka leo o ka uwe ana o kou poe hooholo moku.
29 Dukan waɗanda suke riƙe da matuƙi za su ƙyale jiragensu; ma’aikatan jirage da dukan matuƙan jirage za su tsaya a bakin teku.
A o na mea hoe a pau, na holomoku, a me ka poe hooholomoku a pau o ke kai, e iho ae lakou mai luna ae o ko lakou mau moku, a e ku lakou ma ka aina.
30 Za su tā da muryarsu su yi kuka mai zafi a kanki; za su yayyafa ƙura a kawunansu, su yi ta birgima a cikin toka.
A e hooloheia lakou i ko lakou leo nou, a e auwe ikaika lakou, a e hoolei lakou i ka lepo maluna iho o ko lakou poo iho; a e moe lakou iloko o ka lehu.
31 Za su aske kawunansu saboda ke za su kuma sa tufafin makoki. Za su yi kuka dominki su yi ɓacin rai da kuma kuka mai zafi.
A e hooohule loa lakou ia lakou iho nou, a e kaei ia lakou iho me ke kapa ino; a e uwe lakou nou me ke kaumaha o ka naau a me ka auwe nui.
32 Yayinda suke kuka a kanki kuwa, za su yi makoki dominki suna cewa, “Wa ya taɓa yin shiru kamar Taya, kewaye da teku?”
A i ko lakou auwe ana, e hapai lakou i ke kanikau nou, a e kanikau lakou maluna ou, e i ana, Auhea ka like me Turo, i like me ka mea i hookaiia maloko o ke kai?
33 Sa’ad da kayan cinikinki suka tafi ƙasashen hayi, kin gamsar da al’ummai masu yawa; da dukiyarki masu yawa da kuma kayan cinikinki kin azurtar da sarakunan duniya.
I ka puka ana'ku o kou waiwai mai loko aku o na kai, ua hoopaapu oe i na kanaka he nui, ua hoolako oe i na'lii o ka honua me ka nui o kou waiwai, a me kou waiwai kalepa.
34 Yanzu teku ta farfashe ki cikin zurfafan ruwaye; kayan cinikinki da dukan kamfaninki sun nutse tare da ke.
I ka wa e wawahiia'i oe e na kai, ma kahi hohonu o ka wai, e haule kou waiwai kalepa, a me kou lehulehu a pau iwaenakonu ou.
35 Dukan mazaunan bakin teku sun giggice saboda masifarki; sarakunansu sun tsorata ƙwarai fuskokinsu kuwa sun yamutse don tsoro.
E makau aku ia oe ka poe a pau e noho ana ma na mokupuni, a e weliweli loa ko lakou mau alii, a e pioloke lakou ma ko lakou mau maka.
36 ’Yan kasuwa a cikin al’ummai suna yin miki tsaki; kin zo ga mummunar ƙarshe ba za ki ƙara kasancewa ba har abada.’”
E kahaha aku ia oe ka poe kalepa iwaena o na kanaka: e lilo oe i mea weliweli ai, aole loa aku hoi oe,

< Ezekiyel 27 >